Sashe 21
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai tsaye sif dinsa ya wuce ya fidda jallabiya ya saka tana ta faman zuba masa surutu,ko daya bai kula ta ba sai sabgarsa ma da yake,har ya kammala ya zauna.
Cikin hanzari ta jawo abincin gabansa tana fadin bari ta zuba masa,idanu ya zuba mata harta kammala ta dago ta dubeshi suka hada idanu,signa ta masa sannan tace
"Gashi ya mukhtar sai ci ko"
"Qwarai kuwa" ya fada yana janyo abincin gabansa,fatanta daya kawai taga ya sanya koda loma guda bakinsa ne,hakan ya sanya ta bata dukka lokacinta yau ko girkin rana batayi ba cikin gidan ta tsara masa abincin da tasan yafi so.
Kamar ta sume don dadi sanda taga ya kai loma guda bakinsa sai kuma ya dakata ya ajjiye cokalin ba tare da yaci din ba,ya dubeta ya sakar mata wani murmushi
"Yau tare da ke nake sha'awar muci abincin,matso bismillah" tamkar an sanya guduma an doki qirjinta haka taji amma tayi hanzarin mazewa ta girgiza kai
"Haba ai ba girmanka bane,baka ne kai kadai" idanu ya zaro
"Au bakison samun matsayi kenan irin na sumayya bayan naga shi kike ta fafutukar samu maza matso,na saba tare muke cin abinci da ita duk ran girkinta" sai ta wani kamme ido a dole sai ta ja ra'ayinsa
"Haba muntari wannan ai ba tarbiyya bace,miji na diba kema na diba,kaci kawai ni a qoshe ma nake" kafada ya daga alamun rashin damwa daman ya san da kwanan hakan
"To shikenan,ba damuww,bari na kira sumayyan ta tayani ci" kamar ta tashi ta riqo shi haja taji amma don kada ta bada kanta sai ta dake.
Daga bakin qofar dakinsa ya coge ya kirata don kada ma ta samu damar sauya masa abincin,cikin mintuna qalilan sumayyan ta shigo dakin,kallonta yayi cikin salo na burgewa
"Yayarki ta qi tayani cin abinci shi yasa na gayyatoki ki tayani" sai ta danyi jim duk da murmushin da ta sanyawa fuskarta,ta sani cewa suna hada kwanon cin abinci ne kadai idan ranar girkinta ce.
Matsowa yayi da kwanon da sauri gabanta don kada ma ta musanta masa
"Oya,matso mana" da sauri fa'iza tayi tsallen albarka ta dira gabansu,ta sanya hannu ta rufe abincin,cikin daurw fuska tace
"Nifa gaskiya bana son haka,wannan ai bai kamata ba,ni ina shiga sha'aninku ranar kwananta ne,to nima ban lamunta ba girki kai daya na yiwa shi kuma kai zakaci" kallonta yake a nutse tsaf riqe da habarsa kamar yadda sumayyan ke kallonta,murmushi ya aje cikin nutsuwa
"Ikon Allah,to aikam nima ban yarda ba cikin biyu dole ki zabi daya,ko ki tayani ci ko my sumy ta tayani" ya fada yana sareta da idanunsa.
Take gumi ya yanko mata,ta fuskanci idan batayi da gaske ba wankin hula zai iya kaita dare,kafin ta kai ga cewa komai nepa suka kawo wuta,haske ya wadaci dakin,ba bata lokaci fuskar fa'iza ta bayyana,wadda tuni gumi ya yiwa jikinta sharkaf,ganin yadda suke kallon gumin ya sanya ta fara nade tabarmar kunya da hauka,wadda ta sake tonawa kanta asiri tsaf a gun mukhtar din ba tare da ta sani ba
"Lallai muntari,to me kake nufi?,kana nufin baka yarda da ni ba kenan?,ko kama nufin wani abu na zuba maka a ciki?"
"Ni bance kin zuba wani abu ba,amma tunda kika fada din akwai qamshin gaskiya cikin lamarin" miqewa tsaye tayi zata nade tabarmar kunya da hauka
"Lallai ma muntari,sharrin da zakamin kenan,sharrin d'a namijin da ake fada kenan yau yazo kaina,eh lallai ba shakka" tsawa ya daka mata ganin zata masa hauka ya miqe tsaye.
Kallon fuskarsa tayi ta tabbatar babu rahama a cikinta,take tsoro ya dirar mata abu ya hadu kuma da rashin gaskiya,sai taja da baya ganin yadda yayi dab da ita har tana jin hucin numfashinsa,tana niyyar guduwa ya damqi hannunta har da taji azaba har tsakiyar kanta
"Fa'iza!" Ya kira sunanta a matuqar kausashe,hantar cikinta ta kada tamkar zata saki fitsari a wandonta
"Basai na bata lokacina nayi doguwar magana da ke ba,wallahi wallahi duk ranar da kika sake yunqurin zuba min wani abu mai kama da sihiri ko surkulle sai kin raina kanki,ki kuma tabbatar daga ranar sunanki SAKAKKIYA!"
ba qaramin dukan qirjinta kalmar tayi ba,sam bata koda sha'awar jin wata kalma makamanciyar haka daga bakin muntarin,don ko kusa bata marmarin komawa gidansu wanda yake mata daidai da gidan kurkuku,gidan da talauci yunea babu masifa da rashin tarbiyya ya yiwa katutu.
Sakar mata hannu yayi cikin rawar jiki ta juya zata fice don baya da abun cewa,yanayinsa kadai ya tsoratata,balle ko shakka bata yi tasan cewa ya ganta ne muntarin,tsawa ya kuma daka mata ya bata umarnin ta dawo ta kwashe abincinta tasan yadda zatayi da shi baya da buqatar sa,haka ta kwashe kwanukan jiki na rawa ta fice.
*kuyi haquri da wannan*
*mrs muhammad ce*
📚📚📚📚✍✍✍✍
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
1⃣9⃣
_________________________
*Bismillahir rahmamir rahim*
*ala bi zikrillahi tad'ma innul quluub*
______________________
Mamaki fal zuciyar sumayya,kanta ya daure tamau,ta kasa furta ma komai sai kallon mukhtar da takeyi,ta tabbata ba qarya ya yiwa fa'iza ba domin ba halinsa bane,amma halayyar fa'iza har ta kai haka?.
"Ina naki abincin?" Mukhtar ya tambayeta,ta katse tunaninta ta dago ta dubeshi
"Ya d'aki"
"Ki dauko,ban amince kema. a yau kici ba,ki zuba a leda ki saka a shara a zubar,shiga kitchen ki samar mana abinda zamu ci koda indomie ce sai ki hada mana da qwai" ya fada yana kashingida gami da lumshe idanunsa,tsam ta miqe ta fice don aiwatar da abinda ya umarceta.
************************
Cikin kwanakin ta dage sosai da addu'ar neman tsari,ta san tabbas shartin mutum girma gareshi,zuwa yanzu ta kuma sallama kaidin fa'iza,ta fahimci irinsu matan da suka dauki kishi ko a mutu ko ayi rai,irinsu wadanda zash iya aikata komai saboda kishi,sosai take takatsantsan kan duk wani motsi da kai kawo nata a gidan,ba ruwanta da sabgar fa'izan bare wani abu ya shiga tsakaninsu,koda fa'izan zata shekara tana takalar tashin hankali bata bi ta kanta,don ta riga ta tabbatar cewa akwai banbancin gida da kowaccensu ta fito,bai kyautu ta biye mata su zamana kamar wadanda suka fito daga gurbi guda ba.
********************
Tun da asubahin ranar suka dinga jiyo kakarin amai a tsakar gidan nasu,sumayya ta dubi mukhtar dake gefanta wanda basu jima da kammala sallar asubahin ba kasancewar sun makara basu tashi da wuri ba
"Ya mukhtar,kamar kakarin amai nake ji fa a tsakar gida" shi din ma taji amma sam bai da muradin fita,tamkar bazai tanka ba sai ya daure yace
"Eh nima naji" yaci gaba da jan carbinsa,ganin yayi shiru ya sanya ta sake cewa
"Ya mukhtar ka duba mana,inajin kamar fa'iza ce fa" shiru ya sake mata ganin hakan ya sanya itama ta tsuke bakinta tayi shiru tana ci gaba da sauraran kakarin wanda yake fita tamkar da kayan cikinta,ya kammala azkar dinsa ya haye gado abinsa ya kashingida.
Zuciyar musulunci ya sanyata ta kasa daurewa,sai ta miqe ta fidda hijabin jikinga ta nufi qofa,sanya baki yayi ya kirata tare da tambayarta ina zata
"Zanje na duba ne,bai kyautu da mutane cikin gidan ba kuma aqi fita a dubata ba,bamu san meke damunta ba" kai ya girgiza
"Dawo tausa nake so kimin"
"Kayi haquri naje na dubata din minti biyu kawai zan dawo sai na maka tausar"
"Idan ban isa da ke ba shikenan kina iya hakan" ya fada yana maida kansa ya kwantar kan pillow,sai jikinta yayi sanyi bata son saba masa ko kadan,saboda haka ta juyo a sanyaye tahaye gadon.
A tausashe take masa tausar tana leqen fuskarsa ganin yaqi kulata,har ta soma tara qwalla bata iya jure fushinsa,sai taji kawai ya birkitota ya danneta da rabin jikinsa yana dariya qasa qasa
"Raguwa kawai sarkin kuka" ya fada yana lakuce mata hanci,dariya ta saki ya shiga mata cakulkuli daga haka suja shige duniyar ma'aurata wanda hakan shi ya hanasu fitowa da wuri.
Qarfe goma ya gama shirinsa zaya fita,a tsakar gida daga can bakin qofar dakin fa'izan suka ganta zaune dirshan a qasa,ta wani wargaje can qafa can qafa tana numfashi da qyar,da sauri sumayya ta qarasa inda take tana fadin
"Hasbunallahu lafiya fa'iza?"
"Bani da lafiya" ta fada qasa qasa da qyar,ta daga kai ta kalli mukhtar da bai qaraso gun ba,yana tsaye abunsa bakin qofar dakin sumayyan yana daura agogo
"Yaya mukhtar,ko asibiti zamu?" Baice komai ba sai hannunsa da ya sanya cikin aljihun wandonsa ya zaro naira dubu biyu ya miqa mata
"Gashi sai kun dawo Allah ya kiyaye hanya" ya sanya kansa soro ya tada machine dinsa ya fice.
Tana jin rufe qofar gidan nashi ta miqe tamkar ba itace hajaran majaran ba,duk da yanayin jikinta ya nuna bata da qwari sosai,ta sakarwa sumayya harara sannan ta wafce kudin dake hannunta
"Babu inda zaki rakani munafuka" ta fada tana shigewa dakinta,kada kai sumayya tayi cikin zuciyarta tana fadin
"Allah ka shirya,wato hali zanan dutse".
Tana daki tana shafa mai bayan ta kammala wanka ta jiyo fitar fa'izan.
Suna zaune zasu ci abincin dare bayan ya kammala komai,tana gabansa tayi kyau cikin kwalliyar lace ja mai adon baqi tana zuba masa abincin data shirya musamman saboda shi fa'iza tayi sallama ta shigo dakin fuskarta qunshe da murmushi hannubta riqe da farar takarda,daya daga cikin kujerun dakin sumayyan ta samu ta zauna,fuskarsa a hade ya dubeta
" daga ina kike takwas na dare?"sai ta rausayar da ido
"Haba mana muntari,ka tsaya kaji ji da nazo maka da daddadan labari"
"Ba wannan ba ki fara amsa min tambayar da na miki tukunna"
"Kash,labarin da zan baka yanzun duka yafi wannan muhimmanci,amma tunda ka nace sai kaji to daga asibiti jikina ya rikice sai na wuce gida na kwanta acan,sai da magariba na danji dama dama" shiru yayi ya soma cin abincinsa,ganin haka ya sanya tace
"Ka godewa Allah muntari,Allah ya kusa cika maka burinka da ka dade kana fata,ka kusa zama baba,an auna ni ina da juna biyu har na wata biyu".
Qwarewa yayi da lomar abincin da ya kai bakinsa,sai ya soma tari babu qaqqautawa,cikin hanzari sumayya ta miqa masa ruwan tana jujjuya maganar cikin ranta,indai hakan gaskiya ne to ya tabbata ITACE BATA HAIHUWA?.
Cikin hanzari ta jawo abincin gabansa tana fadin bari ta zuba masa,idanu ya zuba mata harta kammala ta dago ta dubeshi suka hada idanu,signa ta masa sannan tace
"Gashi ya mukhtar sai ci ko"
"Qwarai kuwa" ya fada yana janyo abincin gabansa,fatanta daya kawai taga ya sanya koda loma guda bakinsa ne,hakan ya sanya ta bata dukka lokacinta yau ko girkin rana batayi ba cikin gidan ta tsara masa abincin da tasan yafi so.
Kamar ta sume don dadi sanda taga ya kai loma guda bakinsa sai kuma ya dakata ya ajjiye cokalin ba tare da yaci din ba,ya dubeta ya sakar mata wani murmushi
"Yau tare da ke nake sha'awar muci abincin,matso bismillah" tamkar an sanya guduma an doki qirjinta haka taji amma tayi hanzarin mazewa ta girgiza kai
"Haba ai ba girmanka bane,baka ne kai kadai" idanu ya zaro
"Au bakison samun matsayi kenan irin na sumayya bayan naga shi kike ta fafutukar samu maza matso,na saba tare muke cin abinci da ita duk ran girkinta" sai ta wani kamme ido a dole sai ta ja ra'ayinsa
"Haba muntari wannan ai ba tarbiyya bace,miji na diba kema na diba,kaci kawai ni a qoshe ma nake" kafada ya daga alamun rashin damwa daman ya san da kwanan hakan
"To shikenan,ba damuww,bari na kira sumayyan ta tayani ci" kamar ta tashi ta riqo shi haja taji amma don kada ta bada kanta sai ta dake.
Daga bakin qofar dakinsa ya coge ya kirata don kada ma ta samu damar sauya masa abincin,cikin mintuna qalilan sumayyan ta shigo dakin,kallonta yayi cikin salo na burgewa
"Yayarki ta qi tayani cin abinci shi yasa na gayyatoki ki tayani" sai ta danyi jim duk da murmushin da ta sanyawa fuskarta,ta sani cewa suna hada kwanon cin abinci ne kadai idan ranar girkinta ce.
Matsowa yayi da kwanon da sauri gabanta don kada ma ta musanta masa
"Oya,matso mana" da sauri fa'iza tayi tsallen albarka ta dira gabansu,ta sanya hannu ta rufe abincin,cikin daurw fuska tace
"Nifa gaskiya bana son haka,wannan ai bai kamata ba,ni ina shiga sha'aninku ranar kwananta ne,to nima ban lamunta ba girki kai daya na yiwa shi kuma kai zakaci" kallonta yake a nutse tsaf riqe da habarsa kamar yadda sumayyan ke kallonta,murmushi ya aje cikin nutsuwa
"Ikon Allah,to aikam nima ban yarda ba cikin biyu dole ki zabi daya,ko ki tayani ci ko my sumy ta tayani" ya fada yana sareta da idanunsa.
Take gumi ya yanko mata,ta fuskanci idan batayi da gaske ba wankin hula zai iya kaita dare,kafin ta kai ga cewa komai nepa suka kawo wuta,haske ya wadaci dakin,ba bata lokaci fuskar fa'iza ta bayyana,wadda tuni gumi ya yiwa jikinta sharkaf,ganin yadda suke kallon gumin ya sanya ta fara nade tabarmar kunya da hauka,wadda ta sake tonawa kanta asiri tsaf a gun mukhtar din ba tare da ta sani ba
"Lallai muntari,to me kake nufi?,kana nufin baka yarda da ni ba kenan?,ko kama nufin wani abu na zuba maka a ciki?"
"Ni bance kin zuba wani abu ba,amma tunda kika fada din akwai qamshin gaskiya cikin lamarin" miqewa tsaye tayi zata nade tabarmar kunya da hauka
"Lallai ma muntari,sharrin da zakamin kenan,sharrin d'a namijin da ake fada kenan yau yazo kaina,eh lallai ba shakka" tsawa ya daka mata ganin zata masa hauka ya miqe tsaye.
Kallon fuskarsa tayi ta tabbatar babu rahama a cikinta,take tsoro ya dirar mata abu ya hadu kuma da rashin gaskiya,sai taja da baya ganin yadda yayi dab da ita har tana jin hucin numfashinsa,tana niyyar guduwa ya damqi hannunta har da taji azaba har tsakiyar kanta
"Fa'iza!" Ya kira sunanta a matuqar kausashe,hantar cikinta ta kada tamkar zata saki fitsari a wandonta
"Basai na bata lokacina nayi doguwar magana da ke ba,wallahi wallahi duk ranar da kika sake yunqurin zuba min wani abu mai kama da sihiri ko surkulle sai kin raina kanki,ki kuma tabbatar daga ranar sunanki SAKAKKIYA!"
ba qaramin dukan qirjinta kalmar tayi ba,sam bata koda sha'awar jin wata kalma makamanciyar haka daga bakin muntarin,don ko kusa bata marmarin komawa gidansu wanda yake mata daidai da gidan kurkuku,gidan da talauci yunea babu masifa da rashin tarbiyya ya yiwa katutu.
Sakar mata hannu yayi cikin rawar jiki ta juya zata fice don baya da abun cewa,yanayinsa kadai ya tsoratata,balle ko shakka bata yi tasan cewa ya ganta ne muntarin,tsawa ya kuma daka mata ya bata umarnin ta dawo ta kwashe abincinta tasan yadda zatayi da shi baya da buqatar sa,haka ta kwashe kwanukan jiki na rawa ta fice.
*kuyi haquri da wannan*
*mrs muhammad ce*
📚📚📚📚✍✍✍✍
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
1⃣9⃣
_________________________
*Bismillahir rahmamir rahim*
*ala bi zikrillahi tad'ma innul quluub*
______________________
Mamaki fal zuciyar sumayya,kanta ya daure tamau,ta kasa furta ma komai sai kallon mukhtar da takeyi,ta tabbata ba qarya ya yiwa fa'iza ba domin ba halinsa bane,amma halayyar fa'iza har ta kai haka?.
"Ina naki abincin?" Mukhtar ya tambayeta,ta katse tunaninta ta dago ta dubeshi
"Ya d'aki"
"Ki dauko,ban amince kema. a yau kici ba,ki zuba a leda ki saka a shara a zubar,shiga kitchen ki samar mana abinda zamu ci koda indomie ce sai ki hada mana da qwai" ya fada yana kashingida gami da lumshe idanunsa,tsam ta miqe ta fice don aiwatar da abinda ya umarceta.
************************
Cikin kwanakin ta dage sosai da addu'ar neman tsari,ta san tabbas shartin mutum girma gareshi,zuwa yanzu ta kuma sallama kaidin fa'iza,ta fahimci irinsu matan da suka dauki kishi ko a mutu ko ayi rai,irinsu wadanda zash iya aikata komai saboda kishi,sosai take takatsantsan kan duk wani motsi da kai kawo nata a gidan,ba ruwanta da sabgar fa'izan bare wani abu ya shiga tsakaninsu,koda fa'izan zata shekara tana takalar tashin hankali bata bi ta kanta,don ta riga ta tabbatar cewa akwai banbancin gida da kowaccensu ta fito,bai kyautu ta biye mata su zamana kamar wadanda suka fito daga gurbi guda ba.
********************
Tun da asubahin ranar suka dinga jiyo kakarin amai a tsakar gidan nasu,sumayya ta dubi mukhtar dake gefanta wanda basu jima da kammala sallar asubahin ba kasancewar sun makara basu tashi da wuri ba
"Ya mukhtar,kamar kakarin amai nake ji fa a tsakar gida" shi din ma taji amma sam bai da muradin fita,tamkar bazai tanka ba sai ya daure yace
"Eh nima naji" yaci gaba da jan carbinsa,ganin yayi shiru ya sanya ta sake cewa
"Ya mukhtar ka duba mana,inajin kamar fa'iza ce fa" shiru ya sake mata ganin hakan ya sanya itama ta tsuke bakinta tayi shiru tana ci gaba da sauraran kakarin wanda yake fita tamkar da kayan cikinta,ya kammala azkar dinsa ya haye gado abinsa ya kashingida.
Zuciyar musulunci ya sanyata ta kasa daurewa,sai ta miqe ta fidda hijabin jikinga ta nufi qofa,sanya baki yayi ya kirata tare da tambayarta ina zata
"Zanje na duba ne,bai kyautu da mutane cikin gidan ba kuma aqi fita a dubata ba,bamu san meke damunta ba" kai ya girgiza
"Dawo tausa nake so kimin"
"Kayi haquri naje na dubata din minti biyu kawai zan dawo sai na maka tausar"
"Idan ban isa da ke ba shikenan kina iya hakan" ya fada yana maida kansa ya kwantar kan pillow,sai jikinta yayi sanyi bata son saba masa ko kadan,saboda haka ta juyo a sanyaye tahaye gadon.
A tausashe take masa tausar tana leqen fuskarsa ganin yaqi kulata,har ta soma tara qwalla bata iya jure fushinsa,sai taji kawai ya birkitota ya danneta da rabin jikinsa yana dariya qasa qasa
"Raguwa kawai sarkin kuka" ya fada yana lakuce mata hanci,dariya ta saki ya shiga mata cakulkuli daga haka suja shige duniyar ma'aurata wanda hakan shi ya hanasu fitowa da wuri.
Qarfe goma ya gama shirinsa zaya fita,a tsakar gida daga can bakin qofar dakin fa'izan suka ganta zaune dirshan a qasa,ta wani wargaje can qafa can qafa tana numfashi da qyar,da sauri sumayya ta qarasa inda take tana fadin
"Hasbunallahu lafiya fa'iza?"
"Bani da lafiya" ta fada qasa qasa da qyar,ta daga kai ta kalli mukhtar da bai qaraso gun ba,yana tsaye abunsa bakin qofar dakin sumayyan yana daura agogo
"Yaya mukhtar,ko asibiti zamu?" Baice komai ba sai hannunsa da ya sanya cikin aljihun wandonsa ya zaro naira dubu biyu ya miqa mata
"Gashi sai kun dawo Allah ya kiyaye hanya" ya sanya kansa soro ya tada machine dinsa ya fice.
Tana jin rufe qofar gidan nashi ta miqe tamkar ba itace hajaran majaran ba,duk da yanayin jikinta ya nuna bata da qwari sosai,ta sakarwa sumayya harara sannan ta wafce kudin dake hannunta
"Babu inda zaki rakani munafuka" ta fada tana shigewa dakinta,kada kai sumayya tayi cikin zuciyarta tana fadin
"Allah ka shirya,wato hali zanan dutse".
Tana daki tana shafa mai bayan ta kammala wanka ta jiyo fitar fa'izan.
Suna zaune zasu ci abincin dare bayan ya kammala komai,tana gabansa tayi kyau cikin kwalliyar lace ja mai adon baqi tana zuba masa abincin data shirya musamman saboda shi fa'iza tayi sallama ta shigo dakin fuskarta qunshe da murmushi hannubta riqe da farar takarda,daya daga cikin kujerun dakin sumayyan ta samu ta zauna,fuskarsa a hade ya dubeta
" daga ina kike takwas na dare?"sai ta rausayar da ido
"Haba mana muntari,ka tsaya kaji ji da nazo maka da daddadan labari"
"Ba wannan ba ki fara amsa min tambayar da na miki tukunna"
"Kash,labarin da zan baka yanzun duka yafi wannan muhimmanci,amma tunda ka nace sai kaji to daga asibiti jikina ya rikice sai na wuce gida na kwanta acan,sai da magariba na danji dama dama" shiru yayi ya soma cin abincinsa,ganin haka ya sanya tace
"Ka godewa Allah muntari,Allah ya kusa cika maka burinka da ka dade kana fata,ka kusa zama baba,an auna ni ina da juna biyu har na wata biyu".
Qwarewa yayi da lomar abincin da ya kai bakinsa,sai ya soma tari babu qaqqautawa,cikin hanzari sumayya ta miqa masa ruwan tana jujjuya maganar cikin ranta,indai hakan gaskiya ne to ya tabbata ITACE BATA HAIHUWA?.