Sashe 130
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
So take ya sakar mata hannu ko don idanuwan mutane da ke kai kawo a wajen,uwa uba ga haramci na riqe mata hannu da yayi,tayi yunqurin zame hannun nata amma abu yaci tura yana tsaye qyam yana dubanta,babban goro sai magogin qarfe,ya kusa lullube tsahonta baki daya,dududun nata tsawon bata fi iya qirjinsa ba,ga wani kwarjini daya cika wajen,ganin masu wucewa sun soma ankara ya sanyata cewa
"Ka sakar min hannu" cikin izza da motsa labbansa
"Saikin gayan abinda ke baki tsoro,me ya koroki bayan kowa na kai kawo a nutse amma banda ke?" Daga fararen idanunta tayi ta watsa mishi su,duk da yadda qirjinta ke bugawa,lumshe idonsa yayi ya bude ya janye nashi idanun daga kallonta,bai taba ganin mace mai farin qwayar idanu ba kamar haka ya raya a ransa,tsaki yaja a fili sannan ya saki hannun nata
"Ki kula next time,ban son irin wannan shirmen" ya fada yana duban gefanta,ita ke shirmen ma?,abun ya bata haushi,sai ta banka masa harara ta gefan ido duk da yadda gabanta ke faduwa qasa qasa tace
"Kaima sai ka kula tunda kana da idanu ai ba ni kadai ke da idanuwa ba" batasan tayi kuskure ba saboda kaifin ji da Allah ya hore mishi,ko yaya magana take yana iya jiyota,yana daya daga cikin wadanda Allah ya yiwa baiwar ji,har wani lokaci ba'a iya gulmarsa matuqar yana cikin gidan,har yayi gaba ya juyo a mamakance yana dubanta,karo na farko kenan da wata 'ya ta taba maida masa magana,bakinta ta murguda duk don ta sake bashi haushi tayi gaba abinta,wani abu ya tsaya mishi a rai,ranshi ya baci,yau shi akewa rashin kunya?,abinda yafi tsana kenan a rayuwarsa tun lokacin quruciya,abinda ya fara hadashi kenan da su'adah tun tana qaramarsa,lallai zaiyi maganinta,wace ita da har take jin karanta ya kai tsaiko,babu shakka sai ya hukuntata.
A bangaren anty maamaa ta tadda su,tana zaune tsakiyar yayunta anty farida da anty huda da matan yayyen ta ni'imah da fahariyya,sai qawayenta da cousins dinta irinsu eesha humaida ummu salma da sauransu,a hankali ta qaraso saboda lasalar da take ji cikin jikinta tana karbar saqon harara daga amira,duk da haka murmushi ne kan fuskarta,ta riga da ta sani itace mai laifi,sauran da suka san mekw faruwa dariya suka dunga yi sunsan za'a kwashi daramer,amma sai sumayya ta kashe mata gwiwa da fadin
"Ta zama ta saifullahi,ayya yarinya zata bar gida" ai kuwa sai ta soma qwalla,tana dariya ciki ciki ta qaraso ta zauna gefanta ra mata rada a kunne ma tsawon minti biyu,sau gani sukayi ta saki dariya tana share hawayen,huda ce taja tsaki
"Au qaryar banza,dama fa son aurenta take 'yar banza bansani bane,saifullahin da ake ji da shi kamar a lashe mishi mazaunai" dariya ta kamasu baki daya,dqi dai da dai dai sumayya ta bi ta gaida kowa,batasan matan yaya adam ba sai lokacin ni'imah da fahariyya,fahariyya ita ta fara tahowa ni'imah ta jira maigidan sai jiya suka taho tare da daddare,bata ga fahariyyan ba saboda 'yar jin kaice itama kamar yadda amira ke gaya mata,ni'imah din ce babu ruwanga,hakanan take haquri da halayyar fahariyya na goranta mata da take lokaci lokaci akan rashin haihuwa,saidai zaman nasu babu yabi ba fallasa,rashin mutuncin fahariyyar da sauqi sakamakon cewa adam din tsayayyen namiji ne,bai yarda a wulaqanta masa uwar gida ba,sam basa shiri da su'adah da fahariyya saboda kowacce na jin kanta da jin cewa ta isa saidai daya tabi daya,duk da a zahiri duk cikin yaran gidan babu wanda ke da dukiyat almustapha,wannan ya qara kishin su'ad cikin zuciyar fahariyya,itakam ni'imah 'yar babu ruwa na ce,ta kama mutuncin kanta,don iyayenta ba wasu bane rufin asirin Allah ke garesu,sai a yanzu da tayi dace da miji na qwarai suke samun sauyin rayuwa sanadiyyarsa,duk da haka dama tana da managartan halaye wadanda su suka fusgi adam zuwa gareta,duk da tarin yaran masu kudi dake sonshi a lokacin,ta kasance ta daban a gunsa har a yanzun duk da bata taba haihuwa da shu ba,sakamakon haquri biyayya da tsantsar iya zamantakewa da miji mai tafiyar da hankali.
Da daidai suka miqe suka fice ya rage saga sumayyan sai anty ni'imah sai humaida,suma sun maqale ne saboda suna kwasar wasu sirrika da lacture da anty ni'iman ke bawa amira,wanda baga fara ba sai bayan da wadancan suka fita,ba amira ba hatta su sumayya sun qaru da ita sosai,a nan suka zauna suka ci gaba da hirarsu,ni'imah ba dai sauqin kai ba,kamar qannenta haka ta daukesu,aqalla zata girme musu da kusan shekaru goma,amma sam hakan bai wani nuna ba sosai sabida tsabar gayu.
Qarfe bakwai na magariba aka tafi kai amarya,babu wani takura ko neman mota kasancewar kusan kowa ya mallaki motar hawanshi,wanda ya taho daga wani garin ne bai taho da abun hawanshi ba sukayi amfani da motocin gidan baabaa,ga kuma ta familyn saifullahi.
Ba shakka wannan shi ake kira qwarya tabi qwarya,ba shakka amiran ta shiga gidan da yayi dai dai da ita,gidane na alfarma wanda ke tafiya da tunanin mai tunani,sanda aka fara tafiya amiran ta riqe sumayya gam kan sai ta jira anzo an sayi baki,sun riga da sun gama tsarawa babu batun siyan baki,ko akwai din ma ita batajin zata tsaya,saboda mutum biyu daga cikin abokan saifullahi da suka uzzurawa rayuwarta tun ranar kamu,ta musu qaryar a niger take,saboda haka bata son su hadu bare su takura ta,dabara tayi mata cewar bari taje tayi fitsari daga haka ta arto gida.
Biki ya tashi lafiya,ummee da kanta ta yi ma sumayyan godiya tare da godiyar kayan humra data yi mata wanda su aka jerawa amiran ma,kunya ce ta kama sumayyan,duka duka me tayi,su basu duba tarin karamcinsu wanda ya kai ga cancantarsu kan yi musu komai.
Tun a daren ta kashe wayarta kwata kwata,don ta tabbatar cewa gobe kamar da qasa sai amira ta nemeta,jikinta ya gaji tubus irin gajiyar da bata taba yin irinta ba,lallai biki ba wasa bane,tunda ta kwanta bata tashi ba sai da gari ya waye,ta makara sallar asuba,don sai shida da rabi ta yita,tana gamawa ta koma ta sake kwanciya,ba ita ta farka ba sai sha biyu saura na rana,yunwa ta sadakarta,a guje tayi kicin ta tadda anty dije na soya miya qamshinta ya cika gidan baki daya,ba magana ta mata nuni da kayan break dinta dake ajjiye gefe,tana kaiwa baki daya yiwa antyn sannu da aiki
"Ai ke zanwa sannu,yaran nan sunso tadaki badon ma hanasu ba,shi yasa da abbansu zai fita na hadasu da shi ya kaisu wajen inna(kakarshi)"
"Kai kina ji da ni anty na" ta fada tana jan kujera don ta ji dadin cin abincin sosai
"Ba dole ba,kece fa babbar diya" suka sanya dariya baki daya sannan suka ci gaba da hira suna tattauna wasu daga lamuran da suka faru yayin bikin,antyn na juye miyar cikin warmer tace
"Ai ke kam bakiga hutu ba,saura sati uku a shiga wani bikin"
"Wallahi anty shi yasa nakeso nayi kamar kwana uku haka ina bacci,don so nake next week na wuce kano" hararata antyn tayi
"Dama na sani ai,ke kam garin nan kamar yana mintsininki,gidan fa baki daya baya dadi wallahi idan kika tafi,hatta da abbansu ya dinga mitar kin dade,amma wani lokaci sai na rayawa a raina dole fa mu saba tunda wataran zaki aure,idan kika tafi kuma ya zamuyi" shiru sumayyan tayi taci gaba da kurbar tea,saboda anty dijen ta kawo zancan da bata qauna cikin hirar tasu,sai data gama sha ta sure cup din tana goge hannunta sannan tace
"Anty,wata tambaya ce da ni"
"Uhmmm,Allah yasa na sani" shiru ya danyi tana tsara yadda zata jefa mata tambayar kafin tace
"Wai idan wata ko wani yazo ya cewa budurwa ki taimaka ki gyara rayuwar wane,wai me hakan yake nufi?" Waiwayowa tayi ta kalleta har sai da gaban sumayya ya fadi,Allah yasa ba wani mummunan abu bane,kamar antyn ta tambayeta wa ya fadawa wani hakan sai kuma ta fasa,taci gaba da aikinta tana bata amsa
"Maganar na da ma'ana bangare biyu,nq farko idan har aka fadi haka ga wani ko wata makusanciya ta mutum ana nufin ta dinga bashi shawara da hanashi aikata wasu abubuwa,ko kuma wani abu na son faruwa da shi ana son ka taimaka kada ya fada cikin wannan abun,sannan ma'anar na iya daukan AURE ko SOYAYYA,abun nufi.......shi wanda ya gaya miki maganar yana ganin kamar kina da wasu qualities da wani namiji ke buqata,wanda wannan qualities din zau taimaka masa wajen gyaruwa ko ingantuwar rayuwarsa,babu kuma hanyar da zaki gyara ko ki inganta rayuwar tasa sai ta hanyar AURENSA ko yin SOYAYYA da shi,to sai a baka maganar a dunqule" tunda ta dauko maganar gaban sumayyan ke faduwa
"Da gaske baba na nufin kenan ta auri almustapha?,abinda baabaa ke son fadi mata kenan" kai ta shiga girgizawa cikin zuciyarta ta soma furta
"La haula wala quwwata illa billah,Allah ka sani ina ganin qima da darajar wannan bawa naka,ya Allah ka fidda masa wannan tunanin daga zuciyarsa a kaina,ka jefa masa tunanin wata,Allah kada ka bashi iko ya tambayi abinda bazan iya masa ba"
"Ke sumayya meye haka?" Inji anty dije ganin yadda take kada kai tana mus mus da baki,murmushin yaqe na musamman ta qaqalo sannan tace
"Ba komai,kawai ina mamakin yadda muka kasa fassarar maganar,wani ne ya gayawa wata" ta fada tana miqewa tsaye sannan ta fice daga kitchen din,da kallo anty dije ta bita,cikin zuciyarta tana addu'a,Allah ubangiji ya sanya sumayyan tayi gamo da miji ne dan gaske,wanda zata huce takaicinta,babu shakka zata so za kuma tayi burin sumayyan tayi auren da zata huta ta sanadiyyarta,juyawa tayi taci gaba da aikinta tana addu'a cikin ranta.
A sanyaye ta zauna bakin gado maganar na sake y mata yawo,indai haka ne ba shakka dole ta qauracewa haduwar ta da baabaa,kai ya zame mata jazaman tafiya kano,kuma bata jin zata dawo nan kusa idan ta tafi din,zata yita qirqiro dalilai ne wadanda zasu zaunar da ita a can.
"Ka sakar min hannu" cikin izza da motsa labbansa
"Saikin gayan abinda ke baki tsoro,me ya koroki bayan kowa na kai kawo a nutse amma banda ke?" Daga fararen idanunta tayi ta watsa mishi su,duk da yadda qirjinta ke bugawa,lumshe idonsa yayi ya bude ya janye nashi idanun daga kallonta,bai taba ganin mace mai farin qwayar idanu ba kamar haka ya raya a ransa,tsaki yaja a fili sannan ya saki hannun nata
"Ki kula next time,ban son irin wannan shirmen" ya fada yana duban gefanta,ita ke shirmen ma?,abun ya bata haushi,sai ta banka masa harara ta gefan ido duk da yadda gabanta ke faduwa qasa qasa tace
"Kaima sai ka kula tunda kana da idanu ai ba ni kadai ke da idanuwa ba" batasan tayi kuskure ba saboda kaifin ji da Allah ya hore mishi,ko yaya magana take yana iya jiyota,yana daya daga cikin wadanda Allah ya yiwa baiwar ji,har wani lokaci ba'a iya gulmarsa matuqar yana cikin gidan,har yayi gaba ya juyo a mamakance yana dubanta,karo na farko kenan da wata 'ya ta taba maida masa magana,bakinta ta murguda duk don ta sake bashi haushi tayi gaba abinta,wani abu ya tsaya mishi a rai,ranshi ya baci,yau shi akewa rashin kunya?,abinda yafi tsana kenan a rayuwarsa tun lokacin quruciya,abinda ya fara hadashi kenan da su'adah tun tana qaramarsa,lallai zaiyi maganinta,wace ita da har take jin karanta ya kai tsaiko,babu shakka sai ya hukuntata.
A bangaren anty maamaa ta tadda su,tana zaune tsakiyar yayunta anty farida da anty huda da matan yayyen ta ni'imah da fahariyya,sai qawayenta da cousins dinta irinsu eesha humaida ummu salma da sauransu,a hankali ta qaraso saboda lasalar da take ji cikin jikinta tana karbar saqon harara daga amira,duk da haka murmushi ne kan fuskarta,ta riga da ta sani itace mai laifi,sauran da suka san mekw faruwa dariya suka dunga yi sunsan za'a kwashi daramer,amma sai sumayya ta kashe mata gwiwa da fadin
"Ta zama ta saifullahi,ayya yarinya zata bar gida" ai kuwa sai ta soma qwalla,tana dariya ciki ciki ta qaraso ta zauna gefanta ra mata rada a kunne ma tsawon minti biyu,sau gani sukayi ta saki dariya tana share hawayen,huda ce taja tsaki
"Au qaryar banza,dama fa son aurenta take 'yar banza bansani bane,saifullahin da ake ji da shi kamar a lashe mishi mazaunai" dariya ta kamasu baki daya,dqi dai da dai dai sumayya ta bi ta gaida kowa,batasan matan yaya adam ba sai lokacin ni'imah da fahariyya,fahariyya ita ta fara tahowa ni'imah ta jira maigidan sai jiya suka taho tare da daddare,bata ga fahariyyan ba saboda 'yar jin kaice itama kamar yadda amira ke gaya mata,ni'imah din ce babu ruwanga,hakanan take haquri da halayyar fahariyya na goranta mata da take lokaci lokaci akan rashin haihuwa,saidai zaman nasu babu yabi ba fallasa,rashin mutuncin fahariyyar da sauqi sakamakon cewa adam din tsayayyen namiji ne,bai yarda a wulaqanta masa uwar gida ba,sam basa shiri da su'adah da fahariyya saboda kowacce na jin kanta da jin cewa ta isa saidai daya tabi daya,duk da a zahiri duk cikin yaran gidan babu wanda ke da dukiyat almustapha,wannan ya qara kishin su'ad cikin zuciyar fahariyya,itakam ni'imah 'yar babu ruwa na ce,ta kama mutuncin kanta,don iyayenta ba wasu bane rufin asirin Allah ke garesu,sai a yanzu da tayi dace da miji na qwarai suke samun sauyin rayuwa sanadiyyarsa,duk da haka dama tana da managartan halaye wadanda su suka fusgi adam zuwa gareta,duk da tarin yaran masu kudi dake sonshi a lokacin,ta kasance ta daban a gunsa har a yanzun duk da bata taba haihuwa da shu ba,sakamakon haquri biyayya da tsantsar iya zamantakewa da miji mai tafiyar da hankali.
Da daidai suka miqe suka fice ya rage saga sumayyan sai anty ni'imah sai humaida,suma sun maqale ne saboda suna kwasar wasu sirrika da lacture da anty ni'iman ke bawa amira,wanda baga fara ba sai bayan da wadancan suka fita,ba amira ba hatta su sumayya sun qaru da ita sosai,a nan suka zauna suka ci gaba da hirarsu,ni'imah ba dai sauqin kai ba,kamar qannenta haka ta daukesu,aqalla zata girme musu da kusan shekaru goma,amma sam hakan bai wani nuna ba sosai sabida tsabar gayu.
Qarfe bakwai na magariba aka tafi kai amarya,babu wani takura ko neman mota kasancewar kusan kowa ya mallaki motar hawanshi,wanda ya taho daga wani garin ne bai taho da abun hawanshi ba sukayi amfani da motocin gidan baabaa,ga kuma ta familyn saifullahi.
Ba shakka wannan shi ake kira qwarya tabi qwarya,ba shakka amiran ta shiga gidan da yayi dai dai da ita,gidane na alfarma wanda ke tafiya da tunanin mai tunani,sanda aka fara tafiya amiran ta riqe sumayya gam kan sai ta jira anzo an sayi baki,sun riga da sun gama tsarawa babu batun siyan baki,ko akwai din ma ita batajin zata tsaya,saboda mutum biyu daga cikin abokan saifullahi da suka uzzurawa rayuwarta tun ranar kamu,ta musu qaryar a niger take,saboda haka bata son su hadu bare su takura ta,dabara tayi mata cewar bari taje tayi fitsari daga haka ta arto gida.
Biki ya tashi lafiya,ummee da kanta ta yi ma sumayyan godiya tare da godiyar kayan humra data yi mata wanda su aka jerawa amiran ma,kunya ce ta kama sumayyan,duka duka me tayi,su basu duba tarin karamcinsu wanda ya kai ga cancantarsu kan yi musu komai.
Tun a daren ta kashe wayarta kwata kwata,don ta tabbatar cewa gobe kamar da qasa sai amira ta nemeta,jikinta ya gaji tubus irin gajiyar da bata taba yin irinta ba,lallai biki ba wasa bane,tunda ta kwanta bata tashi ba sai da gari ya waye,ta makara sallar asuba,don sai shida da rabi ta yita,tana gamawa ta koma ta sake kwanciya,ba ita ta farka ba sai sha biyu saura na rana,yunwa ta sadakarta,a guje tayi kicin ta tadda anty dije na soya miya qamshinta ya cika gidan baki daya,ba magana ta mata nuni da kayan break dinta dake ajjiye gefe,tana kaiwa baki daya yiwa antyn sannu da aiki
"Ai ke zanwa sannu,yaran nan sunso tadaki badon ma hanasu ba,shi yasa da abbansu zai fita na hadasu da shi ya kaisu wajen inna(kakarshi)"
"Kai kina ji da ni anty na" ta fada tana jan kujera don ta ji dadin cin abincin sosai
"Ba dole ba,kece fa babbar diya" suka sanya dariya baki daya sannan suka ci gaba da hira suna tattauna wasu daga lamuran da suka faru yayin bikin,antyn na juye miyar cikin warmer tace
"Ai ke kam bakiga hutu ba,saura sati uku a shiga wani bikin"
"Wallahi anty shi yasa nakeso nayi kamar kwana uku haka ina bacci,don so nake next week na wuce kano" hararata antyn tayi
"Dama na sani ai,ke kam garin nan kamar yana mintsininki,gidan fa baki daya baya dadi wallahi idan kika tafi,hatta da abbansu ya dinga mitar kin dade,amma wani lokaci sai na rayawa a raina dole fa mu saba tunda wataran zaki aure,idan kika tafi kuma ya zamuyi" shiru sumayyan tayi taci gaba da kurbar tea,saboda anty dijen ta kawo zancan da bata qauna cikin hirar tasu,sai data gama sha ta sure cup din tana goge hannunta sannan tace
"Anty,wata tambaya ce da ni"
"Uhmmm,Allah yasa na sani" shiru ya danyi tana tsara yadda zata jefa mata tambayar kafin tace
"Wai idan wata ko wani yazo ya cewa budurwa ki taimaka ki gyara rayuwar wane,wai me hakan yake nufi?" Waiwayowa tayi ta kalleta har sai da gaban sumayya ya fadi,Allah yasa ba wani mummunan abu bane,kamar antyn ta tambayeta wa ya fadawa wani hakan sai kuma ta fasa,taci gaba da aikinta tana bata amsa
"Maganar na da ma'ana bangare biyu,nq farko idan har aka fadi haka ga wani ko wata makusanciya ta mutum ana nufin ta dinga bashi shawara da hanashi aikata wasu abubuwa,ko kuma wani abu na son faruwa da shi ana son ka taimaka kada ya fada cikin wannan abun,sannan ma'anar na iya daukan AURE ko SOYAYYA,abun nufi.......shi wanda ya gaya miki maganar yana ganin kamar kina da wasu qualities da wani namiji ke buqata,wanda wannan qualities din zau taimaka masa wajen gyaruwa ko ingantuwar rayuwarsa,babu kuma hanyar da zaki gyara ko ki inganta rayuwar tasa sai ta hanyar AURENSA ko yin SOYAYYA da shi,to sai a baka maganar a dunqule" tunda ta dauko maganar gaban sumayyan ke faduwa
"Da gaske baba na nufin kenan ta auri almustapha?,abinda baabaa ke son fadi mata kenan" kai ta shiga girgizawa cikin zuciyarta ta soma furta
"La haula wala quwwata illa billah,Allah ka sani ina ganin qima da darajar wannan bawa naka,ya Allah ka fidda masa wannan tunanin daga zuciyarsa a kaina,ka jefa masa tunanin wata,Allah kada ka bashi iko ya tambayi abinda bazan iya masa ba"
"Ke sumayya meye haka?" Inji anty dije ganin yadda take kada kai tana mus mus da baki,murmushin yaqe na musamman ta qaqalo sannan tace
"Ba komai,kawai ina mamakin yadda muka kasa fassarar maganar,wani ne ya gayawa wata" ta fada tana miqewa tsaye sannan ta fice daga kitchen din,da kallo anty dije ta bita,cikin zuciyarta tana addu'a,Allah ubangiji ya sanya sumayyan tayi gamo da miji ne dan gaske,wanda zata huce takaicinta,babu shakka zata so za kuma tayi burin sumayyan tayi auren da zata huta ta sanadiyyarta,juyawa tayi taci gaba da aikinta tana addu'a cikin ranta.
A sanyaye ta zauna bakin gado maganar na sake y mata yawo,indai haka ne ba shakka dole ta qauracewa haduwar ta da baabaa,kai ya zame mata jazaman tafiya kano,kuma bata jin zata dawo nan kusa idan ta tafi din,zata yita qirqiro dalilai ne wadanda zasu zaunar da ita a can.