Sashe 171
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
ta fahimci salon magana ce kawai ta qwatar kai,tunda da aiki ne da tuni ya shaidawa baba,amma ko baban baisan da zuwanshi ba,koma meye tana maraba kuma tana fatan alkhairi da samun wannan kyakkyawan canjin,sai ta saki murmushi
"Masha Allah" ta fada tana maida dubanta ga sumayya
"Me zaku ci,ko zaki shiga kitchen ki sama muku ko snacks ne,yau duka ma'aikatan na can baya suna aikace aikace suma"
"Am ok ummee" almustapha ya fadi,farinciki ya mamayetq,ta tabbata tunda ya fadi hakan hakanne,sai ta waiwaya ta dubi sumayya
"To kefa amira?"
"Nima ummee na......"
"Qarya take,ba abinda naga taci tunda muka taho" almustapha ya katseta yana tsareta da ido,murmushi ya subucewa ummee,salon da bata taba gani wajen almustaphan ba yau sai gashi da shi
"Maza shiga ki samu wani abu kici,halan shi kin sama masa wani abun yaci ke baki ci komai ha ko?" Cikin kunya tana murmushi ta miqe kanta a qasa tayi kitchen din,yayin da ya bita da kallo yana yabawa salon kunyarta,yanayin yadda take ganin girma da darajar mahaifansa,tunanin yadda cikin qan qanin lokaci kan ya gama shiryawa ta hada misi wani hadadden patatoe salad ya fado masa,ya jima baici hadin salad da ya masa dadi irin wannan na,murmushi ua dan qwace masa,yanayim takun ta na burgeshi,ya dauke kai sanda ta kai ga shigewa kitchen din,sai suka hada ido da ummee,shi yai qasa da kai kunya na lullubeshi,ita kuma ta dauke kai tana sakin murmushin tsantsar farinciki,waskewa yayi da cewa
"Ummee ya adam bai qaraso bane?"
"Ka fadi haka mana tunda wannan karon ka rigashi zuwa,ina zaton sai wajen laraba zai qaraso,amma dai ni'ima ya hadato da yaran sunyo gaba,dazun da safe suka sauka,shi da fahariyya sai ran laraban"kai ya gyada cikin gamsuwa
"Kunje kun gaida maamaan ne?"
"A'ah"
"To bari ta fito sai kuje ku gaisa,da alama itama batasan da zuwan naka ba,babanku kam baya gari,ya tafi jigawa ta'aziyyar wani abokinsu da ya rasu,amma gobe ma zaya dawo" ta fadi tana daga wayarta dake ringing wanda amira ce ke kiranta,bayan sun gaisa take shaida mata zuwansu sumayyan,ihu ta saki har almustapha dake zaune yana jiyota,hararar wayar yake kaman amiran ma wajen,magiya ta dinga kan ummee ta bata sumayyan ta kira wayanta a kashe,dai dai sanda sumayyan ke fitowa daga kitchen din,ummi ta miqa mata wayar,a ladabce ta amsa ta koma gefe tana fidda murmushi,addu'a kawai take kada amiran ta baro zance ta bata kunya,ai kuwa zuba ta hau yi
"Amma namecy kinci amanar qauna da baki gayan har kin iso abuja ba,halan soyayya ta fara zaqi har kin soma mancewa da kowa sai wannan miskilin mijin naki,ina fatan kina bada wuta wajen sukurkuta masa shi muga ta tsiya,tab ai wallahi jibi nima zan taho Allah,ina fata kin samo mana tsaraban baby,wallahi har so nake naga babynku,kyau tako ina,wazai dauko uwa ko uba?,wa yaga ya man ya baby" gaba daya kunya ta cika sumayyan,yadda almustapha kadai ya kafeta da ido tasan yanajin komai amiran ke fada,ta sanshi sarai da kaifin ji,yunqurin datse kiran take sai ya miqa mata hannu,a hankali ta tako ta miqa masa wayar,ya kara akunnensa sanda amiran ke cewa
"Wayyo soyayyya zamu sha kallo......"
"Gidanku mara kunya fitsararra,idan naga qafarki gidan nan jibi sai na karyata na zubar,idan kin musa kuma bismillah" ya datse kiran,daga bangaren amira sai ta kwabe fuska zata sanya kuka,saifullah dake zqune gefanta ya dunga tiqa dariya har da qwarewa da lemon da yake sh,haushi ya sanyata daukan filo ta dinga maka mishi shi kuwa yana fadin
"Maganin aku kuturu mai shegen zance kenan,tun dazun nake kwabarki kiyi a hankali may be suna tare amma kika qi ji,tunda kuwa ya man ya fadi haka ke da zuwa gida sai ana gobe daurin aure"kuka kuwa ta sanya taba buga qafa
"wallahi wallahi ban yarda ba,don kawai kaji ya almustapha ya fada ko?"sai ta saki filon ta wuce bedroom alamaun taji haushi ya miqe da sauri ya bita domin yayi lallashi.
Boye dariya ummin ta shiga yi tana basarwa,don itama taji wani abun,sauka yayi daga bangaren kira ya shiga wajen adana lambobi,da dai dai ya dinga bi har ya iso wajen lambar da ya tabbata tata ce saboda ga hotonta nan saman lambar,ya dauki wayar shi ya kwashe lambobin ya adana a tashi wayar,ganin yadda kunya ta rufe sumayyan yasa tace
"kuje ku gaida maamaa,daga nan ku wuce sashenku sai da safe ma hadu"
"To" ya fada yana sauke qafarshi wanda ya dora daya kan daya ya miqe ya isa gefan ummin ya ajjiye mata wayarta
"Sai da safe ummee" suka hada baki wajen fada sai da ya waiwayo ya dubeta,dauke kanta tayi ummen ta amsa
"Sai da safe,Allah ya bamu alkhairi".
Kusan bangaren anty maamaa wannan karon yafi jama'a,hakan baya rasa nasaba da kasancewar ita keda bikin wannan karon,auren yara biyu tak duka maza da Allah ya bata,baki ta kama itama
"almustapha?,tun yanzu?"murmushi kawai ya saki yana fatan kada ta sake cewa wani abu saboda 'yammatan dake falon,bai ko zauna ba hannunshi zube a aljihun wandonshi ya soma gaidata,ta amsa cikin farinciki itama,don ta tabbata lallai hasashen baban ya soma zama gaskiya,tunda ga mustpha ya waiwayi gida ana daurin auren qannenshi saura kwana shida,sumayya kam tuni tana wajen humaida,wadda sukayi farinciki ganin juna,ya waiwaya bayan sun gaisa,ganinta wajensu ya sanya ya basar ya juya ya fice,cikin sakewa suka gaisa da anty maman tana dan tsokanar sumayyan kafin ta miqe ta fice ta basu wuri,ta sake sosai cikinsu humaidan aka dinga hira,abinka da mata gwanayen gulma,kusan kowa kallon sumayyan yake,kowa da irin gulmar dake cinsa arai,yayin da dama daga cikinsu ke jin dama sune sumayyar,a qalla sai gashi sun kwashe wajen awa daya suna shan hirarsu,don humaida har kiran amira tayi ta saka handsfree aka dan taba da ita,hakan ya sake tsokalota taji kamar tayi tsuntsuwa ta taho.
Tun da ya shigo yaje duba agogo yana kasa kunne amma yaji shiru,har ya kammala shirin kwanciya cikin wasu hadaddun pyjamas masu shegen kyau da suka haska shi,yana son ya daure ya basar amma sai zuciyarsa ta gaza,a hankali ya sauko ya soma takawa ya sauka qasan benen,ya bude dakunan baccinta bai ga alamun ta shigo ba,ya koma sama ya bude dakin baccinta dake sama nan ma babu alamun an shiga,dakinshi ya koma ya zauna gefan gado yana son samin meke sanyashi damuwa haka da lamuranta?,laluba lambarta fake cikin wayrsa wadda yayi servinn dazu yayi sannan ya shiga bangaren aikawa da saqonni ya tura mata gajeran tex
"Come back", suna tsaka da hiransu saqon ya shigo,sai abun ya daure mata kai kasancewar bata da lambarsa,daga bisani ta ajjiye wayar tana zaton batan kai saqon yayi ba wayarta zai shigo ba,mintina goma suka shude shiru,ya sake lalubo lambar ya kira,bugu kusan uku sannan ta daga ta kara kunnenta,yana iya jiyo hayaniyar su ta cikin wayar,haka kawai tasha jinin jikinta duk da batasaj number din ba
"Assalamu alaikum" ta furta a nutse,har cikin zuciyarsa sallamar ta ratsashi,cikin zuciyarshi ya amsa a fili kuma yace
"Bance ki dawo gida ba?" Ta fahimci muryar sarai amma sai tace
"Waye ke magana?"
"Ok,baki gane ba kenan?"
"Eh" ta fada tana sani
"Well" ya ambata shima yana katse wayar,sai ta ajjiye wayar yana qoqarin saukowa daga saman gadon.
Anty maamaa ce ta sauko daga sama tana duban sumayya
"Lalala amiran umman khalipha?,me kike har yanzu baki wuce gida ba?,ya zaki baroshi shi kadai waya gaya miki ana wannan sakacin,tashi ki wuce tun bai biyo sawunki ba wallahi" ta fadi don tasan halin mustaphan sarai,murmushi ta saki yayim da su humaida suka sanya dariya,humaida tace
"Allah sarki mu da yake warin takalmi muke mu kwana muna hira ma ko anty"
"Yo wa ya damu da ku?", ta fada tana juyawa sama tare da yiwa sumayya sallama,dif dariyansu ta katse baki daya,kowa ya kama kanshi,hakan ya sanyata dagowa,sai ta ganshi tsaye cikin kayan bacci,takowa ya dinga yi a nutse har inda take sandare a atsaye,yasa hannu ya zare wayarta dake hannunta ya dauke cak,baki daya 'yammatan sukayi mutuwar zaune na wucin gadi har ita sumayyan,ko a jikinsa ya juya dauke da ita ya fice daga falon.
Kallon kallo aka soma yi tsakaninsu,humaida ce ta soma tuntsirewa da dariya,abun ya matuqar burgeta,kamar a fina finan india
" to wallahi tunda guy din nan ya soma haka mu rufawa kanmu a siri mu dinga kora masa matarsa da wuri,idan ba haka ba wataran sai munga abinda idanuwanmu ba zasu iya dauka ba"
"Wai shi dan air ba" inji wata daga cikinsu,wadda a zahirin gaskiya hassada take ji cikin zuciyarta,don itama taso ace ta zama daya daga cikin matanshi
"Ba wani dan air wallahi,har ga Allah abinda ya sanya nakesom auran irin mazan nan,nuna so babu limit ko a gaban waye wallahi,wani miskilin namijin bai iya nuna miki qauna ba,idanunshi basa gani balle suji kunyar kowa" dariya suka sanya suka ci gaba da tattaunawa kowa na fadar albarkacin bakinshi.
"Masha Allah" ta fada tana maida dubanta ga sumayya
"Me zaku ci,ko zaki shiga kitchen ki sama muku ko snacks ne,yau duka ma'aikatan na can baya suna aikace aikace suma"
"Am ok ummee" almustapha ya fadi,farinciki ya mamayetq,ta tabbata tunda ya fadi hakan hakanne,sai ta waiwaya ta dubi sumayya
"To kefa amira?"
"Nima ummee na......"
"Qarya take,ba abinda naga taci tunda muka taho" almustapha ya katseta yana tsareta da ido,murmushi ya subucewa ummee,salon da bata taba gani wajen almustaphan ba yau sai gashi da shi
"Maza shiga ki samu wani abu kici,halan shi kin sama masa wani abun yaci ke baki ci komai ha ko?" Cikin kunya tana murmushi ta miqe kanta a qasa tayi kitchen din,yayin da ya bita da kallo yana yabawa salon kunyarta,yanayin yadda take ganin girma da darajar mahaifansa,tunanin yadda cikin qan qanin lokaci kan ya gama shiryawa ta hada misi wani hadadden patatoe salad ya fado masa,ya jima baici hadin salad da ya masa dadi irin wannan na,murmushi ua dan qwace masa,yanayim takun ta na burgeshi,ya dauke kai sanda ta kai ga shigewa kitchen din,sai suka hada ido da ummee,shi yai qasa da kai kunya na lullubeshi,ita kuma ta dauke kai tana sakin murmushin tsantsar farinciki,waskewa yayi da cewa
"Ummee ya adam bai qaraso bane?"
"Ka fadi haka mana tunda wannan karon ka rigashi zuwa,ina zaton sai wajen laraba zai qaraso,amma dai ni'ima ya hadato da yaran sunyo gaba,dazun da safe suka sauka,shi da fahariyya sai ran laraban"kai ya gyada cikin gamsuwa
"Kunje kun gaida maamaan ne?"
"A'ah"
"To bari ta fito sai kuje ku gaisa,da alama itama batasan da zuwan naka ba,babanku kam baya gari,ya tafi jigawa ta'aziyyar wani abokinsu da ya rasu,amma gobe ma zaya dawo" ta fadi tana daga wayarta dake ringing wanda amira ce ke kiranta,bayan sun gaisa take shaida mata zuwansu sumayyan,ihu ta saki har almustapha dake zaune yana jiyota,hararar wayar yake kaman amiran ma wajen,magiya ta dinga kan ummee ta bata sumayyan ta kira wayanta a kashe,dai dai sanda sumayyan ke fitowa daga kitchen din,ummi ta miqa mata wayar,a ladabce ta amsa ta koma gefe tana fidda murmushi,addu'a kawai take kada amiran ta baro zance ta bata kunya,ai kuwa zuba ta hau yi
"Amma namecy kinci amanar qauna da baki gayan har kin iso abuja ba,halan soyayya ta fara zaqi har kin soma mancewa da kowa sai wannan miskilin mijin naki,ina fatan kina bada wuta wajen sukurkuta masa shi muga ta tsiya,tab ai wallahi jibi nima zan taho Allah,ina fata kin samo mana tsaraban baby,wallahi har so nake naga babynku,kyau tako ina,wazai dauko uwa ko uba?,wa yaga ya man ya baby" gaba daya kunya ta cika sumayyan,yadda almustapha kadai ya kafeta da ido tasan yanajin komai amiran ke fada,ta sanshi sarai da kaifin ji,yunqurin datse kiran take sai ya miqa mata hannu,a hankali ta tako ta miqa masa wayar,ya kara akunnensa sanda amiran ke cewa
"Wayyo soyayyya zamu sha kallo......"
"Gidanku mara kunya fitsararra,idan naga qafarki gidan nan jibi sai na karyata na zubar,idan kin musa kuma bismillah" ya datse kiran,daga bangaren amira sai ta kwabe fuska zata sanya kuka,saifullah dake zqune gefanta ya dunga tiqa dariya har da qwarewa da lemon da yake sh,haushi ya sanyata daukan filo ta dinga maka mishi shi kuwa yana fadin
"Maganin aku kuturu mai shegen zance kenan,tun dazun nake kwabarki kiyi a hankali may be suna tare amma kika qi ji,tunda kuwa ya man ya fadi haka ke da zuwa gida sai ana gobe daurin aure"kuka kuwa ta sanya taba buga qafa
"wallahi wallahi ban yarda ba,don kawai kaji ya almustapha ya fada ko?"sai ta saki filon ta wuce bedroom alamaun taji haushi ya miqe da sauri ya bita domin yayi lallashi.
Boye dariya ummin ta shiga yi tana basarwa,don itama taji wani abun,sauka yayi daga bangaren kira ya shiga wajen adana lambobi,da dai dai ya dinga bi har ya iso wajen lambar da ya tabbata tata ce saboda ga hotonta nan saman lambar,ya dauki wayar shi ya kwashe lambobin ya adana a tashi wayar,ganin yadda kunya ta rufe sumayyan yasa tace
"kuje ku gaida maamaa,daga nan ku wuce sashenku sai da safe ma hadu"
"To" ya fada yana sauke qafarshi wanda ya dora daya kan daya ya miqe ya isa gefan ummin ya ajjiye mata wayarta
"Sai da safe ummee" suka hada baki wajen fada sai da ya waiwayo ya dubeta,dauke kanta tayi ummen ta amsa
"Sai da safe,Allah ya bamu alkhairi".
Kusan bangaren anty maamaa wannan karon yafi jama'a,hakan baya rasa nasaba da kasancewar ita keda bikin wannan karon,auren yara biyu tak duka maza da Allah ya bata,baki ta kama itama
"almustapha?,tun yanzu?"murmushi kawai ya saki yana fatan kada ta sake cewa wani abu saboda 'yammatan dake falon,bai ko zauna ba hannunshi zube a aljihun wandonshi ya soma gaidata,ta amsa cikin farinciki itama,don ta tabbata lallai hasashen baban ya soma zama gaskiya,tunda ga mustpha ya waiwayi gida ana daurin auren qannenshi saura kwana shida,sumayya kam tuni tana wajen humaida,wadda sukayi farinciki ganin juna,ya waiwaya bayan sun gaisa,ganinta wajensu ya sanya ya basar ya juya ya fice,cikin sakewa suka gaisa da anty maman tana dan tsokanar sumayyan kafin ta miqe ta fice ta basu wuri,ta sake sosai cikinsu humaidan aka dinga hira,abinka da mata gwanayen gulma,kusan kowa kallon sumayyan yake,kowa da irin gulmar dake cinsa arai,yayin da dama daga cikinsu ke jin dama sune sumayyar,a qalla sai gashi sun kwashe wajen awa daya suna shan hirarsu,don humaida har kiran amira tayi ta saka handsfree aka dan taba da ita,hakan ya sake tsokalota taji kamar tayi tsuntsuwa ta taho.
Tun da ya shigo yaje duba agogo yana kasa kunne amma yaji shiru,har ya kammala shirin kwanciya cikin wasu hadaddun pyjamas masu shegen kyau da suka haska shi,yana son ya daure ya basar amma sai zuciyarsa ta gaza,a hankali ya sauko ya soma takawa ya sauka qasan benen,ya bude dakunan baccinta bai ga alamun ta shigo ba,ya koma sama ya bude dakin baccinta dake sama nan ma babu alamun an shiga,dakinshi ya koma ya zauna gefan gado yana son samin meke sanyashi damuwa haka da lamuranta?,laluba lambarta fake cikin wayrsa wadda yayi servinn dazu yayi sannan ya shiga bangaren aikawa da saqonni ya tura mata gajeran tex
"Come back", suna tsaka da hiransu saqon ya shigo,sai abun ya daure mata kai kasancewar bata da lambarsa,daga bisani ta ajjiye wayar tana zaton batan kai saqon yayi ba wayarta zai shigo ba,mintina goma suka shude shiru,ya sake lalubo lambar ya kira,bugu kusan uku sannan ta daga ta kara kunnenta,yana iya jiyo hayaniyar su ta cikin wayar,haka kawai tasha jinin jikinta duk da batasaj number din ba
"Assalamu alaikum" ta furta a nutse,har cikin zuciyarsa sallamar ta ratsashi,cikin zuciyarshi ya amsa a fili kuma yace
"Bance ki dawo gida ba?" Ta fahimci muryar sarai amma sai tace
"Waye ke magana?"
"Ok,baki gane ba kenan?"
"Eh" ta fada tana sani
"Well" ya ambata shima yana katse wayar,sai ta ajjiye wayar yana qoqarin saukowa daga saman gadon.
Anty maamaa ce ta sauko daga sama tana duban sumayya
"Lalala amiran umman khalipha?,me kike har yanzu baki wuce gida ba?,ya zaki baroshi shi kadai waya gaya miki ana wannan sakacin,tashi ki wuce tun bai biyo sawunki ba wallahi" ta fadi don tasan halin mustaphan sarai,murmushi ta saki yayim da su humaida suka sanya dariya,humaida tace
"Allah sarki mu da yake warin takalmi muke mu kwana muna hira ma ko anty"
"Yo wa ya damu da ku?", ta fada tana juyawa sama tare da yiwa sumayya sallama,dif dariyansu ta katse baki daya,kowa ya kama kanshi,hakan ya sanyata dagowa,sai ta ganshi tsaye cikin kayan bacci,takowa ya dinga yi a nutse har inda take sandare a atsaye,yasa hannu ya zare wayarta dake hannunta ya dauke cak,baki daya 'yammatan sukayi mutuwar zaune na wucin gadi har ita sumayyan,ko a jikinsa ya juya dauke da ita ya fice daga falon.
Kallon kallo aka soma yi tsakaninsu,humaida ce ta soma tuntsirewa da dariya,abun ya matuqar burgeta,kamar a fina finan india
" to wallahi tunda guy din nan ya soma haka mu rufawa kanmu a siri mu dinga kora masa matarsa da wuri,idan ba haka ba wataran sai munga abinda idanuwanmu ba zasu iya dauka ba"
"Wai shi dan air ba" inji wata daga cikinsu,wadda a zahirin gaskiya hassada take ji cikin zuciyarta,don itama taso ace ta zama daya daga cikin matanshi
"Ba wani dan air wallahi,har ga Allah abinda ya sanya nakesom auran irin mazan nan,nuna so babu limit ko a gaban waye wallahi,wani miskilin namijin bai iya nuna miki qauna ba,idanunshi basa gani balle suji kunyar kowa" dariya suka sanya suka ci gaba da tattaunawa kowa na fadar albarkacin bakinshi.