Sashe 57
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tunda ta farka daga suman da tayi take qaraji tana kuka,sai data tada hankalim duk marasa lafiyan dake dakin,babu yadda zinatu batayi kan ta lallabata ba amma taqi yin shiru,duk yadda take jin dadin halin da taga zainab din a ciki amma ji take kamar ta zura da gudu,dadi take ji sosai da wannan labarin na samuwar cutar qanjamau jikin zainab din,ganin yadda zainab din ke firgita musu marasa lafiya ya sanya suka canza mata daki.
Kusan kwana tayi a haka kafin daga baya ta fara sassauta qugin da takeyi saboda ta fara jin sassaucin radadin da take ji a zuciyarta.
Tana jingine a bango har zinatu ta gama bata shayin,saidai har a lokacin bata ce komai ba sai faman jinjina kai da take,kanta ta daga ta kalli zinatu da jajayen idanuwanta kamar na maza murya a kausashe tace
" kin gayawa wani a gidan mu abinda ke faruwa ne"kai ta kada tana ajjiye kofin hannunta
"A'ah,babu wanda na gayawa"
"To bana buqatar kowa ya sani"
"To" kawai zinatun ta fada tana dariyar mugunta cikin zuciyarta.
"Cutar qanjamau zinatu" tayi furucin tana kallon zinatu tamkar mai neman tabbaci kan wata magana,cikin fuskar tausayin qarya tace
"Don Allah ki bar daga hankalinki zainab,mutum nawa ne masu irin cuwin ke rayuwarsu hankali kwance"
"Dalla can malama daqiqiya kawai,bani da dama kenan ta komawa mukhtar ko kin manta?" Shiru zinatu tayi zagin da tayi mata yana mata ciwo amma ba zata iya maidawa ba
"Zinatu,hakan fa yana nufin mutuwata gab take da ni kenan"
Kallonta kawai zinatun tayi ba tare da tace komai ba,kamar zararriya sai ta miqe tsaye tana girgiza kai
"Inaaa,wallahi bazai yiwu ba,wallahil azim bazan mutu ni kadai ba,kai ka zama silar kasancewata cikin wannan hali,kaine sila,kai ka jawo min" ta fada tana zarya cikin dakin,mayafinta ta figa ta yafa tana fadin
"Ki nemo kudinsu ki biyasu ki sameni a gida zamu warware" tayi maganar tana ficewa daga asibitin.
*tofa,muje zuwa masu karatu*
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣7⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
_____________________________
*wa may ya'amal misqala zarratin khairan yarah,wa may ya'amal misqala zarratin sharran yarah*
*_duk wanda ya aikata dai dai qwayar zarra na alkahiri zai gani,duk wanda kuma ya aikata dai dai da qwayar zarra na sharri zai gani_*
_______________________________
*Gaisuwa da fatan alkhairi gareku*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽
*sis farida muhammad abbas*
*sis rabi'ah haroun*
*sis dada*
*Bilkisu mai gadon zinare*
*mrs alqali*
*maman sayyid*
Bayan sallar isha'i ne,idarwarta kenan abdallah ya soma rigima tilas ta kwantar da shi gefanta ta soma lallabashi,don kwanakin abinda ya koya kenan rigima idan zaiyi bacci,ya Abbakar ne dake shirin wucewa gidansa ya leqo
"Kinyi baqo sumayya"
"Baqo?,baqo kuma ya abbakar?" Ta tambaya cikin mamaki da faduwar gaba,waye yake son jawo mata jarfa tana zamanta lafiyar Allah
"Eh baqo,kiyi ki fito kada ki zauna" ya fada cikin halin ko in kula da yanayinta yana sakin labulen ya fice,magabar tayita juyawa cikin ranta,sai ta banzatar da zancan jin yaya abbakar din na yiwa mama sai da safe ya wuce gidansa.
Minti kusan goma da fitar tasa mama ta dago labulen ta shigo
"Wai ba yayanki ya fada miki kina da baqo ba" kamar zata saki kuka ta dubeta
"Mama ban fa san ko waye ba"
"Idan kinje kya ga ko waye din yana sitting room din malam,tashi maza ki wuce kuma saura kije ki yiwa mutane sakarci",tilas ta miqe bayan ta kwantar da abdallah a kan gado ko hijabin jikinta bata cire ba ta fito zuciyarta fal quna.
Turus tayi bakin qofar ragowar sallamarta ta koma ciki,da hanzari ta juya tana mai neman fita,cikin zafin nama ya sha gabanta wanda saura kadan jikinsu ya hadu,sai ta ja baya tana dubansa,mukhtar ne sanye da dinkim shadda ruwan sararin samaniya babu hula kansa,ta masa kyau sosai saidai ramar da yayi ta bayyana,hancinta ya cika da qamshin turarensa ya dinga tuna mata baya,saboda haka da sauri tace
" matsamin na wuce"
"Babu inda zakije sumayya yau sai kince wani abu game da ni,kin yafe min ko baki yafemin ba,sumayya ya ina kike so na dora raina?,laifi ne na aikatashi na nemi afuwarki sumayya amma kinqi kice komai,kinsan kullum ya nake kwana ya nake tashi da rashin cewa komanki?,kinsan me nakeji cikin qirji na" sai kuma ya sassauta murya cikin sanyi
"Kinfi kowa sanin wane mukhtar sumayya,kinfi kowa sanin wane irin zama mukayi a baya,sumayya ki tausaya min koda ba zaki tausayamin ba ki tausayawa abdallah,abdallah ya zama marayan qarfi da yaji,abdallah na buqatar mu ni da ke a tare,idan baki tausayawa mana ba sumayya waye zaiji tausayinmu duk duniya?,taba qirjina sumayya kiji" ya fada yana fincikar hannunta zuwa qirjinsa,sosai taji zuciyarsa na bugawa,gaza cire hannunta tayi sai da taji ya ambaci wash,da sauri ta dubeshi sai taga yana dafe da kansa yana layi,batasan sanda ta riqeshi ba a rude tana cewa lafiya?,ganin yana neman gun zama ya sanya ta zaunar da shi tana masa sannu,tsahon mintina biyar sannan ya sauke numfashi ya gyara zamansa tana zaune can nesa da shi ya dubeta
"Ciwon kai nake fama da shi,amma wannan duka ba damuwata bace burina kawai ki yafemin" ya fada yana duban qwayar idanunta,a hankali ta janye idanuwanta zuciyarta na mata bitar waye mukhtar agurinta,
"Na yafe maka" ta furta murya can qasa
"Allah ya yafe mana baki daya" wani wawar ajiyar zuciya ya saki,baki daya jikinsa ya saki,wani farinciki yaji yana ratsa kowacce gaba ta jikinsa,yana so yaje ga sumayyan amma sam jikinsa babu qwari ko kadan,sai ya miqa mata hannu
"Taso sumayya kizo kusa da ni don Allah" sai ta girgiza kai ba tare data motsa ba,tilas ya tattaro duk wani ragowar qarfinsa ya kiqe ya isa gareta,kusa da ita ya zauna har tana gogar kafadarta,hakan ne ya sanyata ta janye da sauri tana hada rai
"Meye haka,don nace na yafe maka ai hakan ba yana nufin kai mijina bane ko zan sakw aurenka ba" da sauri ya sake matsawa kusa da ita babu gun matsawa a gunta don ya kaita qarshen kujerar sai ya kama hannunta ya matse cikin nashi
"Sumayya,na sake miki wani laifin don na bada sadakinki,amma bisa sharadin matsawar baki amince ba zan karbi kaya na na haqura"
Wani abu taji yana ratsa zuciyarta mai kama da farinciki,zuciyarta ta karye hawaye ya biyo kuncinta,cikin raunanniyar murya ta kwabe fuskarta
"Ni nace maka ka kai sadakina ba tare da sani na ba?,ai kuwa sai kaje ka karbi abinka don ni ban amince ba,kuma......" Bata ankara ba ya hade bakinsu waje daya wanda hakan yayi sanadiyyar katsewar maganarta,sun dauki kusan minti goma a haka sannan ya janye yana dubanta,qasa tayi da kanta kan fuskarta qaramin murmushi na fita a fuskarta
"Magana ta qare,na sanki tun ba yau ba,dukkan abinda zaki fada a yanzun nasan aji ne kawai za'a jamin ko ba haka ba" sake hade fuska tayi kamar gaske
"Nidai na fada kaje ka karbi sadakinka,bana yi"
"Ok to bari na kira ya abbakar na sanar masa" ya fada yana fiddo wayarsa daga aljihun gaban rigarsa,ganin da gaske lambar ya abbakar yake nemowa ya sanyata qwace wayar
"A'ah,ki bani mana na isar mishi da saqonki"
"Ni bance ba" ta fada a shagwabe,sai yayi jagale yana kallonta saboda tuna masa da baya da tayi ta salon yanayin maganar da tayi
"Kada ki hanani fa tafiya gida yau na kwana a nan"
"Bismillah mana ai ga guri nan" sai yayi kalar tausayi yana dubanta
"Yaushe za'a tara shaidu sumayya ki koma dakinki" idanu ta juya ta dan murguda baki
"Sai shekara iwar haka" qirjinsa ya dafe yana kallonta
"Mutuwa kike so nayi kafin lokacin sannan ko?" Rai ta hade
"Ka daina fadin haka mana ya mukhtar,ni kunya nake ji gaskiya ka bari idan ja shirya zan fada maka ka sanarwa ya abbakar" hannunta wanda ke cikin nashi ya sumbata yana fadin
"Na gode,na gode,na gode sumayya,na gode da karamcin da kika nuna min a rayuwa,na gode da kika nuna ke mai qaunata ce har yanzu" sai ya dakata yana fidda zoben azurfan dake yatsansa ya zura a nata,ya mata yawa hakan ya basu dariya baki dayansu,sai ya cire ya sanya mata a yatsan tsakiya duk da haka ya mata yawa
"Ina son zoben nan sumayy,amma sai naga yafi kyau a hannunki,ki ajiyemin zan karba"
"Idan kuma naji dadinsa bazan maida maka ba"
Dariya ya danyi sannan yace
"Babu komai,ai da kai da kaya duka mallakar wuya ne" sallamar halima ta sanya sumayya miqewa,shigowa tayi dauke da abdallah tana fadin
"Wallahi yaron nan ya koyi rigima,tunda ya tashi yaje zunduma ihu nayi tsammani ma kin jiyo shi"
"Ina zata jiyoshi ta shiga kogin qauna" mukhtar ya fada cikin salon zolaya yana miqa hannu ya amshi abdallah dake ta dokin zuwa gunsa yana kiran abba na,murmushi halima tayi tana yiwa sumayya kallon tsokana ta fice,ita kanta wani dadi taji don babu wanda yaji dadin rabuwarta da mukhtar,qafarta har qaiqayi take taje ta bawa zainab labari.
'Yar kallo sumayya ta koma sanda mukhtar suka soma wasa da abdallah,bata taba ganin d'a da uba irin haka ba,sai wajen qarfe goma ya fito zai tafi,qin tafiya yayi har sai data masa rakiya bakin mota,har ya shiga ya fito ya sake kallonta
"Ban son tafiya sumayya,banqi ace tare da ke zan tafi ba,don Allah ki taimaka ki gama shirye shiryen da duk zaki da wuri,ni na amince ma duk abinda baki qarasa ba ki qarasa shi a gida na zan baki wannan damar,ji nake kamar lokaci na qure mana" murmushi tayi tana jin maganar tasa na sauka sosai cikin zuciyarta
"Kada ka damu ya mukhtar,ka qarasa gida dare yanayi" ta fada tana taka masa,sai da yaja motar ya bar layin sannan ta koma cikin gida.
******* ******* ******
Cikin abinda bai gaza sati biyu ba mukhtar ya sabunta soyayyarsa baki daya,kullum yana tare da ita idan baizo ba kuwa ranar katin waya zaici ubanshi,har tsokanarta su halima sukeyi,wai sai kace wasu masu auren fari,ya dawo mata ya mukhtar dinta sak,sai ta samu kanta da dokanta wajen ganin ta a gidanta cikin sabuwar rayuwa ita da mukhtar dinta da yaronta.
Kusan kwana tayi a haka kafin daga baya ta fara sassauta qugin da takeyi saboda ta fara jin sassaucin radadin da take ji a zuciyarta.
Tana jingine a bango har zinatu ta gama bata shayin,saidai har a lokacin bata ce komai ba sai faman jinjina kai da take,kanta ta daga ta kalli zinatu da jajayen idanuwanta kamar na maza murya a kausashe tace
" kin gayawa wani a gidan mu abinda ke faruwa ne"kai ta kada tana ajjiye kofin hannunta
"A'ah,babu wanda na gayawa"
"To bana buqatar kowa ya sani"
"To" kawai zinatun ta fada tana dariyar mugunta cikin zuciyarta.
"Cutar qanjamau zinatu" tayi furucin tana kallon zinatu tamkar mai neman tabbaci kan wata magana,cikin fuskar tausayin qarya tace
"Don Allah ki bar daga hankalinki zainab,mutum nawa ne masu irin cuwin ke rayuwarsu hankali kwance"
"Dalla can malama daqiqiya kawai,bani da dama kenan ta komawa mukhtar ko kin manta?" Shiru zinatu tayi zagin da tayi mata yana mata ciwo amma ba zata iya maidawa ba
"Zinatu,hakan fa yana nufin mutuwata gab take da ni kenan"
Kallonta kawai zinatun tayi ba tare da tace komai ba,kamar zararriya sai ta miqe tsaye tana girgiza kai
"Inaaa,wallahi bazai yiwu ba,wallahil azim bazan mutu ni kadai ba,kai ka zama silar kasancewata cikin wannan hali,kaine sila,kai ka jawo min" ta fada tana zarya cikin dakin,mayafinta ta figa ta yafa tana fadin
"Ki nemo kudinsu ki biyasu ki sameni a gida zamu warware" tayi maganar tana ficewa daga asibitin.
*tofa,muje zuwa masu karatu*
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣7⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
_____________________________
*wa may ya'amal misqala zarratin khairan yarah,wa may ya'amal misqala zarratin sharran yarah*
*_duk wanda ya aikata dai dai qwayar zarra na alkahiri zai gani,duk wanda kuma ya aikata dai dai da qwayar zarra na sharri zai gani_*
_______________________________
*Gaisuwa da fatan alkhairi gareku*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽
*sis farida muhammad abbas*
*sis rabi'ah haroun*
*sis dada*
*Bilkisu mai gadon zinare*
*mrs alqali*
*maman sayyid*
Bayan sallar isha'i ne,idarwarta kenan abdallah ya soma rigima tilas ta kwantar da shi gefanta ta soma lallabashi,don kwanakin abinda ya koya kenan rigima idan zaiyi bacci,ya Abbakar ne dake shirin wucewa gidansa ya leqo
"Kinyi baqo sumayya"
"Baqo?,baqo kuma ya abbakar?" Ta tambaya cikin mamaki da faduwar gaba,waye yake son jawo mata jarfa tana zamanta lafiyar Allah
"Eh baqo,kiyi ki fito kada ki zauna" ya fada cikin halin ko in kula da yanayinta yana sakin labulen ya fice,magabar tayita juyawa cikin ranta,sai ta banzatar da zancan jin yaya abbakar din na yiwa mama sai da safe ya wuce gidansa.
Minti kusan goma da fitar tasa mama ta dago labulen ta shigo
"Wai ba yayanki ya fada miki kina da baqo ba" kamar zata saki kuka ta dubeta
"Mama ban fa san ko waye ba"
"Idan kinje kya ga ko waye din yana sitting room din malam,tashi maza ki wuce kuma saura kije ki yiwa mutane sakarci",tilas ta miqe bayan ta kwantar da abdallah a kan gado ko hijabin jikinta bata cire ba ta fito zuciyarta fal quna.
Turus tayi bakin qofar ragowar sallamarta ta koma ciki,da hanzari ta juya tana mai neman fita,cikin zafin nama ya sha gabanta wanda saura kadan jikinsu ya hadu,sai ta ja baya tana dubansa,mukhtar ne sanye da dinkim shadda ruwan sararin samaniya babu hula kansa,ta masa kyau sosai saidai ramar da yayi ta bayyana,hancinta ya cika da qamshin turarensa ya dinga tuna mata baya,saboda haka da sauri tace
" matsamin na wuce"
"Babu inda zakije sumayya yau sai kince wani abu game da ni,kin yafe min ko baki yafemin ba,sumayya ya ina kike so na dora raina?,laifi ne na aikatashi na nemi afuwarki sumayya amma kinqi kice komai,kinsan kullum ya nake kwana ya nake tashi da rashin cewa komanki?,kinsan me nakeji cikin qirji na" sai kuma ya sassauta murya cikin sanyi
"Kinfi kowa sanin wane mukhtar sumayya,kinfi kowa sanin wane irin zama mukayi a baya,sumayya ki tausaya min koda ba zaki tausayamin ba ki tausayawa abdallah,abdallah ya zama marayan qarfi da yaji,abdallah na buqatar mu ni da ke a tare,idan baki tausayawa mana ba sumayya waye zaiji tausayinmu duk duniya?,taba qirjina sumayya kiji" ya fada yana fincikar hannunta zuwa qirjinsa,sosai taji zuciyarsa na bugawa,gaza cire hannunta tayi sai da taji ya ambaci wash,da sauri ta dubeshi sai taga yana dafe da kansa yana layi,batasan sanda ta riqeshi ba a rude tana cewa lafiya?,ganin yana neman gun zama ya sanya ta zaunar da shi tana masa sannu,tsahon mintina biyar sannan ya sauke numfashi ya gyara zamansa tana zaune can nesa da shi ya dubeta
"Ciwon kai nake fama da shi,amma wannan duka ba damuwata bace burina kawai ki yafemin" ya fada yana duban qwayar idanunta,a hankali ta janye idanuwanta zuciyarta na mata bitar waye mukhtar agurinta,
"Na yafe maka" ta furta murya can qasa
"Allah ya yafe mana baki daya" wani wawar ajiyar zuciya ya saki,baki daya jikinsa ya saki,wani farinciki yaji yana ratsa kowacce gaba ta jikinsa,yana so yaje ga sumayyan amma sam jikinsa babu qwari ko kadan,sai ya miqa mata hannu
"Taso sumayya kizo kusa da ni don Allah" sai ta girgiza kai ba tare data motsa ba,tilas ya tattaro duk wani ragowar qarfinsa ya kiqe ya isa gareta,kusa da ita ya zauna har tana gogar kafadarta,hakan ne ya sanyata ta janye da sauri tana hada rai
"Meye haka,don nace na yafe maka ai hakan ba yana nufin kai mijina bane ko zan sakw aurenka ba" da sauri ya sake matsawa kusa da ita babu gun matsawa a gunta don ya kaita qarshen kujerar sai ya kama hannunta ya matse cikin nashi
"Sumayya,na sake miki wani laifin don na bada sadakinki,amma bisa sharadin matsawar baki amince ba zan karbi kaya na na haqura"
Wani abu taji yana ratsa zuciyarta mai kama da farinciki,zuciyarta ta karye hawaye ya biyo kuncinta,cikin raunanniyar murya ta kwabe fuskarta
"Ni nace maka ka kai sadakina ba tare da sani na ba?,ai kuwa sai kaje ka karbi abinka don ni ban amince ba,kuma......" Bata ankara ba ya hade bakinsu waje daya wanda hakan yayi sanadiyyar katsewar maganarta,sun dauki kusan minti goma a haka sannan ya janye yana dubanta,qasa tayi da kanta kan fuskarta qaramin murmushi na fita a fuskarta
"Magana ta qare,na sanki tun ba yau ba,dukkan abinda zaki fada a yanzun nasan aji ne kawai za'a jamin ko ba haka ba" sake hade fuska tayi kamar gaske
"Nidai na fada kaje ka karbi sadakinka,bana yi"
"Ok to bari na kira ya abbakar na sanar masa" ya fada yana fiddo wayarsa daga aljihun gaban rigarsa,ganin da gaske lambar ya abbakar yake nemowa ya sanyata qwace wayar
"A'ah,ki bani mana na isar mishi da saqonki"
"Ni bance ba" ta fada a shagwabe,sai yayi jagale yana kallonta saboda tuna masa da baya da tayi ta salon yanayin maganar da tayi
"Kada ki hanani fa tafiya gida yau na kwana a nan"
"Bismillah mana ai ga guri nan" sai yayi kalar tausayi yana dubanta
"Yaushe za'a tara shaidu sumayya ki koma dakinki" idanu ta juya ta dan murguda baki
"Sai shekara iwar haka" qirjinsa ya dafe yana kallonta
"Mutuwa kike so nayi kafin lokacin sannan ko?" Rai ta hade
"Ka daina fadin haka mana ya mukhtar,ni kunya nake ji gaskiya ka bari idan ja shirya zan fada maka ka sanarwa ya abbakar" hannunta wanda ke cikin nashi ya sumbata yana fadin
"Na gode,na gode,na gode sumayya,na gode da karamcin da kika nuna min a rayuwa,na gode da kika nuna ke mai qaunata ce har yanzu" sai ya dakata yana fidda zoben azurfan dake yatsansa ya zura a nata,ya mata yawa hakan ya basu dariya baki dayansu,sai ya cire ya sanya mata a yatsan tsakiya duk da haka ya mata yawa
"Ina son zoben nan sumayy,amma sai naga yafi kyau a hannunki,ki ajiyemin zan karba"
"Idan kuma naji dadinsa bazan maida maka ba"
Dariya ya danyi sannan yace
"Babu komai,ai da kai da kaya duka mallakar wuya ne" sallamar halima ta sanya sumayya miqewa,shigowa tayi dauke da abdallah tana fadin
"Wallahi yaron nan ya koyi rigima,tunda ya tashi yaje zunduma ihu nayi tsammani ma kin jiyo shi"
"Ina zata jiyoshi ta shiga kogin qauna" mukhtar ya fada cikin salon zolaya yana miqa hannu ya amshi abdallah dake ta dokin zuwa gunsa yana kiran abba na,murmushi halima tayi tana yiwa sumayya kallon tsokana ta fice,ita kanta wani dadi taji don babu wanda yaji dadin rabuwarta da mukhtar,qafarta har qaiqayi take taje ta bawa zainab labari.
'Yar kallo sumayya ta koma sanda mukhtar suka soma wasa da abdallah,bata taba ganin d'a da uba irin haka ba,sai wajen qarfe goma ya fito zai tafi,qin tafiya yayi har sai data masa rakiya bakin mota,har ya shiga ya fito ya sake kallonta
"Ban son tafiya sumayya,banqi ace tare da ke zan tafi ba,don Allah ki taimaka ki gama shirye shiryen da duk zaki da wuri,ni na amince ma duk abinda baki qarasa ba ki qarasa shi a gida na zan baki wannan damar,ji nake kamar lokaci na qure mana" murmushi tayi tana jin maganar tasa na sauka sosai cikin zuciyarta
"Kada ka damu ya mukhtar,ka qarasa gida dare yanayi" ta fada tana taka masa,sai da yaja motar ya bar layin sannan ta koma cikin gida.
******* ******* ******
Cikin abinda bai gaza sati biyu ba mukhtar ya sabunta soyayyarsa baki daya,kullum yana tare da ita idan baizo ba kuwa ranar katin waya zaici ubanshi,har tsokanarta su halima sukeyi,wai sai kace wasu masu auren fari,ya dawo mata ya mukhtar dinta sak,sai ta samu kanta da dokanta wajen ganin ta a gidanta cikin sabuwar rayuwa ita da mukhtar dinta da yaronta.