← Book details Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 124 OF 226

Sashe 124

Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Daf da zasu shiga bangaren wanda ta baya suka biyo da yake qofofi biyu garesu,akwai qofar gaba wanda zaka shiga ta falo,akwai qofar baya wanda zaka shiga ta kutchen wannan qofar suka biyo,daga hannun hagu na bakin qofar,a qawace yake da wasu irin nau'in furanni da shukoki masu kaloli daban daban da kuma kyau,baki dayansu kansu daya babu wadda tafi wani tsaho,an qawata gun tamkar wani dan gurin hutawa,kaf gidan nan dinne kadai ke da irin wadan nan shukokin,wanda qilan mamallakin bangaren ne ya siyi abunshi yasa aka tsara masa su a haka,yara ne kusan su hudu,maza biyu mata biyu,a qiyasce zasuyi sa'annin juna baki dayansu,kowanne qananun kaya ne a jikinsa,sun kunna fanfunan suna ta faman wasan ruwa,amira ita ta fara hangosu,sai ta dakata tana daga murya
"Hibba!!,yayi muku kyau da wasan ruwa kunji ko" baki daya suka waiwayo suna dubanta,kyawawan yara ne wanda kallo daya zaka yi musu ka tabbatar jinin gidan baabaa prof ne,wadda aka kira da hibba ita ta matso
"Anty amira,gasar yin alwala muke,su hibban duk basu iya ba,zo kiga na fisu iyawa"
"Matsa ki ban gu,yanzu ban da lokacin shirmenku kinji,tawa ta isheni" sai ta karyar da kai fuskarta kamar mai shirin yin kuka tace
"Don Allah anty amira kizo ki gani" idanunta ta zaro tana dubanta
"Ina wasa dake ne,bakiga ina cikin hidima ba,matsa a wajen nace" sumayya na tsaye tana murmushi tana dubansu,yarinyar ta burgeta,zuciyar son yaranta ta motsa mata,dauke idonta yarinyar tayi daga duban amira ta maida kan sumayya
"Tunda ba zaki ba ai ga wata antyn ko?anty zaki je ki gani?"
"Me zai hana" sumayya ta fada tana murmushi,tsalle ta fara wanda hakan ya sanya sauran yaran qarasowa din jin me ya faru
"Ba inda zata,Allah hibba kin baci da yawa,itama tana da abunyi"
"A'ah,nifa sai naje" inji sumayya wadda dama hanyar kubuta take nema
"Kije ki fito kya sameni a nan" ta fada tana yin gaba din tuni yarinyar ta riqe mata hannu
"Anty muje waccan fanfon,wannan na uncle man ne,zai zanemu ya ganmu a gurin,amma idan mukayi kuka sai ya bamu chaculet yace mu daina" murmushi tayi kawai tace
"Allah"
"Allah anty,kuma duk yafi sona" hibba ta fada suna qarasowa wani waje wanda shima akwai fanfo saidai baikai wancan kyau ba.

Jin muryar yara ya sanyashi daga idanunshi daga kan laptop din dake gabanshi yana duba wasu sababbin design na dogayen riguna da kamfaninsa ke son fitarwa a sabuwar shekara,gefanshi butar shayi ce da cup qwaya daya,a rayuwarshi yana son ababen nan,yanayi na damuna irin wannan bayan gama saukar ruwan sama,da guri wanda ke da wadatar korayen tsirrai,iskar wajen mai dan sanyi sanyi kadan hade da qamshin qasa da qamshin furanni na masa dadi qwarai,ganin yaran tare da wata ya sanyashi maida kanshi yaci gaba da abinda yake.

Daya yaron ne ya tabe fuska yana cewa
"Qarya ne anty,yafi sona,ko za'a tambaya ma" yatsanta ta dora kan lebenta tana zaro masu idanu alamun yayi abunda ba mai kyau ba
"Bakasan ba'a cewa babba qarya yake ba,lala ba kyau,kace Allah na tuba" kan kunnensa kalaman suka sauka sai ya daga kai ya sake duban inda suke tsaye,har yanzu bai gane wace ba,amma yana iya gane yaran saboda baki daya yasan muryoyinsu,hannunshi ya sanya ya tsiyayi shayin ya kai bakinsa yana ci gaba da sauraronsu,a rayuwa Allah ya zuba masa qaunar yara,zama cikinsu yana debe kewanshi a duk sanda ya samu kansa cikin kewa,hakan ya sanya wani lokaci yakan bata lokaci cikin gidan marayunshi,akwai yaran da suka shiga ransa da dama a gidan,baisan so yaushe ne zai daina rayuwar kadaici ba.

Murmushi tayi ganin yaron yayi saurin rufe bakinsa yana cewa
"Allah na tuba"
"To yanzu muje mu gwada inga alwalar kowa din,duk wanda yafi iyawa shi ya m....." Sai ta kasa qarasa sunan
"Wanda duk yafi iyawa shi aka fi so" ta sauya salon maganar tata,tsalle suke har suka isa gaban fanfon,tana tsaye tana kallon kowa daya bayan hannayenta harde a qirjinta,kamar yadda yake zaune saman kujera yan kurbar tea mai zafi yana kallonsu,sai da suka kammala tsaf,tabbas hibba ta fisu iyawa,amma ita dinma akwai gyare gyare,a hankali ta yaye yalwataccen mayafin data suturce jikinta da shu,wanda hakan ya bayyana shape dinta sosai kasancewar riga da skert ne a jikinta,tun bayan zuwanta abuja kayan suka dan kamata kasancewar ta murje ta cicciko,idanuwanshi ya lumshe saboda gujewa kallin haramun dinshi,sai ya kasa sake bude idanuwan mashi ya barsu a lumshe yana sauraron ta tana fadin
"Sai kuyu haka,yauwa haka,haka" bai bude ba har sai da yaji tana fadin
"Idan kayi haka,kayi alwala mai kyau" a hankali ya bude idanuwan nashi,wannan karon fuskarta tarwai take ta haske qwan lantarkin da ta tsaya saitinsa,ya dan qura mata idanuwa yana son tuna inda yasan fuskar
"Mai kuka a uk mall" qwaqwalwarsa ta birkito file dinta,qaramin murmushi ne ya subuce masa,wanda idan baka kula da kyau ba na zaka gane hakan ba,saboda cije leban qasan bakinsa da yayi
"Tana acting kamar wata babba" ya raya hakan a ransa.

Riqeta yaran suka sake yi,nurain daya daga cikin yaran yace
"Anty ki mana tatsuniya,baabaa lami mai aikin momi tana mana" murmushi ta saki,ta lura suma lallai yaran masu son mutane da sabo ne,saidai suna son riqeta gashi tana son tafiya gida ne
"Ban iya tatsuniya ba saidai na baki tarihi"
"Laaaah,irin wanda uncle man ya taba yi mana rannana?" Zaitun daya yarinyar ta ambata da salon tambaya,duk da bata sani ba amma sai ta daga kai
"Ita,amma yanzun inaso naje gida na gaida anty na,sai wani lokacin na muku ko?"
"Yaushe?" Inji hibban,kai ta girgiza qaramar dariya na son subuce mata,yaaraan akwai wayo,tana som tana yaro mai wayo da kaifin qwaqwalwa irin haka,ta tabbatar basirar da wayon bai tashi a banza,zai zama abu ne mai amfani a nan gaba
"Wataran in sha Allah".

A hankali ya janye idanuwanshi daga kansu jin qarar wayarshi,ya cirota daga aljihun black trouser din dake jikinsa yana duba mau kiran,su'ad ce,dan qaramin tsaki yaja,ba matsala yake so ta qara maishi ba,ya riga da ya yanke magana,ya gaji da auren asha ruwan tsuntsaye da sukeyi,ita tana kano shi yana daura,kusan tun jiya bayan isowarshi garin da yaje gidan hamza abun ke dawainiya da shi,kasancewar wanda amiran zata aura cousin suke da hamza,wata rayuwa ya gani ba irin tasu rayuwar ba,ba irin rayuwar gidanshi ba,yana iya tuna sanda hamza ya dagewa auren yarinyar suna ganin baikensa,ashe akwai abinda ya gano?.

Rejecting call din nayi sannan ya maida kansa kan laptop dinshi da niyyar ci gaba da aikin da yakeyi,wani tsakin ya kuma ja ganin lokacin da ya bata yana kallon sha'anin da bai shafe shi ba,yayi asaran time dinsa a banza,saidai yadda take kiranshi a jejjere ya hanashi aiwatar da komai,wani wawan tsakin ya sake ja,a rayuwarshi ya tsani abinda zai takurashi,sai ya ciro wayar a fusace ya daga ya kara a kunnenshi,cikin shagwaba da karyar da murya ta soma fadin
"haba my man,please....please kada muyi haka da kai,ka duba fa ka gani duka duka shekara daya ya rage min na kasance tare da kai fa?"
"Keep quite su'adah please....na riga da na gama magana,idan zaki iya zama gu daya fine,idan ma ba zaki iya zama ba duk daya,amma kada ki zargeni nan gaba" ta tabbatar da cewa shi din kaifi daya ne,baha magana ya sauyata,mutum biyu ne tal a duniya ke sauya masa ra'ayi koda baiyi daidai da mizanin mashi ra'ayin ba,baabaa prof sai ummee,sanin baya qaunar kuka ko misqala zarratin,koda na qaramin yaro ne ya sanyata saka kuka har da sheshsheqa,sai ya lumshe idanuwansa yana sauraren sautin kukan nata,a hankali ya zame wayar daga kunnenshi sannan ya kasheta baki daya ya cillata aljihu,shutting down din system din yayi sannan ya miqe tsaye yana jira ta qarasa mutuwa,ya laluba aljihunsa yaji muqullansa na jiki,ya dauke system din sannan ya dinga takawa a hankali ya nufi inda yayi niyya,baki daya baya marmarin komawa bangaren bare taci gaba da jagula masa lissafi,saboda haka ya isa ga qarama cikin motocinsa ya bude ya ajjiye kayanshi ciki ya tada ta ya fice ba tare da ya nemi kowa ba.

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:51] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖

*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)

7⃣0⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*

*HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKIL*
___________________________________

Mamaki ya kama anty dije ganin sumayya,dariya ta dinga yi tana cewa
"Maganinki,da kika qi dawowa ga mai gaba daya nan taje ta taho mana da ke ai" itama sumayya dariya take
"Hmmm,amira,amira rigima amira tabara,sai ganinta kawai nayi wallahi"
"Ina sane ban gaya miki ba ai" guri sumayyan ta samu ta zauna tana ci gaba da dariya.

Nan ta shantake suna ta hira da anty dijen,bata tashi farga ba sai taga har sha daya tayi,hakan ya sanya ta bude dakinta tayi kwanciyarta,anty dije je cewa
"Abdallah fa?"
"Barshi anty,babu lallai yayi rigima"

****** ****** *******

Qarfe goma na safe tayi wanka bayan ta gama hada breakfast ta barwa anty dije sauran aikin gidan,doguwar riga ta saka ta wani irin yadi mai talewa,hijabi ta zura wanda ya saukar mata har saman tafin qafarta,niqabinta ta daura sannan ta fita ta tadda anty dije na goge kayan kallo a falo
"Anty zan wuce,nasan amira tana can ta cika fam,fashewa kawai take jira tayi" ta fada tana qyalqyalewa da dariya,dariyar itama tayi
"Ato,yau mai rabaku sai Allah" tana dariya ta saki niqab din nata ta fice a gidan.

Ya kusan a qalla mintuna talatin zaune cikin corridor din dake saman benanshi,bata san sanda ya shigo ba,tun daren jiyan taje zaman jiran shigowarshi taji shiru,ta kira wayar babu adadi saidai duka amsa daya ce wayar a akashe take,tun tana kumbura har zuciyarta ta fara saukowa,ta sani cewa fushinsa bashi da dadi,tana shan wuya a duk lokacin da yayi fushi,hakan ya soma daga hankalinta,kusan ranar bata yi cikakken bacci ba,saidai duk da haka bata san shigowarshi cikin gidan ba.

Cikin qanqanin lokaci zuciyarsa tayi fes,fuskarsa ta soma washewa,yaran dake shawagi kan idanunshi a harabar gidan,yaro daya tak yake hangowa cikinsu wanda bai sanshi ba baquwar fuska ne,saidai a yadda wasan da yaran ke gudana duka ya fisu kuzari da wayo,motsin yaron ya dinga bi da kallo yana sakin murmushin gefan baki.
Chapter 124 · 0% Book details