Sashe 216
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daidai sanda suka nufi gidan su'ad na tsaye tsakar dakinta tana amsawa wayar da suke da mahaifiyarta
"Nifa gaskiya su'ad na soma sarewa,kinga tsantsar farinciki da doki da professor yake ciki sanda ya kira mahaifinki kamar ranar aka soma haifa masa jikoki,anya kuwa su'ad ba muyi kuskure ba?,ina da yaqinin Allah kadai yasan dukiyar da zasu samu su kuma mallaka tun suna qananunsu,wanda dukkan abinda suka samu zai koma fa hannun mahaifiyarsu ne" qatuwar ajiyar zuciya ta saki
"Bama wannan ba momy,wallahi na tabbatar na shiha uku,duk wani soyayya da tattali da adalci da almustapha ke qoqarin gwadamin ina da yaqinin sai ta ragu,tun cikin bai fito duniya ba kinga abinda yake?,ina ga ya fito sannan kuma twince mommy?,shi yasa nake tunani anya ba zamu sake plan ba?,na nemi dalilin haihuwa nima ko don na sake janyo hankalinshi zuwa gareni baki daya?"
"Dqlla can rufewa mutane baki,ke ta soyayyarsa ma kadai kike,soyayyar vanza,ana miki maganar kudi abokan tafiya qare magana,so nake fa ki zama cikin jerin attajiran da duniya ke lissafinsu kaman yadda a yanzu mijin naki yake,ke kadai ce fa 'yata ke daya na mallaka,saboda haka ina so naga kinyi shaharar da ko d'a namijin da yayi shekara arba'in yana gwagwarmaya baiyita ba"
"To yanzu ya za'a yi momy?"
"Cikin satin nan kisan yadda zakiyi kizo nan mu warwareta"
"An gama" ta fada tana katse wayar saboda motsi da taji kaman ana shigowa,a hankali ta tako ta fito zuwa falon,almustapha ne riqe da baby daya,wata mace mawociyarsu 'yar asalin qasar saudiyya dauke da dayan,fuskarta a washe tana tana yaba kyawu da girman yaran cikin harshen larabci,duk da bata fahimtar me take fada amma daga yanayin matar tasan tana yabawa ne da yadda yaran suke,idanu ta zuba musu tana karantar fuskar almustapha wanda bata san da dawowarshi ba saibyanzu,tunda sukayi magana ya tambayeta sumayya tace bata sani ba bai kuma kira ba hakanan bata bi ta kanshi ha itama,iya tsahon zamanta da shi bata taba ganinshi cikin wannan hali na matsanancin farinciki ba, saidai ba wanda ya kula da ita a cikinsu saboda tana daga bayan labule ne har suka shige.
Yana fitowa daga dakin ya lura da ita,fuskarshi sake yake dubanta,bacin rai da take dannewa ya taso yafi qarfinta,sai kawai kuka ya qwace mata,sai ta juya da gudu gudu ta koma ciki,tausayinta ne ya sauko masa lokaci guda,yana tunanin rashin samun tata haihuwar shi ya motsa mata,wanda hakan zai iya faruwa ga kowacce mace,kowanne lokaci kuma yanayin kan iya motsuwa cikin zuciyarki har ki kasa controlling din kanki,sai ya rufa mata baya,samunta yayi kuwa zaune saman kujera tana buge buge da hannunta,dama ace dama ace ce fal cikin zuciyarta,zata so a ce itace ta samu wannan yaran ba sumayya ba,wai shin me ya hanata tsayawa ko guda daya ta samu ne?,ba shakka tana ji a jikinta lokaci yayi da zata tashi ta dawowa da kanta dama ta samun haihuwa a gareta,a tausashe ya zauna gefanta yana riqeta,baison idan wani abu ya sameta ta dinga irin wannan acting din dake nuna zallar rashin yarda da qaddara,cikin taushi ya soma ce mata
"Am sorry dear....ba kuka zakiyi ba,addu'a zakiyi Allah ya kawo mana,komai a duniya yana da lokaci sannan komai yai farko yana da qarshe banda ikon Allah,matuqar kina da rabo ta babu makawa sai kin haifa kema"
"Ko bani da rabo wallahi sai na yishi,sai na haihu nima" tsauri maganar tayi masa,haqiqa ba qaramin illa da tasiri dabi'un yahudawa marasa tauhidi suka yiwa su'ad din ha,saidai yana da burin sosai wajen ganin ta daidaitu,duk da hakan ma alhamdulillah,ya rabata da shigar banza ya sata tsaida sallah,koda kuwa zata yita ne bayan wucewar lokacinta
"Subhanallah,kiyi istigfari,babu bawan da yafi qarfin QADDARA,saidai addu'a na maida MUMMUNAR QADDARA ta koma zuwa KYAKKYAWA,ki roqi Allah sai ya kawo komai a sauqaqe,ba wayonki ko dabararki ba,ita kanta ada can an taba kiranta juya,an fidda mata rai zata haihu,amma a yanzu gashi ke ya faru?" Cikin hikima yake gaya kata kalaman kwantar da hankali,saidai jinsu take kaman busat sarewq,abu daya ne ya dan kwantar mata da hankali,kasancewa da yayi tare da ita duk da ba ranarta bace,da kuma yadda yake lallashinta,saidai ba shakka cikin satin nan zata san yadda zata wuce america don bazata juri rasa cika burin data qudurtawa ranta ba.
Maqota biyu da suke da su wadanda ba yarenta ba saidai 'yan uwantaka ta muslunci da tsananin kirki da suke da shi,wanda batasan suna da shi ba sai yanzun da haihuwar 'yan biyu dake da farinjini suka sa tasan hakan,suna kula da ita sosai,akai akai suke leqota da kalar abinci da kulawa da sukewa maijego,akwai mai tayata zama guda daya daya samu wanda ta kasance mutuwar qasar ghana ce,zaman sana'a yasa take zaune a qasar,sai ta kasancewa sumayya tamkar yar uwa,sosai matar ke kula da ita,tana da qoqari da zafin nama qwarai,babu abinda sumayyan ta nema ta rasa,hatta da shi mai gayya mai aikin idan ya fita sha daya,biyat na yammaci ya dawo gida,koda yashe burinsa ya ganshi tare da su,a haka ma idanun su'ad yasa ya dan rage wasu abubuwa tare da danne daukinsa,don har ga Allah tausayinta yake ji,yasan cewa rashin haihuwa babbar damuwa ce dakan iya zamewa wasu matan ciwo cikin zukatansu,abinda bai sani ba shine ta soma girbar abinda ta shuka ne ba tare da shi karan kanshi ya sani ba,wani tsananin son hauhuwa ne ya mata mugun kamu cikin kwanakin da basu haza hudu ba,sosai walwala da kuzarinta ya ragu,kishin yaran da uwarsu baki daya ya gallabeta,ko sau daya tak bata taba kusantar dakin sumayya ba bare tace zata ga yaran,wani abu ke tokare mata wuya duk sanda taji sautin kukansu,ji take kaman ta kaudasu ko ta samu hutu.
Daga daya bangaren kuma tuni ummi ta gama duk wani shirinta na zuwan yaran da mamarsu,kwana biyu taji shiru hakan ne yasa ta tuntubeshi,sai yace 'yar matsala ce aka samu wajen siyan ticket,tuni ta baroshi,wanne matsala ce za'a samu wajen siyan ticket kawai?,shi kansa yasan qaryar bata hadu ba saboda ba sabonshi bace,ko kadan ne kawai baya son su tafi su barshi,baya jin zaman garin zai yiwu gareshi idan suka tafi din,shi a son ranshi duk maison zuwa cikin gidan nasu zai siya masa ticket,wanda bai da visa zai masa suzo suga yaran,sam bazaiyiwu ba ummi ta gaya masa,su a wajensu tamkar haihuwar fari ne,saboda haka dole ya kawo 'yar mutane a kula da ita sosai,sannan itama tana da yan uwa tana son zama cikinsu ai,shikam baiga wacce kulawa akeson bata ba bayan wanda take samu nan daga wajensa,yana kallonta take saka towel cikin tafasasheshen ruwa ta gasa kanta sosai,ta fito taci abinciccika masu gina jiki,ga magungunan da yasa zasuyi mata matuqar amfani a jiki da take sha,hakan ya sanya hatta da ruwan nono ta samu wadatacce,kana kallonsu zaka san kulawa kam sun sameta,daga ita har yaran kai kace sunfi kwanaki hudu da haihuwar,warshe dai haquri ya baiwa ummi yace suna tahowa.
Sai ana ya gobe zasu cika kwanaki bakwai sannan ya siya musu ticket har da shi da su'ad zasu tafi,dakin su'ad ya fara zuwa,ya taddata zaune tana latse latsen waya,sam sumayya bata gaya mishi bata taba zuwa taga yaran ba,shima kuma bai taba kawo ba zata shiga din ba,gefanta ya samu ya zauna yana fuskantar fuskarshi a sake sosai,kai ta daga ta dubeshi,as usal bata iya sannu da zuwa ba ko gaisuwa
"Baki gajiya da danna waya?" Ya tambaya yana daukar remote ya rage saitin kidan dake tashi a tv
"Idan ban danna ba me kake so nayi?" Ta tambayeshi cikin yanayin bacin rai,idanu ya zuba mata yana karantar yanayinta,sai kuma ya hadiye ya dauke kanshi daga fuskarta yaba bata amsa
"Karatun qur'ani,istigfari da sauransu"
"K'nnnnn" ta ce a taqaice,tun daga ranar zuciyarta da shaidan suke gaya mata ta gama burge almustapha fa,yanzu ba sonta yake ba ba kuma qaunarta yake ba,yaranshi da uwarsu su kadai yake so da qauna,bayan babu wani abu da yayi mata wanda ke nuna haman,illa ma lallashinta da yake saboda yana tunanin rashin samun nata yaran na kanta ke damunta
"Gobe zamu shiga nigeria,su ummi sun matsa sai mun dawo a yi suna a can kowa yaga yara"qafafunta ta miqe ranta na baci
"wannan ku ta shafa sai kun dawo" idanunsa ya qanqance yana dubanta,wati mai hali bai fasa halinsa,duk yadda yake tattali da rarrashinta wato shi din banza ne baisan ciwon kanshi ba?
"Kamar yaya fa?" Ta tambayeta yana son qarin bayani
"Ai suma su ummin tsabar gulma ce,babu gidan uban da zani,wato nake inje aji dadin nuna ni gani ban haihu ba wata tazo bayan bayana ta haihu ko?,to bazanje ba,dama an dade ana ruwa qasa na tsotsewa,muna fukin auren ma duk ha sune sila ba sabida kai an tsaneka ba'a sonka" cikin tsananin bacin rai ya daka mata tsawa,nunata yake da yatsa cikin bacin rai
"Hey idiot.....Kar ki soma kuskuren fadin maganar banza kan mahaifana,ki kintsa bakinki kada furucinka ya jawo miki nadama......iyayena sun fiye komai da komai da na mallaka nake da shi,su din wasu abubuwane masu daraja da babu kamarsu,kudi ko qarfin iko basu isa su baka su ba.....ban gaya miki zamu nijeria ba wai don ina neman shawararki ba,umarni nake baki kaman yadda wadanda suka isa da ni suka bani umarni nabi,kema dole kibi umarni na don na isa da ke" ya miqe yana niyyar ficewa ranshi a bace
"To wallahi ba inda zani daga nan nima gidanmu zan wuce ai ina da gidan uba...." Waiwayowa yayi yana mata wani kallo daya sanyata rusuna ba tare data shirya ba
"Really?,....ok,indai haka ne idan kinje kada ki sake ki dawomin gida kinji ko?,ruwanki kije nigeria ruwanki kije ameria amma ki zauna acan,kada qafarki ta dawo gidan muhammad almustapha" yana kaiwa nan ya wuce yana mai buga qofar cikin fushi,kanta ta dafe,tabbas bata da wata mafita,zai iya aikata dukkan abinda yace din,saidai ta gama rayawa ranta abinda zatayi,zuwa gida babu fashi.
"Nifa gaskiya su'ad na soma sarewa,kinga tsantsar farinciki da doki da professor yake ciki sanda ya kira mahaifinki kamar ranar aka soma haifa masa jikoki,anya kuwa su'ad ba muyi kuskure ba?,ina da yaqinin Allah kadai yasan dukiyar da zasu samu su kuma mallaka tun suna qananunsu,wanda dukkan abinda suka samu zai koma fa hannun mahaifiyarsu ne" qatuwar ajiyar zuciya ta saki
"Bama wannan ba momy,wallahi na tabbatar na shiha uku,duk wani soyayya da tattali da adalci da almustapha ke qoqarin gwadamin ina da yaqinin sai ta ragu,tun cikin bai fito duniya ba kinga abinda yake?,ina ga ya fito sannan kuma twince mommy?,shi yasa nake tunani anya ba zamu sake plan ba?,na nemi dalilin haihuwa nima ko don na sake janyo hankalinshi zuwa gareni baki daya?"
"Dqlla can rufewa mutane baki,ke ta soyayyarsa ma kadai kike,soyayyar vanza,ana miki maganar kudi abokan tafiya qare magana,so nake fa ki zama cikin jerin attajiran da duniya ke lissafinsu kaman yadda a yanzu mijin naki yake,ke kadai ce fa 'yata ke daya na mallaka,saboda haka ina so naga kinyi shaharar da ko d'a namijin da yayi shekara arba'in yana gwagwarmaya baiyita ba"
"To yanzu ya za'a yi momy?"
"Cikin satin nan kisan yadda zakiyi kizo nan mu warwareta"
"An gama" ta fada tana katse wayar saboda motsi da taji kaman ana shigowa,a hankali ta tako ta fito zuwa falon,almustapha ne riqe da baby daya,wata mace mawociyarsu 'yar asalin qasar saudiyya dauke da dayan,fuskarta a washe tana tana yaba kyawu da girman yaran cikin harshen larabci,duk da bata fahimtar me take fada amma daga yanayin matar tasan tana yabawa ne da yadda yaran suke,idanu ta zuba musu tana karantar fuskar almustapha wanda bata san da dawowarshi ba saibyanzu,tunda sukayi magana ya tambayeta sumayya tace bata sani ba bai kuma kira ba hakanan bata bi ta kanshi ha itama,iya tsahon zamanta da shi bata taba ganinshi cikin wannan hali na matsanancin farinciki ba, saidai ba wanda ya kula da ita a cikinsu saboda tana daga bayan labule ne har suka shige.
Yana fitowa daga dakin ya lura da ita,fuskarshi sake yake dubanta,bacin rai da take dannewa ya taso yafi qarfinta,sai kawai kuka ya qwace mata,sai ta juya da gudu gudu ta koma ciki,tausayinta ne ya sauko masa lokaci guda,yana tunanin rashin samun tata haihuwar shi ya motsa mata,wanda hakan zai iya faruwa ga kowacce mace,kowanne lokaci kuma yanayin kan iya motsuwa cikin zuciyarki har ki kasa controlling din kanki,sai ya rufa mata baya,samunta yayi kuwa zaune saman kujera tana buge buge da hannunta,dama ace dama ace ce fal cikin zuciyarta,zata so a ce itace ta samu wannan yaran ba sumayya ba,wai shin me ya hanata tsayawa ko guda daya ta samu ne?,ba shakka tana ji a jikinta lokaci yayi da zata tashi ta dawowa da kanta dama ta samun haihuwa a gareta,a tausashe ya zauna gefanta yana riqeta,baison idan wani abu ya sameta ta dinga irin wannan acting din dake nuna zallar rashin yarda da qaddara,cikin taushi ya soma ce mata
"Am sorry dear....ba kuka zakiyi ba,addu'a zakiyi Allah ya kawo mana,komai a duniya yana da lokaci sannan komai yai farko yana da qarshe banda ikon Allah,matuqar kina da rabo ta babu makawa sai kin haifa kema"
"Ko bani da rabo wallahi sai na yishi,sai na haihu nima" tsauri maganar tayi masa,haqiqa ba qaramin illa da tasiri dabi'un yahudawa marasa tauhidi suka yiwa su'ad din ha,saidai yana da burin sosai wajen ganin ta daidaitu,duk da hakan ma alhamdulillah,ya rabata da shigar banza ya sata tsaida sallah,koda kuwa zata yita ne bayan wucewar lokacinta
"Subhanallah,kiyi istigfari,babu bawan da yafi qarfin QADDARA,saidai addu'a na maida MUMMUNAR QADDARA ta koma zuwa KYAKKYAWA,ki roqi Allah sai ya kawo komai a sauqaqe,ba wayonki ko dabararki ba,ita kanta ada can an taba kiranta juya,an fidda mata rai zata haihu,amma a yanzu gashi ke ya faru?" Cikin hikima yake gaya kata kalaman kwantar da hankali,saidai jinsu take kaman busat sarewq,abu daya ne ya dan kwantar mata da hankali,kasancewa da yayi tare da ita duk da ba ranarta bace,da kuma yadda yake lallashinta,saidai ba shakka cikin satin nan zata san yadda zata wuce america don bazata juri rasa cika burin data qudurtawa ranta ba.
Maqota biyu da suke da su wadanda ba yarenta ba saidai 'yan uwantaka ta muslunci da tsananin kirki da suke da shi,wanda batasan suna da shi ba sai yanzun da haihuwar 'yan biyu dake da farinjini suka sa tasan hakan,suna kula da ita sosai,akai akai suke leqota da kalar abinci da kulawa da sukewa maijego,akwai mai tayata zama guda daya daya samu wanda ta kasance mutuwar qasar ghana ce,zaman sana'a yasa take zaune a qasar,sai ta kasancewa sumayya tamkar yar uwa,sosai matar ke kula da ita,tana da qoqari da zafin nama qwarai,babu abinda sumayyan ta nema ta rasa,hatta da shi mai gayya mai aikin idan ya fita sha daya,biyat na yammaci ya dawo gida,koda yashe burinsa ya ganshi tare da su,a haka ma idanun su'ad yasa ya dan rage wasu abubuwa tare da danne daukinsa,don har ga Allah tausayinta yake ji,yasan cewa rashin haihuwa babbar damuwa ce dakan iya zamewa wasu matan ciwo cikin zukatansu,abinda bai sani ba shine ta soma girbar abinda ta shuka ne ba tare da shi karan kanshi ya sani ba,wani tsananin son hauhuwa ne ya mata mugun kamu cikin kwanakin da basu haza hudu ba,sosai walwala da kuzarinta ya ragu,kishin yaran da uwarsu baki daya ya gallabeta,ko sau daya tak bata taba kusantar dakin sumayya ba bare tace zata ga yaran,wani abu ke tokare mata wuya duk sanda taji sautin kukansu,ji take kaman ta kaudasu ko ta samu hutu.
Daga daya bangaren kuma tuni ummi ta gama duk wani shirinta na zuwan yaran da mamarsu,kwana biyu taji shiru hakan ne yasa ta tuntubeshi,sai yace 'yar matsala ce aka samu wajen siyan ticket,tuni ta baroshi,wanne matsala ce za'a samu wajen siyan ticket kawai?,shi kansa yasan qaryar bata hadu ba saboda ba sabonshi bace,ko kadan ne kawai baya son su tafi su barshi,baya jin zaman garin zai yiwu gareshi idan suka tafi din,shi a son ranshi duk maison zuwa cikin gidan nasu zai siya masa ticket,wanda bai da visa zai masa suzo suga yaran,sam bazaiyiwu ba ummi ta gaya masa,su a wajensu tamkar haihuwar fari ne,saboda haka dole ya kawo 'yar mutane a kula da ita sosai,sannan itama tana da yan uwa tana son zama cikinsu ai,shikam baiga wacce kulawa akeson bata ba bayan wanda take samu nan daga wajensa,yana kallonta take saka towel cikin tafasasheshen ruwa ta gasa kanta sosai,ta fito taci abinciccika masu gina jiki,ga magungunan da yasa zasuyi mata matuqar amfani a jiki da take sha,hakan ya sanya hatta da ruwan nono ta samu wadatacce,kana kallonsu zaka san kulawa kam sun sameta,daga ita har yaran kai kace sunfi kwanaki hudu da haihuwar,warshe dai haquri ya baiwa ummi yace suna tahowa.
Sai ana ya gobe zasu cika kwanaki bakwai sannan ya siya musu ticket har da shi da su'ad zasu tafi,dakin su'ad ya fara zuwa,ya taddata zaune tana latse latsen waya,sam sumayya bata gaya mishi bata taba zuwa taga yaran ba,shima kuma bai taba kawo ba zata shiga din ba,gefanta ya samu ya zauna yana fuskantar fuskarshi a sake sosai,kai ta daga ta dubeshi,as usal bata iya sannu da zuwa ba ko gaisuwa
"Baki gajiya da danna waya?" Ya tambaya yana daukar remote ya rage saitin kidan dake tashi a tv
"Idan ban danna ba me kake so nayi?" Ta tambayeshi cikin yanayin bacin rai,idanu ya zuba mata yana karantar yanayinta,sai kuma ya hadiye ya dauke kanshi daga fuskarta yaba bata amsa
"Karatun qur'ani,istigfari da sauransu"
"K'nnnnn" ta ce a taqaice,tun daga ranar zuciyarta da shaidan suke gaya mata ta gama burge almustapha fa,yanzu ba sonta yake ba ba kuma qaunarta yake ba,yaranshi da uwarsu su kadai yake so da qauna,bayan babu wani abu da yayi mata wanda ke nuna haman,illa ma lallashinta da yake saboda yana tunanin rashin samun nata yaran na kanta ke damunta
"Gobe zamu shiga nigeria,su ummi sun matsa sai mun dawo a yi suna a can kowa yaga yara"qafafunta ta miqe ranta na baci
"wannan ku ta shafa sai kun dawo" idanunsa ya qanqance yana dubanta,wati mai hali bai fasa halinsa,duk yadda yake tattali da rarrashinta wato shi din banza ne baisan ciwon kanshi ba?
"Kamar yaya fa?" Ta tambayeta yana son qarin bayani
"Ai suma su ummin tsabar gulma ce,babu gidan uban da zani,wato nake inje aji dadin nuna ni gani ban haihu ba wata tazo bayan bayana ta haihu ko?,to bazanje ba,dama an dade ana ruwa qasa na tsotsewa,muna fukin auren ma duk ha sune sila ba sabida kai an tsaneka ba'a sonka" cikin tsananin bacin rai ya daka mata tsawa,nunata yake da yatsa cikin bacin rai
"Hey idiot.....Kar ki soma kuskuren fadin maganar banza kan mahaifana,ki kintsa bakinki kada furucinka ya jawo miki nadama......iyayena sun fiye komai da komai da na mallaka nake da shi,su din wasu abubuwane masu daraja da babu kamarsu,kudi ko qarfin iko basu isa su baka su ba.....ban gaya miki zamu nijeria ba wai don ina neman shawararki ba,umarni nake baki kaman yadda wadanda suka isa da ni suka bani umarni nabi,kema dole kibi umarni na don na isa da ke" ya miqe yana niyyar ficewa ranshi a bace
"To wallahi ba inda zani daga nan nima gidanmu zan wuce ai ina da gidan uba...." Waiwayowa yayi yana mata wani kallo daya sanyata rusuna ba tare data shirya ba
"Really?,....ok,indai haka ne idan kinje kada ki sake ki dawomin gida kinji ko?,ruwanki kije nigeria ruwanki kije ameria amma ki zauna acan,kada qafarki ta dawo gidan muhammad almustapha" yana kaiwa nan ya wuce yana mai buga qofar cikin fushi,kanta ta dafe,tabbas bata da wata mafita,zai iya aikata dukkan abinda yace din,saidai ta gama rayawa ranta abinda zatayi,zuwa gida babu fashi.