Sashe 145
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Karon farko data fara shiga sashen tunda take zuwa gidan,kamar sauran sassan gidan haka yake saidai duka ya fisu qaawa da burgewa,biye take da anty maamaa jikinta asanyaye,kai tsaye anty maamaan ta miqawa amiran muqullan hannunta ta bata umarnin bude dakunan,sannan ta jiya da ita kafin amiran ta bude dakin suka nufi qofofin kitchen,nata ta bude mata ta nuna mata,komai na a tsare masha Allah,babu abinda ba'a tanadarwa kitchen din ba na kayan amfani,dakin farko ta fara nuna mata sannan na biyu,a nan ta zaunar da ita gefan gado sannan itama ta zauna kan kujerar dake fuskantar gadon
"To mamanmu,ga gidanki nan ga dakunanki nan,daya dakin naki yana sama saidai naga kamar mai gidan kamar baya nan shi yasa bai kanki can ba,nasan zaya nuna miki idan ya dawo,duk abinda zan gaya miki nasan tuni an fada miki tun daga gida,almustapha dai mijinki je biyayya gareshi wajibi ne a gareki,kamar yadda tilas ne ya kyautata miki,bari na fada miki wani sirri na mallakar miji cikin sauqi,yi nayi bari na bari,ma'ana biyayya da kyautatawa,haquri da kai zuciya nesa,wannan shine kadai abinda zan qara miki a kai,Allah ya baku zaman lafiya ya hada kanku baki daya,ga kayan lefanki can kusan fiye da rabi a dinke suke,nasan baki taho da abubuwan buqatarki ba saidai kina iya amfani da su,amira ki tayata ku sanya kayan cikin wardrobe amma kada ki wuce awa daya,kema wucewa zakuyi keda saifullahi kada yazo yayita jiranki"
"To anty" ta fada tana miqewa,kusan sumayya bata da kuzarin da zata yi aikin,amiran ce ta shirya mata duo kayan dake a dinke,sai data gama ta dubeta cike da tsokana tana mata nuni da cikin sif din
"Wadannan kayan gida ne,nan bangaren qananun kaya ne na zaman falo,don bance ki raga ba wajen sanyasu,can sashin kuma kayan daukan magana ne na zuwa turaka kin gane ai?" Ta fada tana daga gira,duk yadda take ji a zuciyarta sai data bata dariya
"Kin fara rainani amira,kada ki manta nifa yayarki ce yanzu"
"Eh wallahi afuwa,amma sai mun fadi gaskiya,sai ma nan da kwana hudu zamu dawo ni da nafisa,sai mun baje miki aiki" ta fada tana ficewa daga sashen da gudu tana dariya,da idanu sumayya ta fita kafin daga bisani ta dauke idanunta tana girgiza kai,tana ji dama itace amiran,ba shakka babu abinda yake rayuwa cikin farinciki ba tare da matsala ba dadi.
Kowanne huduba da ta samu daga kowanne sashi tayi tasiri cikin ruhi da zuciyarta,ta fuskanci kowanne sashe dake da muhimmanci a rayuwarta na supporting wannan aure,wanda ita har yau zurfin tunaninta baikai ga hango abinda su suka hango din ba,a hankali ta bude qofar toilet din dake maqale cikin bedroom din,bandaki ne wadatacce wanda aka qawatashi da dukkan wasu kayayyakin amfani na bandakin zamani,ruwan zafi dana sanyi ta hada yadda take buqata ta shower don bata fiya son shiga bathtube ba.
Ta jima gaban kayan tana kallon yadda amiran ta shirya mata su,kai kawai take kadawa,batasan wacce iriyar qauna amiran ke mata ba,bata da abinda zata saka mata da shi qauna ce daga Allah,da hannu ta dinga taba kayan baccin har ta ciro wasu cotton masu kauri,riga da wando ne dogon wando,iyakar rigar cinya saidai hannun nata dogo ne,bayan ta sanya ta isa gaban mudubi,ga mamakinta irin mayukan da take amfani da su ne da turarukanta,ta tabbatar da cewa wannan aikin amiran ne shima,murmushi ta sake saki tana fadin
"Amira?,amira?,hmm"sai data hade gashinta waje daya sannan ta soma mutststsuka mai bayan ta feshe jikinta da turarukanta.
A fujajan haka ta shigo gidan tamkar wadda aka koro,akwatinta qwaya daya aharabar gidan ta barshi tana baiwa hadiman gidan umarni da su biyota da shi,babu kowa a falon,sauyin da falon ya sake samu kawai ya tabbatar mata ba shakka a yanzun ba ita daya bace mamallakiyar sashen,hakan ya sake tabbatar mata da cewa almustapha zai zama nasu ne su biyu ita da wata,kamar zautacciya haka ta shiha karkada kai ita daya tana fadin
"Ina!,sam wallahi zuciyata ba zata jure wannan ba" ta fada tana haurawa sama cikin hanzari,zuciyarta nata mata saqe saqen irin yanayin da wai zata iya zuwa ta tadda almustapha shi da amaryarshi,kishinta na hauhawa zuciyarta na sake haukata idanunta na kuma rufewa.
"To mamanmu,ga gidanki nan ga dakunanki nan,daya dakin naki yana sama saidai naga kamar mai gidan kamar baya nan shi yasa bai kanki can ba,nasan zaya nuna miki idan ya dawo,duk abinda zan gaya miki nasan tuni an fada miki tun daga gida,almustapha dai mijinki je biyayya gareshi wajibi ne a gareki,kamar yadda tilas ne ya kyautata miki,bari na fada miki wani sirri na mallakar miji cikin sauqi,yi nayi bari na bari,ma'ana biyayya da kyautatawa,haquri da kai zuciya nesa,wannan shine kadai abinda zan qara miki a kai,Allah ya baku zaman lafiya ya hada kanku baki daya,ga kayan lefanki can kusan fiye da rabi a dinke suke,nasan baki taho da abubuwan buqatarki ba saidai kina iya amfani da su,amira ki tayata ku sanya kayan cikin wardrobe amma kada ki wuce awa daya,kema wucewa zakuyi keda saifullahi kada yazo yayita jiranki"
"To anty" ta fada tana miqewa,kusan sumayya bata da kuzarin da zata yi aikin,amiran ce ta shirya mata duo kayan dake a dinke,sai data gama ta dubeta cike da tsokana tana mata nuni da cikin sif din
"Wadannan kayan gida ne,nan bangaren qananun kaya ne na zaman falo,don bance ki raga ba wajen sanyasu,can sashin kuma kayan daukan magana ne na zuwa turaka kin gane ai?" Ta fada tana daga gira,duk yadda take ji a zuciyarta sai data bata dariya
"Kin fara rainani amira,kada ki manta nifa yayarki ce yanzu"
"Eh wallahi afuwa,amma sai mun fadi gaskiya,sai ma nan da kwana hudu zamu dawo ni da nafisa,sai mun baje miki aiki" ta fada tana ficewa daga sashen da gudu tana dariya,da idanu sumayya ta fita kafin daga bisani ta dauke idanunta tana girgiza kai,tana ji dama itace amiran,ba shakka babu abinda yake rayuwa cikin farinciki ba tare da matsala ba dadi.
Kowanne huduba da ta samu daga kowanne sashi tayi tasiri cikin ruhi da zuciyarta,ta fuskanci kowanne sashe dake da muhimmanci a rayuwarta na supporting wannan aure,wanda ita har yau zurfin tunaninta baikai ga hango abinda su suka hango din ba,a hankali ta bude qofar toilet din dake maqale cikin bedroom din,bandaki ne wadatacce wanda aka qawatashi da dukkan wasu kayayyakin amfani na bandakin zamani,ruwan zafi dana sanyi ta hada yadda take buqata ta shower don bata fiya son shiga bathtube ba.
Ta jima gaban kayan tana kallon yadda amiran ta shirya mata su,kai kawai take kadawa,batasan wacce iriyar qauna amiran ke mata ba,bata da abinda zata saka mata da shi qauna ce daga Allah,da hannu ta dinga taba kayan baccin har ta ciro wasu cotton masu kauri,riga da wando ne dogon wando,iyakar rigar cinya saidai hannun nata dogo ne,bayan ta sanya ta isa gaban mudubi,ga mamakinta irin mayukan da take amfani da su ne da turarukanta,ta tabbatar da cewa wannan aikin amiran ne shima,murmushi ta sake saki tana fadin
"Amira?,amira?,hmm"sai data hade gashinta waje daya sannan ta soma mutststsuka mai bayan ta feshe jikinta da turarukanta.
A fujajan haka ta shigo gidan tamkar wadda aka koro,akwatinta qwaya daya aharabar gidan ta barshi tana baiwa hadiman gidan umarni da su biyota da shi,babu kowa a falon,sauyin da falon ya sake samu kawai ya tabbatar mata ba shakka a yanzun ba ita daya bace mamallakiyar sashen,hakan ya sake tabbatar mata da cewa almustapha zai zama nasu ne su biyu ita da wata,kamar zautacciya haka ta shiha karkada kai ita daya tana fadin
"Ina!,sam wallahi zuciyata ba zata jure wannan ba" ta fada tana haurawa sama cikin hanzari,zuciyarta nata mata saqe saqen irin yanayin da wai zata iya zuwa ta tadda almustapha shi da amaryarshi,kishinta na hauhawa zuciyarta na sake haukata idanunta na kuma rufewa.