Sashe 201
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ko mai bai iya shafawa ba bare ya ya sanya kaya ya janyo wayarshi ya soma lalubar wayarta,a kashe aka sake ce masa take,sai yaji hankalinsa bai kwanta,lambar ummi ya soma laluba cikin sa'a ta shiga,fitowar ummin daga dakin kenan taga shigowar kiran
"Ummi an yini lpy?"
"Lpy lau almustapha ya aiki?"
"Alhamdulillah" sai kuma yayi shiru,halin nashi ya motsa,itakam da zaiyu shirun da yafi mata,tasan wal'alla sumayyan yake nema,ita kuma batasan zancan yaje kunnenshi,tafiso matarshi ta warke saidai yazo ya tadda labari kaman ma ba'a yi ba
"Ummi.....sumayya" ya fada kaman mai tsoron fadin
"Uhmmmm,wani abu ne?"
"Tun jiya bamuyi magana ba,ko zan samu jinta?" Kaman ta hanashi saidai ba yadda zata hanashi magana da matarshi
"Kashe zan kai mata"
"Ummi batta a haka zan jira" dariya ma yaso bata har sai data ce
"Almustapha?,kaman wanda network din zai gudu?" Kunya ta kamashi amma sai ya dake yayi shiru yana sauraron tafiyar ummin.
Tana zaune ta gama shirin baccinta tana karanta wani qaramin littafin labarai na larbci,qafarta na saman matashi mai laushi,hannunta daya na ajjiye saman cinyarta,wayar ummi ta miqa mata tana cewa
"Almustapha" littafin ta ajjiye ta karba gabanta na faduwa ta kara kunnenta sanda ummin ke juyawa ta fice,shiru yayi kawai yana saurarenta tamkar baya kan layin yana hadiye wani abu,fitar numfashinta kawai ya soma samar masa da nutsuwa,sallama tayi masa sai da ya bada tazarar wasu sakannni sannan ya amsa
"Why sumayya why?,wato idan ban nemeki ba ba zaki neme ni ba?"
"Ba haka bane.....wayarce bansan inda ta fada ba"
"Kaman yaya?" Ya tambayeta,da sauri ta gyara zancanta
"Amm...ina nufin ta dauna daukan chargy ne" tsaki ya ja sannan yace
"Kamanni ace wayar matata ta har takai matsayin da don kanta zata daina daukan chargy?,ki cire layukanki ki bar amfani da ita,gobe da safe za'a kawo miki wasu,daya ni kadai zan dinga kiranki da ita always ta zama akunne kusa da ke,dayan kuma ki kira duk wanda kika ga dama"
"Na gode Allah ya saka da alkhairi ya qara arziqi"
"Amin.....nifa gaskiya na fara gajiya,haquri na ya kusa qarewa fa....a qa'ida ai cikinki ya shiga wata uku...am a doctor nasan yadda zan kula da mata ta" gabanta ya fadi,yau bisa dukkan alamu rigima yake ji tunda taji muryanshi ta fuskanci haka,tayi qas da murya
"Habba mana.....duka saura sati nawa lokacin da suka ce ya cika,ka qara haquri mana please kaji?" Shiru kawai yayi yana sauraren muryarta yana nazari
"Me ya sameki?" Taji ya furta kai tsaye,sai ta hau fiddo da idanu tana kalle kalle,ta daga wayar ta duba voice call ne ba vedio call ba bare tace yana ganinta
"Ni?...ba bau komai me ka gani"
"Akwai wani sauyi tattare da muryarki,kuma jikina ya bani haka"murmushi tayi duk don ta dauke hankalinsa
"wrong doctor,baka canka dai dai ba,am fine,ina shirin yin bacci ma ummi ta shigo"
"Ban yarda ba,but....tunda kince haka ne is ok,ki kunna wayarki kafin a kawo wata"
"An gama yallabai" murmushi yayi,yanajin kaman tana lallabashi ne kawai ya sauka daga kan layin,sai kawai ua datse kiran yana jin wayar kawai bata yi masa ba,jikinsa bai bashi ba,sam ma ba irin wannan hirar yakeso suyi ba,hankalinsa baki daya yayo nijeria.
Ajiyar zuciya ta saki da taga ya datae layin,da alama halin ne yau ya motsa,dole ta tashi sajida ta sanyata ta dauko wayar ta jona a chargy sannan ta kunnata kafin ta kwanta.
****** ****** *******
Washegari misalin sha daya na safiyar ranan yana tsaye gaban mudubi yana shiryawa,kominshi a nutse a tsare,ya gama komai tsaf yana taje sumarshi ya janyi wayoyinshi dake gefe,tun jiya da ita ya kwana cikin ranshi,yana jin mawuyacine idan baiyi rashin ta ido ba yaje kawai ya daukota,yana jin kaman sun shekara goma ne basu ga juna ba,number baba ya soma don ya gaidashi kaman kowacce safiya,idanunshi suka sauka kan takardar dake gefanshi,ya saka hannu ya dauko ya bude ta,ranshi ya baci sosai ba wai don kudin da ya kashe kawai kan takardar ba,sai na yanda su'ad tayi burus da maganarshi.
Yana tsaka da duban takardar ta fito daga wanka tana tsane jikinta da towel
"Yanzu wai har ka shirya zaka fita,nifa gaskiya na gaki da wuni a gida ni kadai kaman mayya,bayan nasan wuraren shan iska birjik amma ka hanani zuwa ko guri daya"
"Mene wannan?" Ya tambayeta yana nuna mata takardar,daga kai tayi ta kalleta sai kuma ta basar tana hade rai
"Nifa gaskiya banda interest shi yasa na ajjiyeta" ranshi ya kuma baci,ya gyara tsaiwarshi yana kafeta da idanunshi masu sanya mutum yin laushi
"Kinsan nawa na biya miki?,kudin mutum nawa na biya ake kadai don kije ki koya ke kadai din?"
"Sai na biyaka kudinka kamin total,amma bazan iya zuwa ba gsky,ai ba ajina bane ba aganni wani ina koyon girki,haka kawai Allah ya maka arziqin da zamu iya daukan kowanne irin cook kawai sai na bata wa kaina lokacin koyon dafe dafe?" Ta amsa mishi ba tare data dubeshi ba ta soma shafa mai,kai ya gyada yana qoqarin hadiye bacin ranshi,ya maida takardar saman madubin ya ajjiye,shi kadai yasan hukuncin da zaya yanke mata,sai ya janyo jakarshi ya riqe a hannunshi,daya hannun kuma yana riqe da wayoyinshi ya soma takawa zai fice
"Ka mance yau zani siyayya?" Ta furta cikin harshen nasara,banza yayi da ita yaci gaba da takawa har ya fice.
A falo ya tadda mai musu girki ta kammala shirya abinci,cikin girmamawa ta rusuna da harshen larabci ta gaidashi ya amsa yana tsaidara,jakarsa ya bude ya fidda rafar kudi irin na qasar dubai masu azabar kauri da yawa ya miqa mata,shaida mata yayi ya sallameta a aiki ga wannan taje na nemi sana'a tayi,cikin rawar jiki ta sanya hannu biyu ta amsa,ita kanta tasan kudin ba qananun kudi bane,zasu isheta yin duk sana'ar da takeso,tabbas ba qaramin taimakonta yayi ba,ta duqa tayi masa godiya mai yawa sannan ta fice.
Yana kurbar tea yake lalubar lambarta,muryarta kawai yake so ya soma ji a wannan safiyar kafin ya fice,daidai lokacin da a wancan bangaren sumayya take takawa a hankali har ta fice daga dakin saboda mai gyaran ya gaya mata ta dinga takawa ko yaya ne.
Sajida na tsaka da mopping tsakar dakin ta jiyo ringing din wayar sumayyan,ajjiye mop stick din tayi ta nufi inda wayar take,sai taga sunan man,tasan halinshi sarai,idan ya kira mamarsu kiran ya zama miscal yayita fada kenan,hakan ya sanya ta daga ta sanar masa yanzu zata kaima sumayyan kada ta zama misscall,gaidashi ta soma yi sannan tace
"Antyn ta fita tattaka qafarta,amman bari na kai mata" jikinshi ya sake bashi irin yanayin jiya,sai ya ajjiye cup din hannunshi yana tattara hankalinshi gareta
"Tattaka qafarta?,me ya samu qafan?" Ya tambayeta yana addu'an kada dai ace cikin ne ya soma sanya mata kunburin qafa har yanzu
"Faduwa tayi" gabanshi yayi wani mummunan faduwa,a rude yace
"Subhanallah?,garin yaya?"
"Anty aysha ce ta turota daga upstair" bai san sanda ya miqe tsaye zumbur ba,cikin matsanancin tashin hankali da qaraji yace
"Upstairs?,mahaukaciya ce ita?,me ya sami qwaqwalwarta?"tsoro ya kama sajida kaman ita tayi laifin,cikin rawar murya
"ban sani ba uncle"ganin yarinyar ta tsorace ya sanyashi qoqarin sanyaya ranshi saidai bakan ya gagara,sai ua rage sautin muryarshi yana tambayarta yadda akai abun ya faru,bata boye masa komai ba ta kwashe duka ta gaya masa,harda nata wanda ta zuba ruwan klien ta fadi,ranshi ya kai qololuwar baci
" kada ki gayawa kowa munyi waya kin gayan me ya faru,ok?"
"Yes uncle" ta fada tana addu'a cikin ranta Allah yasa unclr man yaci uban anty aysha,dama taji haushi sosai abinda ta yiwa anty amira,har kuka tayi,kullum kuma sai ta tausaya mata idan taga tana dingisa qafarta.
Ya jima jingine jikin kujera yana huci shi daya kamar wani mayunwacin zaki,ya rasa wanne hukunci ne ya dace da yarinyar,ba shakka mutum biyu ne rak a duniya zasuyi masa haka ya qyalesu daga ummi sai baba,ya kamata ya nuna mata wa ta tabo,ya kamata ta gane kuskurenta,baiga dalilin ma da zai sanya ya qyale ta ba,data aikata mishi wannan abun data aikata din gwara tayi masa gagarumar sata,gefe guda haushin sumayyan ya kamashi,don me zata boye mishi?,me yasa ba zata gaya mishi ba,yanzun da wani mummunan abu ne ya sameta haka zata yi shiru,batasan muhimmancin lafiyarta a gareshi ba?,kai bama lafiyarta ba,batasan muhimmancin kanta baki daya tattare da tashi rayuwar ba,bazai iya jira har sai ya koma gida sannan ya dauki mataki ba,hakan ya sanya ya soma lalubar lambar CP,bugu uku kacal ya daga,bayan gaisuwa sama sama da kuma ya bayan saduwa ya soma shaida masa abinda yake da buqata,eesha yake so su kamo mishi ita su sanya masa ita bayan kanta,kuma ko waye yazo nemanta kada su sake su bada ita,kai baya so ma su bari asan a station din da suka ajjiyeta,duk da baban eeshan wani ne amma sahun gwiwa ya take na raqumi,hakan ya sanya ba musu suka amsa mishi bayan ya musu bayanin laifin data aikata,ya tambayi mahmoud adress na school dinsu ya aika musu,a yau yaje da buqatar ta kwana bayan cell,wayar ya kashe yana furzar da iska,tabbas sai ta gane shayi ruwa ne.
"Ummi an yini lpy?"
"Lpy lau almustapha ya aiki?"
"Alhamdulillah" sai kuma yayi shiru,halin nashi ya motsa,itakam da zaiyu shirun da yafi mata,tasan wal'alla sumayyan yake nema,ita kuma batasan zancan yaje kunnenshi,tafiso matarshi ta warke saidai yazo ya tadda labari kaman ma ba'a yi ba
"Ummi.....sumayya" ya fada kaman mai tsoron fadin
"Uhmmmm,wani abu ne?"
"Tun jiya bamuyi magana ba,ko zan samu jinta?" Kaman ta hanashi saidai ba yadda zata hanashi magana da matarshi
"Kashe zan kai mata"
"Ummi batta a haka zan jira" dariya ma yaso bata har sai data ce
"Almustapha?,kaman wanda network din zai gudu?" Kunya ta kamashi amma sai ya dake yayi shiru yana sauraron tafiyar ummin.
Tana zaune ta gama shirin baccinta tana karanta wani qaramin littafin labarai na larbci,qafarta na saman matashi mai laushi,hannunta daya na ajjiye saman cinyarta,wayar ummi ta miqa mata tana cewa
"Almustapha" littafin ta ajjiye ta karba gabanta na faduwa ta kara kunnenta sanda ummin ke juyawa ta fice,shiru yayi kawai yana saurarenta tamkar baya kan layin yana hadiye wani abu,fitar numfashinta kawai ya soma samar masa da nutsuwa,sallama tayi masa sai da ya bada tazarar wasu sakannni sannan ya amsa
"Why sumayya why?,wato idan ban nemeki ba ba zaki neme ni ba?"
"Ba haka bane.....wayarce bansan inda ta fada ba"
"Kaman yaya?" Ya tambayeta,da sauri ta gyara zancanta
"Amm...ina nufin ta dauna daukan chargy ne" tsaki ya ja sannan yace
"Kamanni ace wayar matata ta har takai matsayin da don kanta zata daina daukan chargy?,ki cire layukanki ki bar amfani da ita,gobe da safe za'a kawo miki wasu,daya ni kadai zan dinga kiranki da ita always ta zama akunne kusa da ke,dayan kuma ki kira duk wanda kika ga dama"
"Na gode Allah ya saka da alkhairi ya qara arziqi"
"Amin.....nifa gaskiya na fara gajiya,haquri na ya kusa qarewa fa....a qa'ida ai cikinki ya shiga wata uku...am a doctor nasan yadda zan kula da mata ta" gabanta ya fadi,yau bisa dukkan alamu rigima yake ji tunda taji muryanshi ta fuskanci haka,tayi qas da murya
"Habba mana.....duka saura sati nawa lokacin da suka ce ya cika,ka qara haquri mana please kaji?" Shiru kawai yayi yana sauraren muryarta yana nazari
"Me ya sameki?" Taji ya furta kai tsaye,sai ta hau fiddo da idanu tana kalle kalle,ta daga wayar ta duba voice call ne ba vedio call ba bare tace yana ganinta
"Ni?...ba bau komai me ka gani"
"Akwai wani sauyi tattare da muryarki,kuma jikina ya bani haka"murmushi tayi duk don ta dauke hankalinsa
"wrong doctor,baka canka dai dai ba,am fine,ina shirin yin bacci ma ummi ta shigo"
"Ban yarda ba,but....tunda kince haka ne is ok,ki kunna wayarki kafin a kawo wata"
"An gama yallabai" murmushi yayi,yanajin kaman tana lallabashi ne kawai ya sauka daga kan layin,sai kawai ua datse kiran yana jin wayar kawai bata yi masa ba,jikinsa bai bashi ba,sam ma ba irin wannan hirar yakeso suyi ba,hankalinsa baki daya yayo nijeria.
Ajiyar zuciya ta saki da taga ya datae layin,da alama halin ne yau ya motsa,dole ta tashi sajida ta sanyata ta dauko wayar ta jona a chargy sannan ta kunnata kafin ta kwanta.
****** ****** *******
Washegari misalin sha daya na safiyar ranan yana tsaye gaban mudubi yana shiryawa,kominshi a nutse a tsare,ya gama komai tsaf yana taje sumarshi ya janyi wayoyinshi dake gefe,tun jiya da ita ya kwana cikin ranshi,yana jin mawuyacine idan baiyi rashin ta ido ba yaje kawai ya daukota,yana jin kaman sun shekara goma ne basu ga juna ba,number baba ya soma don ya gaidashi kaman kowacce safiya,idanunshi suka sauka kan takardar dake gefanshi,ya saka hannu ya dauko ya bude ta,ranshi ya baci sosai ba wai don kudin da ya kashe kawai kan takardar ba,sai na yanda su'ad tayi burus da maganarshi.
Yana tsaka da duban takardar ta fito daga wanka tana tsane jikinta da towel
"Yanzu wai har ka shirya zaka fita,nifa gaskiya na gaki da wuni a gida ni kadai kaman mayya,bayan nasan wuraren shan iska birjik amma ka hanani zuwa ko guri daya"
"Mene wannan?" Ya tambayeta yana nuna mata takardar,daga kai tayi ta kalleta sai kuma ta basar tana hade rai
"Nifa gaskiya banda interest shi yasa na ajjiyeta" ranshi ya kuma baci,ya gyara tsaiwarshi yana kafeta da idanunshi masu sanya mutum yin laushi
"Kinsan nawa na biya miki?,kudin mutum nawa na biya ake kadai don kije ki koya ke kadai din?"
"Sai na biyaka kudinka kamin total,amma bazan iya zuwa ba gsky,ai ba ajina bane ba aganni wani ina koyon girki,haka kawai Allah ya maka arziqin da zamu iya daukan kowanne irin cook kawai sai na bata wa kaina lokacin koyon dafe dafe?" Ta amsa mishi ba tare data dubeshi ba ta soma shafa mai,kai ya gyada yana qoqarin hadiye bacin ranshi,ya maida takardar saman madubin ya ajjiye,shi kadai yasan hukuncin da zaya yanke mata,sai ya janyo jakarshi ya riqe a hannunshi,daya hannun kuma yana riqe da wayoyinshi ya soma takawa zai fice
"Ka mance yau zani siyayya?" Ta furta cikin harshen nasara,banza yayi da ita yaci gaba da takawa har ya fice.
A falo ya tadda mai musu girki ta kammala shirya abinci,cikin girmamawa ta rusuna da harshen larabci ta gaidashi ya amsa yana tsaidara,jakarsa ya bude ya fidda rafar kudi irin na qasar dubai masu azabar kauri da yawa ya miqa mata,shaida mata yayi ya sallameta a aiki ga wannan taje na nemi sana'a tayi,cikin rawar jiki ta sanya hannu biyu ta amsa,ita kanta tasan kudin ba qananun kudi bane,zasu isheta yin duk sana'ar da takeso,tabbas ba qaramin taimakonta yayi ba,ta duqa tayi masa godiya mai yawa sannan ta fice.
Yana kurbar tea yake lalubar lambarta,muryarta kawai yake so ya soma ji a wannan safiyar kafin ya fice,daidai lokacin da a wancan bangaren sumayya take takawa a hankali har ta fice daga dakin saboda mai gyaran ya gaya mata ta dinga takawa ko yaya ne.
Sajida na tsaka da mopping tsakar dakin ta jiyo ringing din wayar sumayyan,ajjiye mop stick din tayi ta nufi inda wayar take,sai taga sunan man,tasan halinshi sarai,idan ya kira mamarsu kiran ya zama miscal yayita fada kenan,hakan ya sanya ta daga ta sanar masa yanzu zata kaima sumayyan kada ta zama misscall,gaidashi ta soma yi sannan tace
"Antyn ta fita tattaka qafarta,amman bari na kai mata" jikinshi ya sake bashi irin yanayin jiya,sai ya ajjiye cup din hannunshi yana tattara hankalinshi gareta
"Tattaka qafarta?,me ya samu qafan?" Ya tambayeta yana addu'an kada dai ace cikin ne ya soma sanya mata kunburin qafa har yanzu
"Faduwa tayi" gabanshi yayi wani mummunan faduwa,a rude yace
"Subhanallah?,garin yaya?"
"Anty aysha ce ta turota daga upstair" bai san sanda ya miqe tsaye zumbur ba,cikin matsanancin tashin hankali da qaraji yace
"Upstairs?,mahaukaciya ce ita?,me ya sami qwaqwalwarta?"tsoro ya kama sajida kaman ita tayi laifin,cikin rawar murya
"ban sani ba uncle"ganin yarinyar ta tsorace ya sanyashi qoqarin sanyaya ranshi saidai bakan ya gagara,sai ua rage sautin muryarshi yana tambayarta yadda akai abun ya faru,bata boye masa komai ba ta kwashe duka ta gaya masa,harda nata wanda ta zuba ruwan klien ta fadi,ranshi ya kai qololuwar baci
" kada ki gayawa kowa munyi waya kin gayan me ya faru,ok?"
"Yes uncle" ta fada tana addu'a cikin ranta Allah yasa unclr man yaci uban anty aysha,dama taji haushi sosai abinda ta yiwa anty amira,har kuka tayi,kullum kuma sai ta tausaya mata idan taga tana dingisa qafarta.
Ya jima jingine jikin kujera yana huci shi daya kamar wani mayunwacin zaki,ya rasa wanne hukunci ne ya dace da yarinyar,ba shakka mutum biyu ne rak a duniya zasuyi masa haka ya qyalesu daga ummi sai baba,ya kamata ya nuna mata wa ta tabo,ya kamata ta gane kuskurenta,baiga dalilin ma da zai sanya ya qyale ta ba,data aikata mishi wannan abun data aikata din gwara tayi masa gagarumar sata,gefe guda haushin sumayyan ya kamashi,don me zata boye mishi?,me yasa ba zata gaya mishi ba,yanzun da wani mummunan abu ne ya sameta haka zata yi shiru,batasan muhimmancin lafiyarta a gareshi ba?,kai bama lafiyarta ba,batasan muhimmancin kanta baki daya tattare da tashi rayuwar ba,bazai iya jira har sai ya koma gida sannan ya dauki mataki ba,hakan ya sanya ya soma lalubar lambar CP,bugu uku kacal ya daga,bayan gaisuwa sama sama da kuma ya bayan saduwa ya soma shaida masa abinda yake da buqata,eesha yake so su kamo mishi ita su sanya masa ita bayan kanta,kuma ko waye yazo nemanta kada su sake su bada ita,kai baya so ma su bari asan a station din da suka ajjiyeta,duk da baban eeshan wani ne amma sahun gwiwa ya take na raqumi,hakan ya sanya ba musu suka amsa mishi bayan ya musu bayanin laifin data aikata,ya tambayi mahmoud adress na school dinsu ya aika musu,a yau yaje da buqatar ta kwana bayan cell,wayar ya kashe yana furzar da iska,tabbas sai ta gane shayi ruwa ne.