Sashe 75
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna haka hafiz ya fito daga wajen uncle farouq,fuskarsa qunshe da murmushi hannunsa dauke da laptop sabuwar qar,idanun laila suka fara kaiwa kai
"Laaah,ya hafiz sabuwar laptop abba yayi ne?"
"Wannan ba ta abba bace,tawa ce wanda ba za'a london da shi ba" ya fada yana zama tare da budeta ya kunna,tuni laila aka fara raba ido,ta matso kusa da shi
"Da gaske kake ya hafiz" hararta yayi
"Da da wasa nake miki" shiru tayi sannan daga bisani tace
"Allah ko nima na fasa zuwan ne a siya min,kada muje mu dawo dadi ya qare kai kuma ga abarka nan kama mora?" Dariya ta qwacewa sumayya,tana niyyar cewa wani abu anty dije itama ta fito daga dakin hannunta dauke da wata laptop dim,gefansu sumayyan ta zauna tana kallon hafiz
"Tofa,an samu nayi ko?" Murmushi yayi kawai yana danne dannensa dadi ya cikashi,sumayya ta miqawa laptop din tana cewa
"Ungo wannan" amsa tayi tana duban antyn
"Daki zan kai miki?"
"A'ah taki ce,abba laila ya siya miki yace zai miki bayani,akwai abinda ya shirya miki kan bunqasar karatunki yana so kiyi karatu ne da ita,idan mun tafi ina tsammanin akwai makaranta da zai sama miki da zaki koyi karatu ma shekara gudan,nasan baki da matsala ta karatu da rubutu duka kin iya,hakanan turancinki ba laifi zaki iya karantawa ki fahimci wasu abubuwan,fahimtar sosai da maidawa yadda ya kamata ne kawai matsalarki" qamewa tai a gun tana mamaki,to ita ya zata iya da wannan aba da uncle din ya mallaka mata,kasa magana tayi har sai da laila ta saki dan ihu tana karbarta daga hannunta
"Wayyo!,muma munyi computer,ya hafiz ka daina mana kallon banza" cikin sanyin murya da sake gasgata qaunarta da anty dije tace
"Anty na rasa wacce iriyan godiya zan muku,na gode na gode Allah ya saka muku da alkhairi,ya biya muku dukkan buqata ya jiqan magabatanku,ya hada kan zuriyyarku baki daya"
"Amin" anty dijen ta amsa tana shigewa ciki.
Da sauri laila ta miqe ta jona mata chargy hadu da kunnata,tana da rawar kai hakan ya sanya ta iya laptop din kamar wadda ako koyawa,don suna game sosai a cikin ta muhsina daya daga cikin qawayenta jikokin gidan baabaa prof,nan ta fara duba games din ta ta tarar a ciki,ta zabi daya ta fara bugawa minal ta matso tana kallo.
Daga bakin qofa akayi sallama,dukkansu hankalinsu na kan laptop din sai sumayua wadda ta amsa yana waiwayowa,amira ce ke shigowa fuskarta qunshe da murmushi,sanye take da black gown brided tube midi mai adon zane orange a jiki mai dogon hannu,kanta yane da mayafi medium orange haka plate shoes dinta,hannunta riqe da wayarta,fuskarta ba makeup saidai akwai alamun hoda da lipstic,bayanta wata matashiya ce,sanye da baqin skert da t.shirt ruwan omo dukkansu na yadi,sai dan madaidaicin hijab dake wuyanta,kallon farko zaka gane 'yar aiki ce,eh tana daya daga cikin ma'aikatan gidan baabaa prof,qarasowa tayi cikin falon wanda hakan ya ankarar da su laila
"Anty amira ina wuni" suka gaisheta baki dayansu ta amsa tana zama gefan sumayya
"Kin ganni da daddare ko?" Murmushi kawai tayi tana janyo lemo da ruwa nata wanda tun dazun bata sha ba da suka gama cin abinci ta ajjiye gaban amiran tana cewa
"Bismillah"
"Um_um,a qoshe nake,shopping naje nayo sai nace bari na shigo,ina so dama na baki haquri ne kan abunda ya faru dazu" kusan ta mance ma ma ya farun
"Mefa?" Sumayyan ta tambayeta
"Bigeki da antynmu tayi dazu,kiyi haquri don Allah,antynmu ce saidai bata da kirki sam,kiyi haquri" murmushi ta kuma yi har fararen haqoranta na bayyana
"Babu komai,ai karo mukayi"kai amira ta girgiza
" duk da haka,nasan halinta ai,kiyi haquri"
"Bafa komai" ta sake maimaitawa,maida dubanta tayi ga wadda suka shigo din tare,tana tsaye har yanzu
"Ki zauna mana" sumayya tace mata,murmushi tayi tace
"No madam,na gode". Kan ta sake cewa komai wayarsu ta tafi da gidanka dake kitchen ta fara burari,laila ta subi khalipha
" jeka duba khalipha"kanta na ga laptop don bata son a mata game over,da sauri ya miqe ya shige kitchen din minti daya tsakani ya fito
"Anty sumayya ke ake nema" yana fada alqasim ya fado mata,fuska ta tsuke
"Kace bana nan"
"Yace don annabi ki daure ki daga" khaliphan dake tsaye bakin qofar kitchen din ya fada,goshinta ta dafe da tafin hannunta,bata so a hadata da ma'aiki taqi yin abu,amira ta miqe tana dubanta
"Kije ki amsa mana namecy,zan tafi sai da safe ki gaida umman khalipha" ta fadi tana murmushi
"Sai da safe ki gaida gida" sumayyan ta fadi itama tana miqewa,ita tayi kitchen su suka fice ita da mai aikinta.
Murya a sanyaye ya mata sallama,a dake ta amsa
"Bakisan halin da zuciyata ta fada sanadinki ba sumayya,please don Allah ki daure ki dinga daga wayata ko ba zaki ce min komai ba"shiru ta danyi ta rasa me zata ce da shi,zuwa yanzu yaci ace yayi zuciya ya bar nemanta
"me kake so nace mai kake buqata?"
"Yauwa beauty,a qalla ko gaisuwa ma ta wadatar" kusan wannan ne abinda abdur rahman ya gaya mata,gashi yana neman jefata cikin tarkon sabo da jin muryarsa,wannan wanne irin wayo ne,ba zata yarda ba kam
"Sai anjima" tace masa tana kife kan wayar ta fito daga kitchen din tana sauke numfashi,inda ta tashi nan ta koma ya zauna ta janyo wayarta tana laluban lambar mamanta tana son jin muryar abdallah.
****** ******** ********
Ramadan ya rage saura kwanaki uku,nan sumayya taga tsari,yadda anty dije ke tsara gidan nata tare da sauya abubuwa sabida shigar watan,baki ta sake tana mamaki don su duk basu irin wannan,dariya anty dije tayi
"Da kike mamakin nawa gyaran kice idan kika ga na gidan baaba prof saikin yada idonki?"ido ta qwalalo
"duk kyau da tsaruwar wannan gidan sai an sake masa wani tsarin?"
"Duk shekara iwar haka sai dukka gidan sun sake komai nasu,sai su rabar da tsofaffin ga 'yan aikinsu,wasunsu har kayan sawa da yayi shekarar nan ake canza wardrobe baki dayanta" baki sumayya ta sake tana duban anty dije kamar ita ce ke sanya su
"Gaskiya mutanen nan mabarnata ne,yanzu wannan gidan ba ya isheka har qarshen rayuwarka ba,wani ma idan yana wani gu baisan da wani ba,har meye ne zai tsufa a shekara a sauya shi?"dariya sosai anty dije tayi
" lallai har yau bakisan wannan familyn ba,kowa da irin matsayinsa fa,ita rayuwa kowa da inda Allah ya ajiyeahi,idan kaga rayuwar wasu kai a gunka barna ce da almubazzaranci,ko kaga tsabar warya ce ko bazata yiwu ba,amma kaima da Allah zai kaika irin wannan matsayin babu shakka sai kayi kamar ko fiye da abinda yakeyi,yanzu kamar ni din nan,da wasu zasu ga abinda nake cewa zasuyi nima almubazzaranci bane,amma ba haka bane,idan Allah ya wadataka kana da shi ka sauya to ka bawa na qasa da kai wancan su amfana suma,ba ka qanqame ba ka qanqame jama'a ba,amma.....zauna na gaya miki su waye wadan nan family din kinji"ba musu sumayyan ta zauna tana baza kunne,itama anty dijen zama tayi,kafin tace komai laila ta shigo tana sanar mata tayi baquwa tilas suka katse hirar ta fita wajensu,sumayya ta tashi ta kama mata aikin da ta tafi ta bari.
********* ****** ********
Baki daya a yanzu rayuwar gidan bata yiwa karima dadi,bata da buri a yanzu da ya wuce taga yaranta da mijinta kusa da ita amma abu ya gagara,kowa tsoro da haushin zama kusa da ita yake,hatta da lukman din ma kwanciyar bacci kadai ke kawoshi bangaren,ya sauya mata irin sauyin da bata taba zata ba,bai shiga shirginta indai ba haqqinta na aure zai sauke mata ba,wanda shima yasan idan ya take mata sai Allah ya tuhumeshi,a nan takan so jan ra'ayinsa amma abu yaci tura,da ya gama yake wanka idan an kusa asuba ya zauna karatun qur'ani da addu'o'i har sai an kirayi asuba ya fita yayi sallah,idan ya dawo ya zarce wajen hajiya su hafu da yara suyi karatu sannan su shirya ya miqa su makaranta,idan ya dawo shine zai shigo mata yayi wanka ya fice ko sauraron abincinta baiyi gun hajiya shima yake ci,hakan shi ya sake taka muhimmiyar rawa wajen rugujewar duk wani aiki da zata masa,walau na abinci ko na jinnu,ya tsayawa addu'a abincinta kuwa baici bare ya dameshi,bata gane bata da wayo ba sai sanda taso ta gwada yi masa tawaye kan yadda yake maganar sumayya da daukar yaranta ya kaiwa mama su,ranar taga tijarar da tunda Allah ya hadata da shi bai taba yi mata ba,tayi kuka na fitar rai,a hankali kuma sai ta soma tunanin me yafi zaman lafiya dadi?,me zaisa ba zata haqura da komai ba ta kawo qarshen wannan zaman fagen yaqin da sukeyi,abinda bata sani ba tanqwara busashen itace abune mai wahala,ta riga da ra yiwa kanta mummunar lamba wajensa.
Duk sanda yaje yakanyi yunqurin karbar adreas din sumayya wajen zainab ko halima,saidai duk sanda yaso yin hakan sai ya taras basa nan suna tahfiz,ita kuwa mama ba wani riqe adress din tayi ba,yaciji yatsa yaji ciwon abun da tun lokacin aurensu da tace zata gidan anty dijen lokacin da shima zaije abujan bai bita ba yaga gidan,da tuni yanzu bakinsa alekum sai ya kama hanya,wayarta kuwa idan ya kira sau biyar idan yaci sa'a zata daga sau daya su gaisa ta tambayi yara,daga haka zata katse kiran sai kuma wani lokacin.
****** ******** ********
Ranar lahadi da daddare watan azumi ya bayyana,hakan ya sanya litinin daukacin al'umar musulmin duniya suka tashi da azumi a bakinsu,duk gidan kowa na azumi banda minal saboda shekarunta basu qarasa ba,ta fara gwadawa zuwa sha biyu anty dije ta bata abinci,kafin azahar su laila anyi laqwas saman kujera,khalipha an fara mutstsuka idanuwa,dariya sosai sumayya ta dinga sheqa musu yayin da anty dije tayi kicin kicin da fuska don kada ma wani yaga fuskar da zaice zai karya,hafiz ne kadai da qwarinsa da yake shine babba.
"Laaah,ya hafiz sabuwar laptop abba yayi ne?"
"Wannan ba ta abba bace,tawa ce wanda ba za'a london da shi ba" ya fada yana zama tare da budeta ya kunna,tuni laila aka fara raba ido,ta matso kusa da shi
"Da gaske kake ya hafiz" hararta yayi
"Da da wasa nake miki" shiru tayi sannan daga bisani tace
"Allah ko nima na fasa zuwan ne a siya min,kada muje mu dawo dadi ya qare kai kuma ga abarka nan kama mora?" Dariya ta qwacewa sumayya,tana niyyar cewa wani abu anty dije itama ta fito daga dakin hannunta dauke da wata laptop dim,gefansu sumayyan ta zauna tana kallon hafiz
"Tofa,an samu nayi ko?" Murmushi yayi kawai yana danne dannensa dadi ya cikashi,sumayya ta miqawa laptop din tana cewa
"Ungo wannan" amsa tayi tana duban antyn
"Daki zan kai miki?"
"A'ah taki ce,abba laila ya siya miki yace zai miki bayani,akwai abinda ya shirya miki kan bunqasar karatunki yana so kiyi karatu ne da ita,idan mun tafi ina tsammanin akwai makaranta da zai sama miki da zaki koyi karatu ma shekara gudan,nasan baki da matsala ta karatu da rubutu duka kin iya,hakanan turancinki ba laifi zaki iya karantawa ki fahimci wasu abubuwan,fahimtar sosai da maidawa yadda ya kamata ne kawai matsalarki" qamewa tai a gun tana mamaki,to ita ya zata iya da wannan aba da uncle din ya mallaka mata,kasa magana tayi har sai da laila ta saki dan ihu tana karbarta daga hannunta
"Wayyo!,muma munyi computer,ya hafiz ka daina mana kallon banza" cikin sanyin murya da sake gasgata qaunarta da anty dije tace
"Anty na rasa wacce iriyan godiya zan muku,na gode na gode Allah ya saka muku da alkhairi,ya biya muku dukkan buqata ya jiqan magabatanku,ya hada kan zuriyyarku baki daya"
"Amin" anty dijen ta amsa tana shigewa ciki.
Da sauri laila ta miqe ta jona mata chargy hadu da kunnata,tana da rawar kai hakan ya sanya ta iya laptop din kamar wadda ako koyawa,don suna game sosai a cikin ta muhsina daya daga cikin qawayenta jikokin gidan baabaa prof,nan ta fara duba games din ta ta tarar a ciki,ta zabi daya ta fara bugawa minal ta matso tana kallo.
Daga bakin qofa akayi sallama,dukkansu hankalinsu na kan laptop din sai sumayua wadda ta amsa yana waiwayowa,amira ce ke shigowa fuskarta qunshe da murmushi,sanye take da black gown brided tube midi mai adon zane orange a jiki mai dogon hannu,kanta yane da mayafi medium orange haka plate shoes dinta,hannunta riqe da wayarta,fuskarta ba makeup saidai akwai alamun hoda da lipstic,bayanta wata matashiya ce,sanye da baqin skert da t.shirt ruwan omo dukkansu na yadi,sai dan madaidaicin hijab dake wuyanta,kallon farko zaka gane 'yar aiki ce,eh tana daya daga cikin ma'aikatan gidan baabaa prof,qarasowa tayi cikin falon wanda hakan ya ankarar da su laila
"Anty amira ina wuni" suka gaisheta baki dayansu ta amsa tana zama gefan sumayya
"Kin ganni da daddare ko?" Murmushi kawai tayi tana janyo lemo da ruwa nata wanda tun dazun bata sha ba da suka gama cin abinci ta ajjiye gaban amiran tana cewa
"Bismillah"
"Um_um,a qoshe nake,shopping naje nayo sai nace bari na shigo,ina so dama na baki haquri ne kan abunda ya faru dazu" kusan ta mance ma ma ya farun
"Mefa?" Sumayyan ta tambayeta
"Bigeki da antynmu tayi dazu,kiyi haquri don Allah,antynmu ce saidai bata da kirki sam,kiyi haquri" murmushi ta kuma yi har fararen haqoranta na bayyana
"Babu komai,ai karo mukayi"kai amira ta girgiza
" duk da haka,nasan halinta ai,kiyi haquri"
"Bafa komai" ta sake maimaitawa,maida dubanta tayi ga wadda suka shigo din tare,tana tsaye har yanzu
"Ki zauna mana" sumayya tace mata,murmushi tayi tace
"No madam,na gode". Kan ta sake cewa komai wayarsu ta tafi da gidanka dake kitchen ta fara burari,laila ta subi khalipha
" jeka duba khalipha"kanta na ga laptop don bata son a mata game over,da sauri ya miqe ya shige kitchen din minti daya tsakani ya fito
"Anty sumayya ke ake nema" yana fada alqasim ya fado mata,fuska ta tsuke
"Kace bana nan"
"Yace don annabi ki daure ki daga" khaliphan dake tsaye bakin qofar kitchen din ya fada,goshinta ta dafe da tafin hannunta,bata so a hadata da ma'aiki taqi yin abu,amira ta miqe tana dubanta
"Kije ki amsa mana namecy,zan tafi sai da safe ki gaida umman khalipha" ta fadi tana murmushi
"Sai da safe ki gaida gida" sumayyan ta fadi itama tana miqewa,ita tayi kitchen su suka fice ita da mai aikinta.
Murya a sanyaye ya mata sallama,a dake ta amsa
"Bakisan halin da zuciyata ta fada sanadinki ba sumayya,please don Allah ki daure ki dinga daga wayata ko ba zaki ce min komai ba"shiru ta danyi ta rasa me zata ce da shi,zuwa yanzu yaci ace yayi zuciya ya bar nemanta
"me kake so nace mai kake buqata?"
"Yauwa beauty,a qalla ko gaisuwa ma ta wadatar" kusan wannan ne abinda abdur rahman ya gaya mata,gashi yana neman jefata cikin tarkon sabo da jin muryarsa,wannan wanne irin wayo ne,ba zata yarda ba kam
"Sai anjima" tace masa tana kife kan wayar ta fito daga kitchen din tana sauke numfashi,inda ta tashi nan ta koma ya zauna ta janyo wayarta tana laluban lambar mamanta tana son jin muryar abdallah.
****** ******** ********
Ramadan ya rage saura kwanaki uku,nan sumayya taga tsari,yadda anty dije ke tsara gidan nata tare da sauya abubuwa sabida shigar watan,baki ta sake tana mamaki don su duk basu irin wannan,dariya anty dije tayi
"Da kike mamakin nawa gyaran kice idan kika ga na gidan baaba prof saikin yada idonki?"ido ta qwalalo
"duk kyau da tsaruwar wannan gidan sai an sake masa wani tsarin?"
"Duk shekara iwar haka sai dukka gidan sun sake komai nasu,sai su rabar da tsofaffin ga 'yan aikinsu,wasunsu har kayan sawa da yayi shekarar nan ake canza wardrobe baki dayanta" baki sumayya ta sake tana duban anty dije kamar ita ce ke sanya su
"Gaskiya mutanen nan mabarnata ne,yanzu wannan gidan ba ya isheka har qarshen rayuwarka ba,wani ma idan yana wani gu baisan da wani ba,har meye ne zai tsufa a shekara a sauya shi?"dariya sosai anty dije tayi
" lallai har yau bakisan wannan familyn ba,kowa da irin matsayinsa fa,ita rayuwa kowa da inda Allah ya ajiyeahi,idan kaga rayuwar wasu kai a gunka barna ce da almubazzaranci,ko kaga tsabar warya ce ko bazata yiwu ba,amma kaima da Allah zai kaika irin wannan matsayin babu shakka sai kayi kamar ko fiye da abinda yakeyi,yanzu kamar ni din nan,da wasu zasu ga abinda nake cewa zasuyi nima almubazzaranci bane,amma ba haka bane,idan Allah ya wadataka kana da shi ka sauya to ka bawa na qasa da kai wancan su amfana suma,ba ka qanqame ba ka qanqame jama'a ba,amma.....zauna na gaya miki su waye wadan nan family din kinji"ba musu sumayyan ta zauna tana baza kunne,itama anty dijen zama tayi,kafin tace komai laila ta shigo tana sanar mata tayi baquwa tilas suka katse hirar ta fita wajensu,sumayya ta tashi ta kama mata aikin da ta tafi ta bari.
********* ****** ********
Baki daya a yanzu rayuwar gidan bata yiwa karima dadi,bata da buri a yanzu da ya wuce taga yaranta da mijinta kusa da ita amma abu ya gagara,kowa tsoro da haushin zama kusa da ita yake,hatta da lukman din ma kwanciyar bacci kadai ke kawoshi bangaren,ya sauya mata irin sauyin da bata taba zata ba,bai shiga shirginta indai ba haqqinta na aure zai sauke mata ba,wanda shima yasan idan ya take mata sai Allah ya tuhumeshi,a nan takan so jan ra'ayinsa amma abu yaci tura,da ya gama yake wanka idan an kusa asuba ya zauna karatun qur'ani da addu'o'i har sai an kirayi asuba ya fita yayi sallah,idan ya dawo ya zarce wajen hajiya su hafu da yara suyi karatu sannan su shirya ya miqa su makaranta,idan ya dawo shine zai shigo mata yayi wanka ya fice ko sauraron abincinta baiyi gun hajiya shima yake ci,hakan shi ya sake taka muhimmiyar rawa wajen rugujewar duk wani aiki da zata masa,walau na abinci ko na jinnu,ya tsayawa addu'a abincinta kuwa baici bare ya dameshi,bata gane bata da wayo ba sai sanda taso ta gwada yi masa tawaye kan yadda yake maganar sumayya da daukar yaranta ya kaiwa mama su,ranar taga tijarar da tunda Allah ya hadata da shi bai taba yi mata ba,tayi kuka na fitar rai,a hankali kuma sai ta soma tunanin me yafi zaman lafiya dadi?,me zaisa ba zata haqura da komai ba ta kawo qarshen wannan zaman fagen yaqin da sukeyi,abinda bata sani ba tanqwara busashen itace abune mai wahala,ta riga da ra yiwa kanta mummunar lamba wajensa.
Duk sanda yaje yakanyi yunqurin karbar adreas din sumayya wajen zainab ko halima,saidai duk sanda yaso yin hakan sai ya taras basa nan suna tahfiz,ita kuwa mama ba wani riqe adress din tayi ba,yaciji yatsa yaji ciwon abun da tun lokacin aurensu da tace zata gidan anty dijen lokacin da shima zaije abujan bai bita ba yaga gidan,da tuni yanzu bakinsa alekum sai ya kama hanya,wayarta kuwa idan ya kira sau biyar idan yaci sa'a zata daga sau daya su gaisa ta tambayi yara,daga haka zata katse kiran sai kuma wani lokacin.
****** ******** ********
Ranar lahadi da daddare watan azumi ya bayyana,hakan ya sanya litinin daukacin al'umar musulmin duniya suka tashi da azumi a bakinsu,duk gidan kowa na azumi banda minal saboda shekarunta basu qarasa ba,ta fara gwadawa zuwa sha biyu anty dije ta bata abinci,kafin azahar su laila anyi laqwas saman kujera,khalipha an fara mutstsuka idanuwa,dariya sosai sumayya ta dinga sheqa musu yayin da anty dije tayi kicin kicin da fuska don kada ma wani yaga fuskar da zaice zai karya,hafiz ne kadai da qwarinsa da yake shine babba.