← Book details Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 226

Sashe 7

Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

     Basu ankara ba sukaji ana qwala kiran sallar la'asar,nan suka tashi sukayi,maman nana ta dubeta tace
"Ba zaki koma gida kiyi girki wa mukhtar bane"
"Ina som in koma maman nana amma ina zaton har yau basu tafi ba,bari na kira ya mukhtar din naji mai zai ce".

     Koda ta kirashi cewa yayi tayi zamanta kawai idan ya dawo din ya kirata ta dawo,a nan tayi zamanta suka ci gaba da hirarsu har su nana suka dawo daga islamiya,sai qarfe shida kiran mukhtar ya shigo wayarta,ta yiwa maman nana sallama ta wuce gida.

      Kaca-kaca ta tarad da gidan tun daga qofar gidan tamkar bata taba shara ba,kwalaye da ledojin abubuwan da suka jera duja ko ina a gidan,ga kwanukan abinci nan nata har da sabbi da bata taba amfani da su ba,da alama ma girki sukayi saboda kitchen din na bude zasu jerawa amarya nata kayan a ciki,mukhtar na tsaye a tsakar gidan riqe da qugu cikin bacin rai,da alama ransa ya baci da irin abinda sukayi,ga abincin da suka dafa din ma basu iya cinyewa ba sun kuma lalata bare a bawa wani,zai soma sababi ta shige jikinsa ta soma lallabashi,sai da ta sauke masa temper dinsa sannan ya tayata suka fara kintsa gidan fes.

     Kafin su kammala anyi kiran sallar magariba,ruwan wanka ta dora musu sannan sukayi alwala sukayi sallah,bayan sun idar ta juye musu ruwan sukayi wankan tare,ta shirya tsaf tayi kwalliya cikin qananun kaya,zata dora musu girki yace ta barshi kawai ya zura jallabiyyarsa ya fita.

    Cikin minti a shirin ya dawo da ledoji a hannunsa,ya ajjiye kan kujerar yana cewa
"Dauko faranti ki juye mana wannan,ki hado da cups,hala ma yau duka bakici abinci ba" murmushi tayi sanda take fita daga falon tana cewa
"Naci mana ya mukhtar a gidan maman naana" ,ta dawo dauke da plates din ta juye abinda ke cikin ledar.

     Tsire ne da zafinsa sai zuba qamshi yake,sai rabin gasashshiyar kaza,ta bude dayar ledar,lemon roba ne na fanta sai maltina wanda tasan ta mukhtar din ce tunda ita bata dameta ba.

       A nutse suke ci suna hirarsu jifa jifa kamar babu wani abu dake damunsu.

      Suna tsaka da ci wayar sa ta dauki qara,sumayya ta miqe ta isa inda take chargy ta ciro masa kana tazo ta miqa masa,baquwar lambace,yayi kamar bazai daga ba amma yadda kiran keta nacin shigowa ya sanyashi dagawa ya kara a kunnensa.

*mrs muhammad ce*

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 *~KUNDIN QADDARATA~*✍🏽
📖📖📖📖📖

*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)

_________________________

_Bismillahir rahmanir rahim_

*_la yadillu rabbi wala yansa_*
_______________________

*_ina taya maman farida(dan maliki,baya tsami banza,hanyan ruwa)murna sauka lafiya tare sa samun zan kadeden baby boy,Allah ya raya mana shi cikin musulunci,ya albarkaceshi,ya qara musu lafiya ita da babyn,sannan kuma muna kamu tun yanzu,lol_*

0⃣5⃣

    Sallama yayi maimakon ya amsa hello da ake faman cewa,yayi jim yana jiran amsa sallamar tukun,fahimtar abinda yake nufi da akayi ya sanya aka sa sallamar
"Da wa nake magana?",cikin karyar da murya akace
" mukhtar baka ganeni ba,fa'iza ce fa"
"Fa'iza?,wacce fa'iza" wani murmushi akayi mai fidda da sauti cikin siga ta nufin jan hankali
"Fa'iza amaryarka mana".

       Hade rai yayi kana cikin dakiya yace"ok,ya akayi?",sake marairaice murya tayi
"Haba mana mukhtar,ai ko gaisawa ka bari muyi tukunna ko?"
"Yayi kyau,ina gajiya?"
"Gata nan muna fama da ita mun fara shiga sabgogin biki,amma mukhtar ko marmarin sake zuwa guna bakayi,haba"
"Wannan ne dalilin da yasa kika kira ni?" Kai ta girgiza kamar tana gabansa,cikin ji haushin yadda yake amsa mata da qyar kamar wanda aka tilastawa
"A'ah ba shi bane"
"Fadi uzirinki kai tsaye".

      Gyara zama tayi sannan cikin salo da kisisina ta fara magana
"An ce daki falle daya ka bani,haba mukhtar,ya zaka bani daki falle daya sannan ka bawa uwar gidanka ciki da falo alhalin nice amarya ni nafi cancantar ciki da falo"tana direwa ya dora
"Ko?,a wanne hadisin?".

     Fara quluwa tayi amma ta dake"haka na ya dace ai"
"To ai babu damuwa,sai ki gayan nawa muka hada muka gina gidan sai na fidda miki haqqinki" ya fada cikin jin haushi da sigar gatse,da sauri tayi saurin cewa don kada kwabarta tayi ruwa
"Allah ya baka haquri ba nufina kenan ba" tayi saurin katse wayar,cilla wayar yayi gefe yana jan tsaki kana ya tsame hannunshi daga tsiren ya wuce daki.

      Itama kasa ci gaba da cin tayi,saboda haka ta tsame nata hannun ta fada wanka,ta gyara jikinta ta sanya kayan bacci sannan ta lullube farantin tsiren ta bishi da shi,cikin kwantar da murya da tausasa harshe ta sanya shi suka cinye tare.

      Ranar alhamis ta siyi relexer,nan saloon din dake bayan layinsu ta shiga aka wanke mata kanta aka busar mata cikin drayer,da yake tana da gashi babu laifi sai ya sake kyau ya kwanta sosai,daga nan bata shiga gida ba,gidan maman nana ta shiga wadda ta kwaba su madara ruwan kankana qwai su dilka da kurkur tana jiran dawowarta,ita ta gyare mata jikinta fes,zuwa la'asar ta fito shar,fatarta ta sake wani kyau da haske.

    Tsokanarta sosai mukhtar ya dinga yi,yana mata waqa
"Uwar gida na,amarya ta,amanata ki damqeta(waqar my habib(muhammad)" dariyar itama ta dinga yi.

     Ranar juma'a aka zo aka mata lalle ja da baqi,ta aika halima da zainab suka karbo mata dinkinta data bada kala takwas cikin kayanta,duka sai data gwada babu wanda bai mata kyau ba,a nan su halima suka kwanar mata da anty dije qanwar mamanta saboda washe gari asabar zata yi wuni saboda ranar sukace zasu kawo amarya.

       Wuni tayi babu laifi ta dan tara jama'a,sosai mutanen unguwar suka yi mata kara sun shishshigo,maqotanta na kusa da gidan ne suka zauna mata suna jira a kawo amarya su karbeta.

       Ana gab da sallar magariba ta shiga tayi wanka,ta sauya wasu kayan cikin kayanta,shadda ce ja wadda aka yiwa baqin stone work,kwalliya tayi mai kyau da tsari,sosai tayi kyau saidai komai da take yi cikin sanyin jiki take yinsa,haka nan take ta fama da fargaba da faduwar gaba,anty dije nata azalzalarta kan ta shirya kada 'yan kawo amarya su iso bata gama shiryawa ba,ta dauki turare ta feshe jikinta sannan ta nemi baqin mayafinta mai kyau da kwalliyar duwatsu ta yafa ta dawo falo.

       Tun magariba suke zuba idon ganin amarya har qarfe takwas na darw babu ita babu alamarta,hakan ya sanya maqotam suka fara tafiya da dai dai da dai dai saboda dawowar mazajensu,wasunsu kuma sun bar yara a gida,har tara shiru hakan ne yasa 'yan uwanta suka fara mata sallama suma saboda tafiya nasu gidajen,babu wanda za'a bar mata saboda anty dije tace hakan baiyi tsari ba,sai taji zuciyarta ta raurawa qwalla ta cika mata ido,bata san me zata yi ba batasan ya zata yi ba hakanan bata san yadda akeyi ba,anty dije da maman nana ne suka dinga kwantar mata da hankali tare da bata shawarwari wadanda suka sake sanya mata nutsuwa,sukayi mata sallama suka tafi,maman nana kawai ta rage.

       Qarfe goma na dare maman nanan na shirin tafiya itama ganin shirun yayi yawa sai ga hayaniyarsu da ta motocinsu,hakan ya sanyata ta koma ta zauna tana tsumayin isowarsu,saidai ga mamakinta yadda akeyi a al'adance a fara kai amarya ga uwargida su ba hakan bane,dakinta suka bude kai tsaye suka shige da ita suna faman yada kirari tamkar jinin maroqa
"Shiga da bismillah uwar 'ya'yan mukhtar".

       Da sauri maman nana ta soko ma sumayyan wata hirar don ta hana kunnuwanta jin abinda suke fadin,saidai ko kadan bata cimma nasara ba saboda wani tashin hankali da taji ya ziyarceta,gudun zuciyarta ya qaru,sai ta kalli maman nana
" maman naana,qirjina bugawa yake bansan me ya sameni ba"dan murmushin kwantar da hankali tayi mata
"Kada ki damu,wannan shi ake kira kishin,kiyita ambaton hasbunallahu wa ni'imal wakeel,ni'imal maula wa ni'iman nasir" kai ta kada hawaye na silalo mata,ta sanya hannunta ta share tana mai bawa kanta qwarin gwiwa tare da hana kanta da kanta kuka.

     Labule aka bankade aka shigo,fiddausi cs goye da 'yarta,ta dubi sumayyan sannan tace
"Kije dakin amarya,yaya bara'atu na son ganinki",cikin mamaki maman nana ta dubeta
" a'ah,ai ba'a haka,amaryar ai ya kamata tazo ko?"duban maman nanan tayi sai ta juya ta fice ba tare da tace komai ba.

     Ko minti daya ba'a qara ba saiga yaya bara'atun ta shigo
"Baiwar Allah ke a suwa kuma,wacece ke da har zaki hanata zuwa,to bari kiji,idan ma irin masu shige da fice ne gidan kishiyoyi suna hurewa kishiya kunne wahalar da sumayya kawai zakiyi,don zama fa'iza tazo yi ta kuma hayayyafa,ba mun kawota ne don ta tafi ba,saboda haka ke sumayya ina jiranki", wani abu yazo ya tokare maman nana a wuya,tamkar zata tanka sai taga hakan bashi da wani alfanu,tayi qoqarin kai zuciyarta nesa,saboda koda ta tanka din qila qarshe abun ya juye kan sumayyan wanda bazata so hakan ba,sai abun ya mata yawa ta rasa da wanne zata ji.

     Itama ta riqe hannun sumayyan cikin kalamai na qarfafa gwiwa ta mara mata baya har zuwa dakin marya,babu laifi dakin ya cinye komai nata kasancewar yana da yalwa,kuma ba wasu uban kaya suka mata ba,tunda gaba daya sun daga hankali ne anyi bikin cikin matsatstsen lokaci ba tare da sun gama shiryawa ba su kansu.

       Gefe daya suka samu suka zauna,sumayyan ta gaidasu daidaikum cikinsu suka amsa,maman nana kam babu wanda ta duba cikinsu don dama darajar sumayyan ya sanyata shigowa dakin,wata 'yar tsohuwa ce dake zaune gefan amarya wadda ta lullube fuskarta da mayafi tace
" to sumayyatu,ga 'yar uwa nan mun kawo miki,abokiyar zama,Allah ya baku zaman lafiya,muna fata zaku hada kanku ku zauna lafiya"
"Kowa ya kwana lafiya ai shi yaso ato,fa'iza dai gata nan zama daram ila yaumut takunu" yaya bara'atu ta karbe zancan daga gun tsohuwar,rai bace maman nana ta daga kai ta dubi yaya bara'atu,mamaki take bata,wai 'yar yarinyar da duka duka take cikin shekaru na sha takwas take zagewa babba da ita tana yadawa wadan nan habaice habaicen da suka girmi kanta,babu lallai ma kan nata ya iya dauka,ina laifi ma ta bar yaranta masu shekara sha hudu sha biyar su gayawa sumayyan?,wata qila ace wadan nan sine dai dai da ita,amma ba ita ba wadda ta kusa linka shekarun sumayyar ba.
Chapter 7 · 0% Book details