Sashe 172
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bai direta ba sai da ya saita mata hanyar matattakala,ya harde hannunshi yana mata nuni da idanu kan ta hau,babu musu ta haura saman kunyar abinda ya mata cikin jama'a na kama ta har cikin dakinshi,qofa ya maida ya kulle ya waiwayo cikin shammata ya turata saman gadon,baki daya ya danneta,ya dora mata nauyinshi,fuskarsa kawai ya dago yana dubanta,idanunshi cikin nata suna musayar numfashi,sosai ta gane kuranta,numfashinta ya soma mata nauyi
"Qirjina ka daga ni"
"Eh ai so nake na nuna miki banbancin,don na lura kin soma rainani saboda kinga makwancina.....me kike gayawa amira take rawan qafan zuwa ta sameki?,sannan me kike gayawa wadan can shashashan suke babbaka dariya kaman hauka sabon kamu?" Narai narai tayi da idanuwa,yatsansa ya dora saman lebansa yana fadin
"Shshshshsh,banson wani kuka,idan kuwa kika sake kikayi yau tilldown zanyi sai an miki ruwan zafi"cikin taushin murya a shagwabe da son qwatar kanta tace
"Allah babu komai ka yarda dani"sosai ta masa kyau,shagabarta ta taba zuciyarsa qwarai,murmushi na son qwace masa amma ya dake,bai son ta gwada abinda su'ad taso dauka dabi'ar yi,wato kwarzantashi da yabonshi da fadan qwarewarshi a kan shimfidarsu gurin qawayenta,randa kunnensa ya ji masa Allah ya sanya ranar ta soma,mutum biyu ta gayawa,ranar taga tashin hankalin da bata taba gani ba,don cewa yayi tunda ta gaya musu to ta sa a ranta sai ya auresu babu fashi,har ciwo sai da yaso kamata,babu shiri ta fatattakesu sukayi baran baran bata sake ganinsu ba,da qyar ta sha kanshi
"ta yaya zan yarda da ke?"
"Saboda da gaske nake,ba aninda zan gaya musu,nasan fa haramunne mace ta dinga fadin sirrin mijinta,Allah ya la'anci mai aikata hakan"murmushin da baiso dole ya kubce masa,sai ya samu kansa da sanya hannunshi kan hancinta yana jan hancin
"au Allah,ashe ni din mijinki ne" kunya ta kamata,ta rasa inda zata tsomala ranta,sai kawai ya rintse idanuwanta
"Kada fa ki tsammaci na haqura,dole ki bani wani abu da zai sanyani na haquran,idan ba haka ba,Allah yau sai jikinki ya gaya miki" ya fada yana shan qamshi,da sauri ta bude idanunta,kamar zata saka kuka
"To ni mai zan baka?,banda abinda zan baka"
"Akwai" ya fada yana jifanta da wani kallo wanda shi kansa baisan yana mata shi ba,sosai take amsar saqon da yake aikata mata,sai ta kasa janyewa daga kallonshi tamkar masu kallon quda,nuni yayi mata da bakinshi yana cewa
"Kiss me,shine kadai zai sanya na haqura" da sauri ta dago kanta da niyyar yi masa din don ya barta,nauyinsa da kunyarsa take ji amma shi baya gani ne wai,tana dora bakin nata ya hade su waje guda ya shiga sarrafa shi yadda yake so,bashi ya barta ba sai da ya tsotsi lips dinta son ranshi,da gudu ta fada toilet,tana iya jiyoshi cikin rarraunan murya mai taushi yana cewa
"Be carefull,ke da su yanzu akwai banbanci"mamakinsa take,wai almustapha ne haka?,dama haka yake?,tayi maganar a zuciyarta tana tsaye gaban mudubi tana duban kanta murmushi ya qwace mata,wanka ta sake yi saboda kwanciya sannan ta daura alwala ta fito.
Gaban drawer ta ganshi tsaye ya zuge jakarshi,jikinta ta shafe da turaruka bayan ta shafa mai wanda ya qarawa fatarta laushi,ta taka a hankali ta isa inda abun sallah yake ta shinfida zata yi shafa'i da wutiri,har ta idar yana tsaye kaman mai nazari,qaramin tsaki ya saki ya koma gefan gadon ya zauna ta daga kai tana son dubanshi,wai meke sauyashi haka ne?,dazu da zata shiga toilet murmushi ne kwance saman fuskarshi amma yanzu ba haka bane,can qasa taji yace
"Gobe adam zaizo zamu wuce jigawa wajen baba,i think sai wajen alhamis zamu dawo tare da shi"
"Allah ya nuna mana" ta fada tana miqewa ta fahimci kayan sawarshi yake son hadawa ya kasa,hakan ya sanya ta qarasa bakin cupboard din ta soka zaqulo kayan daya bayan daya,sai ya bita da kallo,yana son yaga damuwar tafiyar da zaiyi ya barta ko qanqani ke saman fuskarta,mutum ne shi mai son a kula da shi,rashin hango hakan da baiyi ba sai ya sake dagula masa lissafi,sam baison zuwa jigawar nan,saidai umarnin baban babu abinda zai hanashi binsa matuqar hakan bai sabawa mahalicci ba.
Wani tsakin ya sake ja,yanajin duka lissafinshi ya dagule,bai taba jin wata tafiya ta dameshi ba sai wannan 'yar qanqanuwar tafiya da bata kai matsayin komai ba a irin tafuye tafuyen da ya saba yi,ya bar gida tsawon wata da watanni ba'a ganshi ba shima baiga kowa nashi ba
"Bar kayan,zan samu wasu a can,zo nan" ya fada yana dubanta,ta waiwayo sannan ta tako a hankali zuwa inda yake,da idanu ya nuna mata hijabin jikinta,gabanta ya fadi,bata tsammaci zai ce ta fidda shi ba shi ya sanya ta gwada wata riga da amira ta bata,ta mance da ita baki daya sai yau cikin kaya ta ganota,idanunshi a kanta yana tabbatar mata da cika umarninsa,haka ta sanya hannu tana ji tana gani ta cire din
"Sunbahanallah" ya fada da wani irin amo,hannunshi ya bude mata yana jingine da gadon,sai taci gaba da takowa har inda yake ta shige jikinsa ya rufe hannayensa yana shinshinar qamshinta,ta jima ajikinsa yana abinda ranshi keso,zuwa sannan ya soma sakin layi,a kunnenta ya rada mata
"Naso na barki to have some rest,but i will miss you gobe,zan iya kasancewa dake?,kin amince?" Kanta ta daga masa cikin kasala
"Thank you,thank you soo much" ya fada cikin murya mai cike da shauqi,yanayin yadda ya tafi da ita ya tilasta mata bashi cikakken hadin kai wanda hakan ya yi masa dari bisa dari.
Tana jikinsa amma tunaninta yake,wannan daren ya sake zamar masa na musamman,wani abu ya tsaye masa game da ita,ji yake kamar ya nemi alfarma wajen baba ya barshi a nan,ko kuma ya dauketa su tafi tare,saidai babu damar hakan,ya tabbata tunda baban ya nemi ganinsu wani muhimmin abu zasu yi a can.
Yana tsaye yana shiryawa itama tana tsaye kusa da shi tana miqa masa duk abinda zaiyi amfani da shi,yau din ma dai surukuta suke taqi kallonshi,duk da yadda taso ta morewa kallon nashi,sakamakon shigar shadda da yau yayi,duk da cewa ba dinkin tazarce bace amma tayi masifar yi masa kyau,kwalliyar taso ta tafi da ita don dai kawai ta maze,ga kuma kunyar da jiya ya bata,har ya kammala shiryawa tsaf ta miqa masa kofin hadden coffe wanda ta daidaita masa zafinshi,kofin na riqe a hannunshi,tururinsa da qamshinsa na shiga masa hamci,yayin da dukkan idanunsa da tunaninsa suke kacokam a kanta,ya lura sarai shigar tayi mata,amma bai furta mata ko nuna mata ba
"Wai dama haka aure yake?,haka ake ji?" Yake qiyasatawa a ransa,a hakan yasan bata gama sakewa da shi ba,baisan wanne matsayi ta bashi cikin zuciyarta ba baya ga matsayin miji,sarari yake nema wanda zai zauna ya dasa mata zazzafar soyayyarsa cikin zuciyarta,don har yau baisan a wanne rank ta bashi ba,sai data gaji da shirun ta waiwayo ta dubeshi
"Yana sake hucewa,yaya kuma na jiranka"
"Eh jira dama nake ki gama yajin aikin kallona din sai na sha" ya fada yana kai kofin bakinsa,kai ta kautar tana murmushi a boye,a haka sai ka rantse bai iya magana ba sam,amma idan ya yankota a nutse sai ta tsaya maka.
Ta baya taji ya ruqota,ya mannata da jikinsa kansa saitin kunnenta
"Me zan samu?" Ya fadi yana duban wani kwantaccen gashi dake wuyanta mai santsi,shiru tayi tana tunanin me yake nufi,ganin bata ce komai ba sai ya dora
"Zan wuce,kada ki fiya fita wajen gidan nan,coz nasan akwai baqi da yawa da za'a iya yi a kwanakin nan,ok?"kai ta gyada tana jin wani iri babu dadi,sakinta yayi sanda wayarshi ta soma ruri ya duba yaga yaya adam ne,wanda ya gama shirinsa shi kadai yake jira,ya tsammaci ma shi zai rigashi gama shiryawa kamar yadda aka saba,sai gashi wannan karon almustaphan yana son ya makarar da su,juyawa yayi a hankali zaya fice,sai ta biyo bayanshi cikin sanyin jiki tace
"adawo lafiya,Allah ya tsare hanya,a gaishemin da baba"saqon yayi masa dadi,sai yayi kamar zai juyo sai kuma ya fasa,ya amsa da
"ok" yana ficewa,bayanshi tabi da kallo,bata taba ganin mutumin da kayan hausawa suka masa kyau har haka irinsa ba.
Haka kawai take jin ba dadi,wani yanayi na shigarta,qarfafa jikinta tayi ta gyare ko ina tsaf,sannan tayi wanka tare da yin madaidaiciyar kwalliya ta yafa wadataccen mayafi ta fice wajen su ummee,sai data shiga ta gaida,gidan babu laifi ya sake cika,ga jikoki nam sun soma halartar gidan,yaran huda anty farida da 'ya'yan adam yaran kishiyar ni'ima data taho da su,a wajen maamaa ta hadu da ni'iman,fuska sake suka gaisa,hira ta dan gudana tsakaninsj,haka nan ni'ima ta kwantawa sumayya kamar yadda sumayyan ta kwantawa ni'ima,daga bisani tace bari taje wajen ummee,a can ta tuqe wajen ummeen,cikin siyasa ummen ke janta da hira tana son taji ya zaman nasu yake,sosai tayi qoqarin nuna mata komai lafiya yake,hakan ya sake faranta ran ummeen matuqa,sai ga amira da azahar a gidan,ranar sunga tabara,tunda taji labarin yaa man din sun tafi jigawa tace sai ra taho,ya saif ya iya da tabara,haka ya barta amma da sharafin wuni kawai zata dinga ta dawo,wunin baki daya ya zowa sumayya cikin sakewa,hankalinta kwance,babu gilmawar eesha sam,bata san ina tayi ba,bata san meke faruwa ba don haka babu abinda yazo ranta gamenda eeshan,bata koma sashenta ba sai bayan isha'i,kasa zama tayi,baki daya sashen nata yayi mata babu dadi,hakan ya sanya ta koma neman 'yan kwana,da fari kowa qi yayi,sabida sashen ba wajen zuwan kowa bane,daga mai sashen har uwar gidansa ba masu jan jama'a bane,humaida da humaira suka ce sai sunje,hakan ya sanya nadiya da yusra binsu suma,a dakin gadonta na qasa ta saukesu,hakan ya debe mata kewa matuqa,don suna tsaka da hira bacci ya kwashesu.
"Qirjina ka daga ni"
"Eh ai so nake na nuna miki banbancin,don na lura kin soma rainani saboda kinga makwancina.....me kike gayawa amira take rawan qafan zuwa ta sameki?,sannan me kike gayawa wadan can shashashan suke babbaka dariya kaman hauka sabon kamu?" Narai narai tayi da idanuwa,yatsansa ya dora saman lebansa yana fadin
"Shshshshsh,banson wani kuka,idan kuwa kika sake kikayi yau tilldown zanyi sai an miki ruwan zafi"cikin taushin murya a shagwabe da son qwatar kanta tace
"Allah babu komai ka yarda dani"sosai ta masa kyau,shagabarta ta taba zuciyarsa qwarai,murmushi na son qwace masa amma ya dake,bai son ta gwada abinda su'ad taso dauka dabi'ar yi,wato kwarzantashi da yabonshi da fadan qwarewarshi a kan shimfidarsu gurin qawayenta,randa kunnensa ya ji masa Allah ya sanya ranar ta soma,mutum biyu ta gayawa,ranar taga tashin hankalin da bata taba gani ba,don cewa yayi tunda ta gaya musu to ta sa a ranta sai ya auresu babu fashi,har ciwo sai da yaso kamata,babu shiri ta fatattakesu sukayi baran baran bata sake ganinsu ba,da qyar ta sha kanshi
"ta yaya zan yarda da ke?"
"Saboda da gaske nake,ba aninda zan gaya musu,nasan fa haramunne mace ta dinga fadin sirrin mijinta,Allah ya la'anci mai aikata hakan"murmushin da baiso dole ya kubce masa,sai ya samu kansa da sanya hannunshi kan hancinta yana jan hancin
"au Allah,ashe ni din mijinki ne" kunya ta kamata,ta rasa inda zata tsomala ranta,sai kawai ya rintse idanuwanta
"Kada fa ki tsammaci na haqura,dole ki bani wani abu da zai sanyani na haquran,idan ba haka ba,Allah yau sai jikinki ya gaya miki" ya fada yana shan qamshi,da sauri ta bude idanunta,kamar zata saka kuka
"To ni mai zan baka?,banda abinda zan baka"
"Akwai" ya fada yana jifanta da wani kallo wanda shi kansa baisan yana mata shi ba,sosai take amsar saqon da yake aikata mata,sai ta kasa janyewa daga kallonshi tamkar masu kallon quda,nuni yayi mata da bakinshi yana cewa
"Kiss me,shine kadai zai sanya na haqura" da sauri ta dago kanta da niyyar yi masa din don ya barta,nauyinsa da kunyarsa take ji amma shi baya gani ne wai,tana dora bakin nata ya hade su waje guda ya shiga sarrafa shi yadda yake so,bashi ya barta ba sai da ya tsotsi lips dinta son ranshi,da gudu ta fada toilet,tana iya jiyoshi cikin rarraunan murya mai taushi yana cewa
"Be carefull,ke da su yanzu akwai banbanci"mamakinsa take,wai almustapha ne haka?,dama haka yake?,tayi maganar a zuciyarta tana tsaye gaban mudubi tana duban kanta murmushi ya qwace mata,wanka ta sake yi saboda kwanciya sannan ta daura alwala ta fito.
Gaban drawer ta ganshi tsaye ya zuge jakarshi,jikinta ta shafe da turaruka bayan ta shafa mai wanda ya qarawa fatarta laushi,ta taka a hankali ta isa inda abun sallah yake ta shinfida zata yi shafa'i da wutiri,har ta idar yana tsaye kaman mai nazari,qaramin tsaki ya saki ya koma gefan gadon ya zauna ta daga kai tana son dubanshi,wai meke sauyashi haka ne?,dazu da zata shiga toilet murmushi ne kwance saman fuskarshi amma yanzu ba haka bane,can qasa taji yace
"Gobe adam zaizo zamu wuce jigawa wajen baba,i think sai wajen alhamis zamu dawo tare da shi"
"Allah ya nuna mana" ta fada tana miqewa ta fahimci kayan sawarshi yake son hadawa ya kasa,hakan ya sanya ta qarasa bakin cupboard din ta soka zaqulo kayan daya bayan daya,sai ya bita da kallo,yana son yaga damuwar tafiyar da zaiyi ya barta ko qanqani ke saman fuskarta,mutum ne shi mai son a kula da shi,rashin hango hakan da baiyi ba sai ya sake dagula masa lissafi,sam baison zuwa jigawar nan,saidai umarnin baban babu abinda zai hanashi binsa matuqar hakan bai sabawa mahalicci ba.
Wani tsakin ya sake ja,yanajin duka lissafinshi ya dagule,bai taba jin wata tafiya ta dameshi ba sai wannan 'yar qanqanuwar tafiya da bata kai matsayin komai ba a irin tafuye tafuyen da ya saba yi,ya bar gida tsawon wata da watanni ba'a ganshi ba shima baiga kowa nashi ba
"Bar kayan,zan samu wasu a can,zo nan" ya fada yana dubanta,ta waiwayo sannan ta tako a hankali zuwa inda yake,da idanu ya nuna mata hijabin jikinta,gabanta ya fadi,bata tsammaci zai ce ta fidda shi ba shi ya sanya ta gwada wata riga da amira ta bata,ta mance da ita baki daya sai yau cikin kaya ta ganota,idanunshi a kanta yana tabbatar mata da cika umarninsa,haka ta sanya hannu tana ji tana gani ta cire din
"Sunbahanallah" ya fada da wani irin amo,hannunshi ya bude mata yana jingine da gadon,sai taci gaba da takowa har inda yake ta shige jikinsa ya rufe hannayensa yana shinshinar qamshinta,ta jima ajikinsa yana abinda ranshi keso,zuwa sannan ya soma sakin layi,a kunnenta ya rada mata
"Naso na barki to have some rest,but i will miss you gobe,zan iya kasancewa dake?,kin amince?" Kanta ta daga masa cikin kasala
"Thank you,thank you soo much" ya fada cikin murya mai cike da shauqi,yanayin yadda ya tafi da ita ya tilasta mata bashi cikakken hadin kai wanda hakan ya yi masa dari bisa dari.
Tana jikinsa amma tunaninta yake,wannan daren ya sake zamar masa na musamman,wani abu ya tsaye masa game da ita,ji yake kamar ya nemi alfarma wajen baba ya barshi a nan,ko kuma ya dauketa su tafi tare,saidai babu damar hakan,ya tabbata tunda baban ya nemi ganinsu wani muhimmin abu zasu yi a can.
Yana tsaye yana shiryawa itama tana tsaye kusa da shi tana miqa masa duk abinda zaiyi amfani da shi,yau din ma dai surukuta suke taqi kallonshi,duk da yadda taso ta morewa kallon nashi,sakamakon shigar shadda da yau yayi,duk da cewa ba dinkin tazarce bace amma tayi masifar yi masa kyau,kwalliyar taso ta tafi da ita don dai kawai ta maze,ga kuma kunyar da jiya ya bata,har ya kammala shiryawa tsaf ta miqa masa kofin hadden coffe wanda ta daidaita masa zafinshi,kofin na riqe a hannunshi,tururinsa da qamshinsa na shiga masa hamci,yayin da dukkan idanunsa da tunaninsa suke kacokam a kanta,ya lura sarai shigar tayi mata,amma bai furta mata ko nuna mata ba
"Wai dama haka aure yake?,haka ake ji?" Yake qiyasatawa a ransa,a hakan yasan bata gama sakewa da shi ba,baisan wanne matsayi ta bashi cikin zuciyarta ba baya ga matsayin miji,sarari yake nema wanda zai zauna ya dasa mata zazzafar soyayyarsa cikin zuciyarta,don har yau baisan a wanne rank ta bashi ba,sai data gaji da shirun ta waiwayo ta dubeshi
"Yana sake hucewa,yaya kuma na jiranka"
"Eh jira dama nake ki gama yajin aikin kallona din sai na sha" ya fada yana kai kofin bakinsa,kai ta kautar tana murmushi a boye,a haka sai ka rantse bai iya magana ba sam,amma idan ya yankota a nutse sai ta tsaya maka.
Ta baya taji ya ruqota,ya mannata da jikinsa kansa saitin kunnenta
"Me zan samu?" Ya fadi yana duban wani kwantaccen gashi dake wuyanta mai santsi,shiru tayi tana tunanin me yake nufi,ganin bata ce komai ba sai ya dora
"Zan wuce,kada ki fiya fita wajen gidan nan,coz nasan akwai baqi da yawa da za'a iya yi a kwanakin nan,ok?"kai ta gyada tana jin wani iri babu dadi,sakinta yayi sanda wayarshi ta soma ruri ya duba yaga yaya adam ne,wanda ya gama shirinsa shi kadai yake jira,ya tsammaci ma shi zai rigashi gama shiryawa kamar yadda aka saba,sai gashi wannan karon almustaphan yana son ya makarar da su,juyawa yayi a hankali zaya fice,sai ta biyo bayanshi cikin sanyin jiki tace
"adawo lafiya,Allah ya tsare hanya,a gaishemin da baba"saqon yayi masa dadi,sai yayi kamar zai juyo sai kuma ya fasa,ya amsa da
"ok" yana ficewa,bayanshi tabi da kallo,bata taba ganin mutumin da kayan hausawa suka masa kyau har haka irinsa ba.
Haka kawai take jin ba dadi,wani yanayi na shigarta,qarfafa jikinta tayi ta gyare ko ina tsaf,sannan tayi wanka tare da yin madaidaiciyar kwalliya ta yafa wadataccen mayafi ta fice wajen su ummee,sai data shiga ta gaida,gidan babu laifi ya sake cika,ga jikoki nam sun soma halartar gidan,yaran huda anty farida da 'ya'yan adam yaran kishiyar ni'ima data taho da su,a wajen maamaa ta hadu da ni'iman,fuska sake suka gaisa,hira ta dan gudana tsakaninsj,haka nan ni'ima ta kwantawa sumayya kamar yadda sumayyan ta kwantawa ni'ima,daga bisani tace bari taje wajen ummee,a can ta tuqe wajen ummeen,cikin siyasa ummen ke janta da hira tana son taji ya zaman nasu yake,sosai tayi qoqarin nuna mata komai lafiya yake,hakan ya sake faranta ran ummeen matuqa,sai ga amira da azahar a gidan,ranar sunga tabara,tunda taji labarin yaa man din sun tafi jigawa tace sai ra taho,ya saif ya iya da tabara,haka ya barta amma da sharafin wuni kawai zata dinga ta dawo,wunin baki daya ya zowa sumayya cikin sakewa,hankalinta kwance,babu gilmawar eesha sam,bata san ina tayi ba,bata san meke faruwa ba don haka babu abinda yazo ranta gamenda eeshan,bata koma sashenta ba sai bayan isha'i,kasa zama tayi,baki daya sashen nata yayi mata babu dadi,hakan ya sanya ta koma neman 'yan kwana,da fari kowa qi yayi,sabida sashen ba wajen zuwan kowa bane,daga mai sashen har uwar gidansa ba masu jan jama'a bane,humaida da humaira suka ce sai sunje,hakan ya sanya nadiya da yusra binsu suma,a dakin gadonta na qasa ta saukesu,hakan ya debe mata kewa matuqa,don suna tsaka da hira bacci ya kwashesu.