← Book details Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 226

Sashe 23

Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cike da hanzari fata da buri take barbada garin cikin abincin,don ta fuskanci cewa sam sumayya ko bude kwanon abinci bata yi ba,amma wannan karo taci alwashi kota halin qaqa sai ta sanya ta taci ko loma daya ce kai tama yankewa kanta ko dura ce sai tayi mata.

Tana karkade hannunta cikin nishadi taji caraf an riqe hannunta,tun kafin ta fahimci wake da alhakin riqe mata hannu gabanta yayi wata mummunar faduwa,a hankali tamkar wadda ta warke daga cutar laka ta daga kai suka hada idanu da mukhtar,wani matsanancin tsoro ya shigeta wanda kadan ya rage ta saki fitsari cikin wandonta sakamakon yadda taga idanunsa sun sauya kala cikin sakannin da basu wuce biyar ba.

Wani lafiyayyen mari ya yarfa mata wanda kafin ta ankare da a wanne hali taje ciki ya sake bin fuskarta da wani,hakan ne ya tilasta mata sakin wata gigitacciyar qara saboda ji taje tamkar fuskarta na shirin tsagewa ne,wannan shi yayi silar zaburar sumayya ta miqe ta fito a razane tana tsammanin ko gobara ce ta kama gidan nasu tunda ta bar fa'iza ne cikin kitchen.

Fitowarta yayi dai dai da wurgo fa'iza da mukhtar yayi zuwa filin tsakar gidan
"Subhanallahi" sumayya ta fada da qarfi tana nufar inda fa'iza take don ta d'agata
"Kika tabata sai mun samu mummunan sabanin da bamu taba samun makamancinsa ba ni da ke,sai nayi matuqar saba miki" taji mukhtar na ambata cikin wata kakkausar murya da bata taba zata yana da ita ba.

Yadda ya sake nufo fa'iza gadan gadan ya tsoratasu baki daya,sumayya ta janye gefe jikinta na rawa,bakinta na ambatar duk wata addu'a da tazo bakinta tare da neman agajin Allah ya kawo sauqin kowacce iriyar masifa da zata faru yau a gidan,yayin da tsoron da fa'iza taji ya sanyata sakin ihun neman agaji domin tsantsar bala'in da zata fuskanta ya fito muraran cikin idanun mukhtar tun kafin ya kai ga aiwatar da shi a kanta.

*mrs muhammad ce*

📚📚📚📚✍✍✍✍
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖

*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)

2⃣0⃣

_____________________

*bismillahir rahmanir rahim*

*wa may yatawakkal alal lahi fahuwa hasbuh,innallaha baligu amrih*
_____________________

             Duban sumayya cikin shaqaqqiyar murya yace
"Jeki ki rufemin qofar gidan" tsayawa tayi tana dubansa jikinta na rawa,ta fuskanci me yake nufi,wato don kada ma ihun fa'iza ya sanya ta samu masu kawo mata dauki kenan
"Jeki ki rufemin qofar gida nace" ya maimaita cikin tsawa ganin bata da niyyar tafiya,jikinta na rawa ta wuce taje ta rufo,bata kai ga dawowa tsakar gidan ba kuwa taji ana bugun qofar gidan,daga inda yake ya bata umarnin kada ta bude ta dawo ciki.

             Ga mamakinta fa'iza ke bawa mukhtar haquri hannu bibbiyu take roqonsa,bai ko dubeta ba sai sumayya da ya kalla
"Shiga kitchen ki dauko min cooler dinki wadda take zuba miki abinci" babu musu wannan karon ta shiga ta fito da ita,ya nuna maga gaban fa'iza da ido ta dire anan din ta koma gefe ta tsaya jikinta na rawa.

              "Maza bude ki cinye abincin dake ciki yanzu yanzun nan" wani rugugin aradun tashin hankali ya rufto mata,tirqashi,ai data ci abincin ciki gwara mukhtar din ya kwana ya wuni yana jibgarta,domin cin abinci koda shinkafa qwaya tak dake ciki ne dai dai yake da ban kwana da duniyarta,sai ta zube a qasa tana sake roqarsa yayi haquri kuskure tayi kuma ba zata sake ba,wani murmushi mai tauri da d'aci ya saki
"Ko baki fada ba ai dama har abada ba zaki sake aikata irn wannan mummunan aikin ba cikin gidan mukhtar,afuwa daya da zan iya yi miki idan kina da buqatarta shine ki dauki abincin nan ki cinye salun alun"
"Wallahi muntari bazan iya ci ba,zan iya rasa rayuwata,kayi haquri"sai yayi turus ya zuba mata idanu cike da fargaba da kuma bacin rai
" kice ma niyyar kisan kai kika yi?,sumayyar tawa zaki kashemin?"ya fada cikin wani irin zafin rai,da sauri ta girgiza kai tare da sake debo wata rantsuwa don gyara baran baramar da take gab da sake tafkawa,ganin taqaddamar take qarewa har muntarin na nade hannu zaiyiwa fa'iza dure ya sanya sumayya dake gefe kamar mutum mutumi magantuwa,ta tabbata tunda har fa'izan ta toge kan bazata ci ba komai zaya yi mata ya nuna akwai wani mummunan abu da ta qulla cikin abincin,wanda su kansu basu san meye ba,ba kuma su san sakamakon da hakan zaya haifar ba idan taci din
"Ya mukhtar,ka qyaleta don Allah,koma meye tunda Allah ya kubutar da ni bayan muna da masaniyar ba wayon mu bane sai mu gide masa ko?"
"Ok,haka ne fa" ya fada yana gyada kai tare da duban sumayyan,saidai kallo daya tayi masa ta fuskanci bawai yana nufin ya haqura din bane
"Shikenan ki bar cin abincin" ya fada yana juyawa zuwa dakinsa.

           Murmushin nasara da farinciki fa'iza ta saki tana duban sumayya duba na wulaqanci
"An gaya miki haihuwa kayan banza ce?,ni na sani ko darajar cikinsa dake jikina kawai ta isheni,banza mara amfani ke zaki ci gaba da diban kayan takaici juya kawai wad...........".

               Fitowar mukhtar dauke da belt ita ta maqale sauran zazzafar maganar da take da burin ci gaba da yabawa sumayya,tsayawa yayi gabanta yana gyara belt din tare da fadin
" babu batun cin abinci amma wallahi baki ci banza ba,sai na fanshe wahala da baqinciki rashin zaman lafiya da rashin kwanciyar hankalin da kika shigo kika haddasawa gidanmu,kinga gobe sai ki koyi darasin zaman duniya"kafin su ankara ya fara jibgarta tako ina,tsoro da firgici ya hana sumayya tabuka komai,abinda iyatsawon rayuwarsu bata taba gani mukhtar yayi ba,duka duka koda ga qaramin yaro bare ga matarsa ta aure,lallai babu shakka fa'iza na shirin koyawa mijinsu mummunar aqida idan bata tashi tayi da gaske ba,don daga haka miji ke farawa idan ba'ayi wasa ba.

               Ta nufeshi da hanzari da niyyar dakatar da shi saidai tuni ya hankadata gefe cikim zafin rai ba tare da ya san yayi ba,a rashin sa'a ta fadi kuwa kan hannunta wanda sai da ya bada wani sauti ta saki kalmar wash! Cikin azaba,bata sake yunqurin tashi ba ta zubawa sarautar Allah ido.

              Sai da ya tabbatar ta daku sannan ya dakata yana dubanta
"Ki tatattara duk wani tarkace naki da kika san kin shigo gidan nan da su ki koma inda kika fito,na sakeki saki biyu" wani ihu ta kurma kamar zautacciya tana shirin miqewa tsaye
"Wallahi baki isa ba muntari,zama daram wallahi sai na haife abinda ka qusa min ma rainshi sannan" wata dariya ya saki sannan ya miqa hannunsa ya fincikota tare da fusge zanin jikinta.

               Idanu sumayya dake zaune dirshan kan sumunti ta qwalalo ganin abinda ya fado jikin fa'iza wanda da shi ake canza tafiya ake burga ake kira ciki ne,cikin ma kuma wai na mukhtar dinta,tarin zannuwa ne aka hadasu aka qulle cikin zani daya fa'izan ke daurawa
"Indai ciki ne gashi nan yau kin haifeshi ko,rainonsa kuma sai ki ajjiyemin kayana  ko ni zan raini abu na" ya fada yana qyalqyalewa da dariya,gaba daya wani muzanci ya kama fa'iza,me kenan?,meke shirin faruwa?,dama mukhtar yasan ba ciki bane shi yasa ya qyaleta,shi yasa bai nuna farinciki ba da result din bogi data bashi,bata kammala karanta wasiqar jakin ba maganar mukhtar din ta kuma katseta
"Kin maida mukhtar wawa shashasha jaki irinki ko?,don kinci sa'a na qyaleki tun lokacin ban hukunta ki ba kan raina kin wayo da kikayi ba?,to wallahi kada ki yadda na fito a wanka na taddaki cikin gidan nan,idan ba haka ba kowanne laifi da kika aikata cikin gidan nan iya tsawon zaman da kikayi cikinsa sai na miki hisabinsa tare da hukunci akansa daya bayan daya" ya fada yana yarda belt din ya dauki sabulunsa da ya watse gefe ya shige wankansa.

             Cikin tsananin radadin ciwukan da taji ta miqe ta shige dakinta,bata yi ko minti biyar ba ta fito dauke da jaka da hijabi,har ta gota ta dawo da baya ta dubi sumayya
"Wallahi wallahi kada ki dauka kinci nasara a kaina,yanzu aka fara wasan" ta fada tana mai ficewa da sauri jin motsin mukhtar na niyyar fitowa saga bandakin.

            Bin qofar data fice din yayi da kallo domin yaso ya taddata,sai a lokacin ya maida dubansa ga sumayya
"Me take gaya miki?" Bata amsashi ba sai niyyar miqewa da take amma ta kasa,ganin haka ya sanyashi qarasa gurinta da sauri yana nufin riqe mata hannu ta saki qara da sauri sabida gun ciwon ya taba
"Subhanallahi,hannu kuma sumayya?" Ya tambayeta yana duban gun,banza tayi da shi cikin son yunqurin tashi yayi niyyar taimaka mata da sauri tace
"Barni,bana so" ta tattara qarfinta ta miqe ta nufi dakinta.

            Binta yayi a baya da sauri,tana shirin shiga dakin ya cafkota,qara ta saki saboda hannun ya riqe,sosai ya murde hannun har sai da ya bada qara alamun inda ya gulle ya koma dai dai,kafin ya kammala ta gama hada gumi,jikinta yayi laushi ya jata cikin jikinsa yana goge mata hawaye da gumin da ta hada.

         Cikin kujera ya ajjiyeta yana maida ajiyar zuciya ya fice zuwa dakinsa.

_busy!busy!!! Wlh_

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍✍✍✍
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖

*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)

2⃣1⃣

*innal laha ma'assabirin*

            Cikin qanqanin lokaci yayi wankan ya shirya cikin shadda sea grean,sosai tayi masa kyau,itama sabuwa ce cikin sabbin dinkunan da yayi shima,ya kulle gidan suka fito.

           Sai daya bude mata gidan gaba ta shiga sannan ya zagaya shima ya shiga daya bangaran yana duban ta,yadda fuskarta ta cika da farinciki tana masa addh'a,sosai yaji dadi cikin zuciyarsa shima,yayi bismillah ya tada motar suka fice daga layin a hankali.

               Suna tafe suna hirarsu cikin nishadi da walwala har suka iso qofar gidansu sumayyan,cikin zumudi ta bude ta fice mukhtar ya bita da kallo yana murmushi,tamkar yau ne ta fara zuwa gidan sai murna take.
Chapter 23 · 0% Book details