Sashe 209
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Qarar bude qofar falon nata da rufewa ita ta soma jan hankalin su'ad din,idanu ta zuba mata baki daya,sannu a hankali wani kishi ya soma sokarta na ganin yadda sumayyan tayi kyau kamar 'yar tsana,kai kace drowing ne na girly,cikin da take tsammani zai batata sai gashi ya zame wani ado a jikinta,ya shiga wata na biyar ya zauna daras a jikinta abin sha'awa,ko daya bai tafi da hips da boobs da take da su ba saima qara fito da su da yayi,karon farko data soma ganinta cikin yanayin shigar,a hankali ta janye idanunta daga kanta kishi na nuqurqusarta,da ciki ma kenan ina ga tana ita kadai?,ta yiwa kanta wannan tambayar,da qyar ta iya hadiye yawu ta maida idanunta kan t.v taci gaba da kallo ba don tana fahimta ba,itakam dukkan abin nan da take batasan tana yi ba,kanta tsaye ta shige kitchen tana daga tsaye ta soma gyaran salad dinta.
Tunda ya shigo baki daya tayi gaba da dukkanin imaninsa,ruwa ya shigo sha amma baki daya ya nemi qishirwar ya rasa,sai kawai ya harde hannunshi a qirji ya jingina da qofa yana kallonta,baiso ma tasan ya shigo bare ya ta daina kaikawonta,ilahirin jikinta yake bi da kallo,wani sanyi da farinciki na saukar masa,godiya yakewa Allah cikin zuciyarsa,ba shakka duk yadda yaso ga son dai daita matsayinta cikin zuciyarshi da sauran mata yasan yayiwa kanshi qarya,abune ba mai yiwuwa ba,koda ciwon makanta da ciwon bacewar tunani zai kamashi yana da tabbacin zai iya gane randa yake ranar girkinta,tun daga harabar gidan da yake iya ajje motarsa kama da duk wani lungu da saqo na gidan sauyawa yake,ba'a magana qamshi tsafta da sauransu,sai yake jin kamar harda iskar gidan ma sauyata ake,babu mamaki ko don tsananin soyayyarta da kullum kwanan duniya ake linka masa ne?.
Sai data gama yankawa ta isa gaban famfo ta tara shi cikin ruwa,da hanzari taji an jawota,ko da daga bacci ta tashi tasan waye,mannata yayi da jikinsa ya zagaye hannayensa saman cikinta,sannan ya dora kanshi kan kafadarta
"Barka da dawowa....barka da dawowa sanyin idaniya hasken cikin gidansa....tun dazu naji yanayin gidan ya sauya ashe yariman maza ne ya iso" baisan sanda ta juyi da ita suna fuskantar juna ba,idanunta cikin nashi tana masa wani irin kallo,shi dinma kallon yake jifarta da shi,ya gaza cewa komai,ko yaushe furucinta na musamman ne a gurinsa,duk abinda zata furta ya isa kunnenshi mai dadi ne,mai laushi ne,mai taushi ne mau faranta zuciya tare da zare mata gajiya da baqinciki,kasa cewa komai yayi sai kallon kallo tsakaninsu tare da jifan juna da murmushi,bakinsu kawai ya hade waje daya yana aijata mata da wasu kisses masu zafin gaske,ganin yana neman wuce gona da iri a muhallin da bai dace ba ya sanyata tureshi suna maida numfashi,ya matsa din amma bai bar jikinta ba,dubanta yake da rikitattun idanunshi da suka sauya lokaci daya,cike da shauqi yake dubantan nata
"A kitchen muke fa" ta fada a shagwabe,hancinta ya kama ya dan jaa
"To waye ya jawo?,irin wannan shigar ko gaban wa na ganki hakan na iya faruwa" ya fada da qyar cikin muryarshi dara fara jirkicewa
"Bamu gaisa da baby ba" murmushi ta saki
"Wannan baby......wanne irin qauna ne haka my maan" kada kai kawai yayi yana murmushi,qugunta ya riqo baki daya da hannayenshi
"Qauna?,indai wannan ce qauna to kam bakiga komai ba,babu abinda kika gani babe....banajin zan iya bayyana qaunar da nake mishi ko mata,daga cikin dalilan da ya sanya kenan ban damu da duba me zaki haifa min ba,ko me kika haifamin ina so ina maraba da shi,gudan jin muhammad almustapha ne da summyn malam" murmushi ta saki sosai saboda sunan da ya kirata da shi har fararen haqoranta na bayyana,dubanta yake shima yana murmushi wani farinciki na shigarshi,da kanta ta yaye masa t.shirt din dake jikinta zuwa saman cikinta,ya durqusa a hankali hannunshi saman cikin.
wani wawan tsaki mai shiga kunnuwa suka ji anja,su'ad ce wadda tun shigowarshi cikin kitchen din ta kasa samun nutsuwa,baki dayan hankalinta ya karkata kitchen ne,ta kasa zama har sai data biyo bayansu,kusan duk rabin maganar tasu cikin kunne da idanunta suja yisu,wanda sam basu san da shigowar tata ba banda yanzun,ko kusa ko alama bata taba sanin cewa haka almustaphan ke qaunar haihuwa ba,tayi tsammanin cewa ra'ayinsu daya a qidarsu daya,saboda ganin ko alama bai taba mata magana kan rashin samun juna biyunta ba,abinda bata sani ba shine yana sawa rashi lokaci ne,idan yayi zata haifa masa,bugu da qari yana tausayim macen da bata haihu ba,hakan ya sanya yake ganin girma da qimar ni'imah har gobe
"Amma dai wannan abun bai dace ba ko?" Ta fada zuciyarta kamar zata fadi qasa,waiwayowa yayi yana dubanta
"Shigowa kai tsaye ba tare da yin sallama bane bai dace ba ko ko meye?" Kasa cewa komai tayi don tasan ita ta kawo kanta,ta sani cewa duk ranan girkinta hatta da zurga zurga sumayyan bata fiya ba,data gama uzurorinta ta masa sallama shikenan sai da safe,mazewa ta sake yi kishi na cinta
"Kitchen wajen kowa ne,na shigo daukar abu sai na fasa saboda ku?"
"Yaushe kika fara labe?,kina tsammamin banga shigowarki ba?,kina tsaye tsohon minti goma?" Mamaki ya cikata,bata yi zaton ya ganta ba,da shigowa daukan abu tayi niyyar fakewa tayi boren qarya,da idanu ya tsatstsareta yana hukuntata da kallonshi,wanda ta san fassarar hakan sarai,duk sai ta daburce,numfasawa yayi ya dauke kanshi daga gareta fuskanshi daure ya maida ga sumayya data soma wanke salad dinta
"Muje ki shiryan ruwa nayi wanka"amsa masa tayi da to,ta rufe salad dinta ta ajjiye gefe sannan ta ratsa ta fice,sai data fice daga kitchen din sannan ya maida kallonsa ga su'ad dake tsaye tana cije baki cikin takaici,a hankali ya tako zuwa gabanta,daf da ita ya tsaya tazarar dake tsakaninsu bata da yawa
"Me yasa ko yaushe baki daukan gyara?,baki gyaran kuskurenki cikin sauqi?,Kada kiyi abinda zai siya miki raini,ki guji yin abinda bai dace ba,abinda duk kikasan ba'a yi miki ki nisanci yiwa wani,umarni na baki ba shawara ba" baya ya danja sannan ya juya shima ya fice,yafi kowa sanin halinta,tafi gane tsauri,daukar sauqi take tamkar wata isa ce tata tasa ake mata hakan.
Dukkanin maganganunsa ba damunta sukayi ba a yanzu,abu daya tak ke mata yawo cikin kwanya da qwaqwalwa,so qauna kulawa da tsantsar soyayya da ta gani zalla a qwayar idanunshi yana nunawa ga ciki dama wadda ke dauke da cikin,me yake shirin faruwa ne?,shine tambayar da take wa kanta,a hankali qwaqwalwarta ta soma mata tariyar wasu shekaru can baya da suka shude,shekarun da a cikinsu ta fidda mahaifarta,a sanda anty kubra ke zabga mata fada,a lokacin da take gaya mata tayi kuskure,take gaya mata zata iya dana sani a gaba,take shaida mata matakin kama almustapha a hannu da kyau shine ta ajjiye masa iri,ta hada jini da irin gidan baban,shine zata samu dukkan abinda take so,zata zama tasu ta har abada,jinta take kawai a sannan,gani take labarin qanzon kurege ne kawai,tunda bata ga wani damuwa ko alamu tattare da da almustaphan ba,saidai a yanzu jikinta ya soma sanyi,wutar kishi ta soma nuna mata akwai wani abu dake shirin faruwa,tattalin da take gani wajenshi a kanta ya zarce soyayyar da yake mata ita daya face harda ta abinda ke cikinta,indai ko haka ne itace mafi cancanta data samu wannan launin soyayya da qauna mai ratsa gangar jiki da zuciya,saidai zata sanya ido taga shin abinda take hasashen haka ne?.
*gobe ina da uziri,idan kuka jini shiru saidai kuyi haquri,duk da zanso ace na muku,so nake mu kammala littafin nan kusa in sha Allah,na gode*
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
1⃣0⃣3⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*Allah S W T yana cewa*
*kuyi guzuri,amma mafi alkhairin guziri shine TSORON ALLAH*
___________________________________
Cikin nutsuwa da kwanciyar hankali take renin cikinta,wanda bata taba sanin hakan kwanciyar hankali ke da dadi ba yayin rainon ciki sai yanzu,bata da wata matsala yanzu gaba daya a kafatanin rayuwarta,kullum kwanan duniya farinciki ke sake riskar rayuwarta,tako wanne bangare rayuwa na mata kyau fiye da yadda take so,gefe guda ga mai gidanta mai share kukanta yana tare da ita ako da yaushe,ba abinda ta nema cikin rayuwarta ta rasa,ko da yaushe suna waya da dukkan 'yan gida,halima tuni cikinta ya tsufa dab take da haihuwa,abdallah har yau na wajensu ya dawo wajenta baki daya,ya zama tamkar danta,kai idan ba gaya maka akayi ba bazaka taba cewa basu suka haifeshi ba su da abdur rahman,zainab ma ta samu wani cikin bayan barin da tayi,amira ana can ana fama da laulayi wanda ya sanyata tayi laqwas,ashe da wasa farin garki,nafisa qawarta matar auwal itama ana can ana fama,ko yaushe suna waya tare da yiwa juna fatan sauka lafiya.
Sulaiman wato malam mahaifin sumayya tuni lamura sunyi nisa,ci gaba ake ci gaba da samu cikin gidajen gonakinsa,ya dauki ma'aikata sosai da zasu kula masa da gidajen gonar nashi dake gwambe kano da abuja,shike kula da na kano,na gwambe sun sake diban samarin dake cikin ainihin karkararsu,na abuja kuwa ya bar komai wajen baban tunda yafishin sanin ya yanayun garin yake,tuni malam din ya soma zama wani na musamman shima,gida ya gina musu yalwatacce wanda aka qawati shi da kayan alatu da more rayuwa,sashe biyu ne madaidaita hakan ya sanya yaya abubakar dauko meenat matarshi suka dawo daya sashen da yaransu guda uku,hakan ya yiwa mama dadi qwarai,don dama gidan ya zama sai ita kadai,gashi ya mata girman da bazata iya zama ita kadai din ha,amma dawowarsu amina da jikokin maman hakan sai yayi mata dai dai,zumuncin baba da malam din kuwa sai abinda yayi gaba,don basu cikakken wata basu ga juna ba,ko malam din yazo ko kuma baba yaje,da haka wani lokaci suke zuwa da matansu,wanda hakan ya haifar da sabo sosai tsakanin anty maamaa mama da kuma ummi.
Tunda ya shigo baki daya tayi gaba da dukkanin imaninsa,ruwa ya shigo sha amma baki daya ya nemi qishirwar ya rasa,sai kawai ya harde hannunshi a qirji ya jingina da qofa yana kallonta,baiso ma tasan ya shigo bare ya ta daina kaikawonta,ilahirin jikinta yake bi da kallo,wani sanyi da farinciki na saukar masa,godiya yakewa Allah cikin zuciyarsa,ba shakka duk yadda yaso ga son dai daita matsayinta cikin zuciyarshi da sauran mata yasan yayiwa kanshi qarya,abune ba mai yiwuwa ba,koda ciwon makanta da ciwon bacewar tunani zai kamashi yana da tabbacin zai iya gane randa yake ranar girkinta,tun daga harabar gidan da yake iya ajje motarsa kama da duk wani lungu da saqo na gidan sauyawa yake,ba'a magana qamshi tsafta da sauransu,sai yake jin kamar harda iskar gidan ma sauyata ake,babu mamaki ko don tsananin soyayyarta da kullum kwanan duniya ake linka masa ne?.
Sai data gama yankawa ta isa gaban famfo ta tara shi cikin ruwa,da hanzari taji an jawota,ko da daga bacci ta tashi tasan waye,mannata yayi da jikinsa ya zagaye hannayensa saman cikinta,sannan ya dora kanshi kan kafadarta
"Barka da dawowa....barka da dawowa sanyin idaniya hasken cikin gidansa....tun dazu naji yanayin gidan ya sauya ashe yariman maza ne ya iso" baisan sanda ta juyi da ita suna fuskantar juna ba,idanunta cikin nashi tana masa wani irin kallo,shi dinma kallon yake jifarta da shi,ya gaza cewa komai,ko yaushe furucinta na musamman ne a gurinsa,duk abinda zata furta ya isa kunnenshi mai dadi ne,mai laushi ne,mai taushi ne mau faranta zuciya tare da zare mata gajiya da baqinciki,kasa cewa komai yayi sai kallon kallo tsakaninsu tare da jifan juna da murmushi,bakinsu kawai ya hade waje daya yana aijata mata da wasu kisses masu zafin gaske,ganin yana neman wuce gona da iri a muhallin da bai dace ba ya sanyata tureshi suna maida numfashi,ya matsa din amma bai bar jikinta ba,dubanta yake da rikitattun idanunshi da suka sauya lokaci daya,cike da shauqi yake dubantan nata
"A kitchen muke fa" ta fada a shagwabe,hancinta ya kama ya dan jaa
"To waye ya jawo?,irin wannan shigar ko gaban wa na ganki hakan na iya faruwa" ya fada da qyar cikin muryarshi dara fara jirkicewa
"Bamu gaisa da baby ba" murmushi ta saki
"Wannan baby......wanne irin qauna ne haka my maan" kada kai kawai yayi yana murmushi,qugunta ya riqo baki daya da hannayenshi
"Qauna?,indai wannan ce qauna to kam bakiga komai ba,babu abinda kika gani babe....banajin zan iya bayyana qaunar da nake mishi ko mata,daga cikin dalilan da ya sanya kenan ban damu da duba me zaki haifa min ba,ko me kika haifamin ina so ina maraba da shi,gudan jin muhammad almustapha ne da summyn malam" murmushi ta saki sosai saboda sunan da ya kirata da shi har fararen haqoranta na bayyana,dubanta yake shima yana murmushi wani farinciki na shigarshi,da kanta ta yaye masa t.shirt din dake jikinta zuwa saman cikinta,ya durqusa a hankali hannunshi saman cikin.
wani wawan tsaki mai shiga kunnuwa suka ji anja,su'ad ce wadda tun shigowarshi cikin kitchen din ta kasa samun nutsuwa,baki dayan hankalinta ya karkata kitchen ne,ta kasa zama har sai data biyo bayansu,kusan duk rabin maganar tasu cikin kunne da idanunta suja yisu,wanda sam basu san da shigowar tata ba banda yanzun,ko kusa ko alama bata taba sanin cewa haka almustaphan ke qaunar haihuwa ba,tayi tsammanin cewa ra'ayinsu daya a qidarsu daya,saboda ganin ko alama bai taba mata magana kan rashin samun juna biyunta ba,abinda bata sani ba shine yana sawa rashi lokaci ne,idan yayi zata haifa masa,bugu da qari yana tausayim macen da bata haihu ba,hakan ya sanya yake ganin girma da qimar ni'imah har gobe
"Amma dai wannan abun bai dace ba ko?" Ta fada zuciyarta kamar zata fadi qasa,waiwayowa yayi yana dubanta
"Shigowa kai tsaye ba tare da yin sallama bane bai dace ba ko ko meye?" Kasa cewa komai tayi don tasan ita ta kawo kanta,ta sani cewa duk ranan girkinta hatta da zurga zurga sumayyan bata fiya ba,data gama uzurorinta ta masa sallama shikenan sai da safe,mazewa ta sake yi kishi na cinta
"Kitchen wajen kowa ne,na shigo daukar abu sai na fasa saboda ku?"
"Yaushe kika fara labe?,kina tsammamin banga shigowarki ba?,kina tsaye tsohon minti goma?" Mamaki ya cikata,bata yi zaton ya ganta ba,da shigowa daukan abu tayi niyyar fakewa tayi boren qarya,da idanu ya tsatstsareta yana hukuntata da kallonshi,wanda ta san fassarar hakan sarai,duk sai ta daburce,numfasawa yayi ya dauke kanshi daga gareta fuskanshi daure ya maida ga sumayya data soma wanke salad dinta
"Muje ki shiryan ruwa nayi wanka"amsa masa tayi da to,ta rufe salad dinta ta ajjiye gefe sannan ta ratsa ta fice,sai data fice daga kitchen din sannan ya maida kallonsa ga su'ad dake tsaye tana cije baki cikin takaici,a hankali ya tako zuwa gabanta,daf da ita ya tsaya tazarar dake tsakaninsu bata da yawa
"Me yasa ko yaushe baki daukan gyara?,baki gyaran kuskurenki cikin sauqi?,Kada kiyi abinda zai siya miki raini,ki guji yin abinda bai dace ba,abinda duk kikasan ba'a yi miki ki nisanci yiwa wani,umarni na baki ba shawara ba" baya ya danja sannan ya juya shima ya fice,yafi kowa sanin halinta,tafi gane tsauri,daukar sauqi take tamkar wata isa ce tata tasa ake mata hakan.
Dukkanin maganganunsa ba damunta sukayi ba a yanzu,abu daya tak ke mata yawo cikin kwanya da qwaqwalwa,so qauna kulawa da tsantsar soyayya da ta gani zalla a qwayar idanunshi yana nunawa ga ciki dama wadda ke dauke da cikin,me yake shirin faruwa ne?,shine tambayar da take wa kanta,a hankali qwaqwalwarta ta soma mata tariyar wasu shekaru can baya da suka shude,shekarun da a cikinsu ta fidda mahaifarta,a sanda anty kubra ke zabga mata fada,a lokacin da take gaya mata tayi kuskure,take gaya mata zata iya dana sani a gaba,take shaida mata matakin kama almustapha a hannu da kyau shine ta ajjiye masa iri,ta hada jini da irin gidan baban,shine zata samu dukkan abinda take so,zata zama tasu ta har abada,jinta take kawai a sannan,gani take labarin qanzon kurege ne kawai,tunda bata ga wani damuwa ko alamu tattare da da almustaphan ba,saidai a yanzu jikinta ya soma sanyi,wutar kishi ta soma nuna mata akwai wani abu dake shirin faruwa,tattalin da take gani wajenshi a kanta ya zarce soyayyar da yake mata ita daya face harda ta abinda ke cikinta,indai ko haka ne itace mafi cancanta data samu wannan launin soyayya da qauna mai ratsa gangar jiki da zuciya,saidai zata sanya ido taga shin abinda take hasashen haka ne?.
*gobe ina da uziri,idan kuka jini shiru saidai kuyi haquri,duk da zanso ace na muku,so nake mu kammala littafin nan kusa in sha Allah,na gode*
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
1⃣0⃣3⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*Allah S W T yana cewa*
*kuyi guzuri,amma mafi alkhairin guziri shine TSORON ALLAH*
___________________________________
Cikin nutsuwa da kwanciyar hankali take renin cikinta,wanda bata taba sanin hakan kwanciyar hankali ke da dadi ba yayin rainon ciki sai yanzu,bata da wata matsala yanzu gaba daya a kafatanin rayuwarta,kullum kwanan duniya farinciki ke sake riskar rayuwarta,tako wanne bangare rayuwa na mata kyau fiye da yadda take so,gefe guda ga mai gidanta mai share kukanta yana tare da ita ako da yaushe,ba abinda ta nema cikin rayuwarta ta rasa,ko da yaushe suna waya da dukkan 'yan gida,halima tuni cikinta ya tsufa dab take da haihuwa,abdallah har yau na wajensu ya dawo wajenta baki daya,ya zama tamkar danta,kai idan ba gaya maka akayi ba bazaka taba cewa basu suka haifeshi ba su da abdur rahman,zainab ma ta samu wani cikin bayan barin da tayi,amira ana can ana fama da laulayi wanda ya sanyata tayi laqwas,ashe da wasa farin garki,nafisa qawarta matar auwal itama ana can ana fama,ko yaushe suna waya tare da yiwa juna fatan sauka lafiya.
Sulaiman wato malam mahaifin sumayya tuni lamura sunyi nisa,ci gaba ake ci gaba da samu cikin gidajen gonakinsa,ya dauki ma'aikata sosai da zasu kula masa da gidajen gonar nashi dake gwambe kano da abuja,shike kula da na kano,na gwambe sun sake diban samarin dake cikin ainihin karkararsu,na abuja kuwa ya bar komai wajen baban tunda yafishin sanin ya yanayun garin yake,tuni malam din ya soma zama wani na musamman shima,gida ya gina musu yalwatacce wanda aka qawati shi da kayan alatu da more rayuwa,sashe biyu ne madaidaita hakan ya sanya yaya abubakar dauko meenat matarshi suka dawo daya sashen da yaransu guda uku,hakan ya yiwa mama dadi qwarai,don dama gidan ya zama sai ita kadai,gashi ya mata girman da bazata iya zama ita kadai din ha,amma dawowarsu amina da jikokin maman hakan sai yayi mata dai dai,zumuncin baba da malam din kuwa sai abinda yayi gaba,don basu cikakken wata basu ga juna ba,ko malam din yazo ko kuma baba yaje,da haka wani lokaci suke zuwa da matansu,wanda hakan ya haifar da sabo sosai tsakanin anty maamaa mama da kuma ummi.