← Book details Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 78 OF 226

Sashe 78

Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

       Sai taso ta rude baki daya,ta dinga takawa a hankali tana tunanin inda zata shiga
"Muje na rakaki,naga alamar ko yaushe tsoron shigowa gidan nan kike,ko wani ne zaya kamaki?" Taji an ambata daga gefanta,waiwayawa tayi a hankali,mahmoud ne,yayi adonshi cikin shadda ruwan sea blue,ta masa kyau sosai ta fidda ainihin surarsa,murmushi ya subuce mata,sai ta girgiza kai kawai tana gaidashi,ya amsa mata suka fara takawa zuwa ciki
"Naga kowa tun daga ranar sallah da muka dawo zuwa yau,amma ke kam ban ganki ba,su laila tun dazu suna gidan nan,zaman gida bai damunki ne?" Murmushi ta sake saki tana kada kai
"To ina zanje,ba wanda na sani"
"Nan fa,nan ma gidanku ne,ko bakiga yadda su laila suka maidashi gidansu ba?"
"Haka ne" ta amsa masa don batasan me zata ce ba,shima shirun yayi suka ci gaba da takawa,suna gab da shiga bangaren anty maamaa yace
"Dama dai wani abun dadi kika kawowa baba,yau a gunsa zan maqale,kinsan ni da yaa man bamu cin abinci idan akayi buda baki har sai an kawo na gidan umman khalipha,yace shikam bai gane mana wannan wayon namu ba da muke maqale masa a kwanon,har gwara ni gauro ne shifa yaayaa fa" dariya ya bata har sai data murmusa,ta fuskanci mahmoud irin mutanen nan me masu barkwanci faran faran da saurin sabo da mutane.

        A falon anty maamaan suka ci burki,wasu 'yammata ne zaune a falon biyu na saman kujera biyu na qasa,kowacce ta baje kayan kwalliya suna makeup,baki daya sun cika falon da hira da karadi,kayan sawarsu na aje gefe da alamu fita zasuyi wata unguwa,kana dubansu zakasan suna daga cikin baqin da gidan ke karba a irin wannan lokaci,sallamar mahmoud ita ta janyo hankalinsu
"Anty maamaa" kawai ya fadi,daya daga cikinsu wadda ke qoqarin daura dankwalinta tace
"Tana G-kitchen" juyawa yayi ya dubi sumayya
"Idan baki gaji ba muje bata cikin nan" bata ce komai ba tabi bayansa yayin da 'yammatan suka bishi da kallo,wadda ke daura dankwalince ta tabe baki,kishi ne fal bayya ne a fuskarta,ta kusa da ita ce ta zungurota ganin yadda take binsu da kallo
"Uhmmm,yadai?" Qaramin tsaki ta ja
"Nikam baisan me yasa Allah ya zubawa mazan gidan nan girman kai ba,suna jin kamar su kadai ne halittar maza da Allah ya qirqira a ban qasa,jibi,kamar baisan wace ni ba" dariya wadda ke shafa powder ta qyalqyale da ita sannan ta tsaya da abinda take yi
"Kema kinsan su isa sun kai suyi girmankan,karfa ki manta su su waye?,kina zaton samunsu a bagas ne,nikam banga laifi ba don sunyi girman kai sun kai suyi ne,kibi a sannu idan da rabonki zaki shiga familyn prof,nikam tuni na sallama" ta fadi tana ci gaba da murza hodarta,shiru tayi bata sake cewa komai ba sai taci gaba da gyara daurin dankwalin nata cikin sanyin jiki.

      Bayan suka zagaya sai gasu cikin wani qaton kitchen wanda idan ba wajajen kayi ba ba lallai kasan da zamansa,kitchen ne babba mai dauke da electrics kala daban daban da manyan tukwane,kayan girki nau'i daban daban,kitchen ne da ma'aikatan gidan ke haduwa suyi amfani da shi duk lokacin bikin sallah irin wannan,biki ko suna na gidan idan ya tashi,gaidasu sumayyan tayi tare da yi musu sannu da aiki,antyn na tsaye sanye da jar shadda wadda keta maiqo da qyalli dinkin bubu da aka yiwa adon baqin zare,duk da ta tasamma shekara arba'in da kusan biyar amma sai ka zaci 'yar talatin ce,anty mama kam badai ado ba,tana sabe da wata kyakkyawar yarinya wadda aqalla zatayi shekara daya,an mata kwalliya cikin riga da wando,gashin kanta kuwa adin ribbom ne kala kala,ma'aikatan take sanarwa mai za'a dafa a mazaunin abincin dare a gidan baki daya
"Ah mahmoud yadai?,kun fasa tafiyar ne?" Ta fada bayan sun gama gaisawa da sumayya,shi kuma yana jan yarinyar dake kafadarta din da wasa wadda da alama itama jikar gidan ce,sumayyan na tsaye gefanta antyn riqe da hannunta daya
"A'ah,wannan mai tsoron shigowa gidan nan din na rako zata gaida baabaa" murmushi tayi ta juya tana kallon sumayya,haka nan sumayyan take burgeta tun ganin farko,da alamu zatayi nutsuwa,bata da rawar kai da fi'ili irin na 'yammatan zamani,shigarta kadai ta tabbatar mata da cewa daga babban gida ta fito,koda ba gidan da suke da kudi da ababen more rayuwa ba,a'ah,babban gida na nufin gidan mutunci da karamci,gidan da aka san dattako,gidan da usuli ilimi tarbiyya da wadatar zuci,gidan dake cike da tarbiyya da daraja
"Ba tsoro bane,baqunta ce" inji antyn tana murmushi,kusa da antyn ya matso bayan ya ajjye mata kwanon
"Nidai anty gashi nan,a tuna da ni idan baabaa zaici abinda ke cikin kwanon nan" hararsa tayi
"Haka fa,anqi aure anbi an takura mana miji,kunqi barinsa yayi auki,komai zaici sai kun tayashi" dariya ya sanya yana ficewa tare da fadin
"Wannan tsohon mijin naki anty ana ji da shi" itama dariyar tayi sabida tasan halin zolayar mahmoud,qarasa lissafa musu abinda ya dace tayi sannan ta dubi sumayya tace
"Bismillah" ta soma qoqarin tafiya tare da daukar kwanon,ganin haka ya sanya sumayyan matsawa kusa da antyn ta miqawa yarinyar hannu,zubawa sumayyan ido tayi tana kallonta,dariya anty tayi
"Wannan uwar qyuyar,Allah yasa ta yarda,uwarta na can ta tafi yawon saloon din da ba'a yishi ba sai yau ta barni da rigimamma" kamar taji kuwa abinda antyn tace sai ta miqawa sumayyan hannu alamar ta dauketa,ba antyn ba har masu aikin ta basu dariya,saboda kowa yasan qyuyarta ba da kowa take yarda ba
"Lallai kin ciri tuta mai sunan umma" ta kira sumayyan da haka saboda tuna sunan wace garesu,murmushi ta danyi tabi bayan antyn tana duban yarinyar,sai ta tuna mata abdallahnta,ko yanzu me yake?,tana kewarsa sosai,ta qagu lahadi tayi ta ganshi,sai kuma ta tuna yaranta wadanda ke tayata zama tun suna tsohon gidansu da mukhtar,su naana kam tasan yanzu sun girma,tana saka ran in sha Allah da zarar ta koma zata ziyarcesu,itakam tasan cewa son yara a jininta yake haka halittarta take,duk inda taga yaro ya dinga burgeta tana kallonsa kenan.

A hankali suke ratsa gidan anty maamaan na janta hira kadan kadan,jefi jefi suna gaisawa da mutane a kan hanya wanda da alama basu hadu bane tun safe sai yanzu,ba mamaki saboda girman gidan wanda ya iya hadiye duka baqin dake ciki,tun daga farkon sashen ta tabbatar da cewa akwai banbanci da sauran sasannin gidan,antyn dai na gaba tana bin bayanta,yarinyar na ci gaba da kallon sumayya tare da yi mata shirmen surutu irin na yaran dake son koyon magana ita kuwa na biye mata anty na binsu da murmushi har suka isa qofar da zata sadasu da babban falon dake mallakin mai gidan ne.

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖

*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)

6⃣0⃣

*Bismillahir rahmanir rahim*

*SHIN KO KUNSAN DUK LOKACIN DA AZABA TA TSANANTA GA DAN WUTA,FATAR JIKINSA TA KWASHE TA QONE,ANA SAUYA MASA WATA FATAR NE SANNAN ACI GABA DA GANA MASA AZABA*

*Allahumma la tada a lana zanban illa gafartah*

____________________________________

        Dattijo ne mai kimanin shekaru sittin da biyar zaune kan daya daga cikin kujeru na alfarma dake zagaye da falon,haiba kwarjini da kamala sun bayyana qarara kan fuskarsa,Allah yayi masa baiwar furfura tun daga gemu zuwa kansa,farin gilashi ke saye a fuskarsa baya ga shaddar dake jikinsa fala sol,dogon wando da riga mai gajeran hannu iya gwiwa,da alamu akwai babbar rigarsu wadda bai sanya ta ba,gefensa daga hannun dama samari ne guda uku,wanda ke daura da shi yana fuskantarsa sosai,bisa alamu magana suke mai muhimmanci,kyakkyawan matashine mai cike da kyau kwarjini izza da haiba,sanye yake da irin kayan tsohon bisa dukkan alamu anko sukayi,shi dinma fuskarsa sanye take da gilashin,daya hannun nashi ma wasu matasanne su biyu sai mata guda biyu.
Chapter 78 · 0% Book details