Sashe 56
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana gab da gidan nasu ta kula da motar wadda ko daga bacci ta tashi zata iya ganeta,motar mukhtar ce,sai ta dauke kai tana qoqarin wucewa cikin gidan,saidai abdallah dake kafadarta wanda ya soma zillo ganin babansa yaqi bada hadin kai,tilas taja tunga ta saukeshi da niyyar ta wuce ta barshi a gun,saidai tana dagowa daga durquson da tayi ta tsinci mukhtar din tsaye a gabanta
"Zan wuce malam" ta fada ranta a hade
"Kiyi haquri malama" ya fada da irin salon muryarta,kicin kicin tayi ganin yadda yake son maida lamarin wasa
"Ka bani hanya da Allah kana batamin lokaci bana son shirme" tsit yayi yana kallonta,ita kanta sai taji kalma ta mata nauyi,don haka ta basar ta hanyar gyara hannun hijabinta
"Sumayya" ya kirata da wani irin salo wanda ada can yake kiranta da shi,kira ke da idan yayi mata take jinsa har cikin jikinta
"Ki yafemim sumayya,a kullum tsahon wata biyar kenan cikin neman yafiyarki nake,idan na kira baki dauka,idan nayi miki saqo baki reply,kiyi haquri ki yafemin,na yadda nayi babban kuskure a rayuwata amma na girbe abinda na shuka ai,na rasaki na tsahon wasu shekaru,ban taba tunani a baya akwai abin zai rabani da ke ba idan ba mutuwa ba,tunda na rabu da ke sumayya ban taba samun nutsuwa ta minti guda ba,Allah ya hukuntani tunda har kin shiga gidan wani sumayya,ki zama mai afuwa da yafiya kamar yadda na sanki nasam halinki a baya,mukhtar dinki ne sumayya bazan daina neman yafiyarki ba matuqar baki yafemim ba har sai ranar da numfashina ya bar gangar jikina...."da sauri ta katseshi don yana neman karya mata zuciya
" don Allah ka bani hanya,na gaji da jin kalaman bakinka"murmushi ya saka yana kada kai
"Shikenam sumayya,idan kinso ma ba zaki sake gani na ba tunda haka kika buqata,amma bazan daina neman afuwarki ba,na barki lafiya"ya fada yana juyawa ya danqawa Abdallah wani dan madaidaicin kwali ya wuce motarsa,sai ta samu kanta da tsayawa cak a gun ta kasa tafiya har ya bar layin,tausayinsa nason rinjayar zuciyarta,tuna wahalhalun da tasha shi ya bijiro mata ya taurarar da zuciyarta,kama hannun abdallah tayi suka shige ciki.
***** ****** ******
Tunda ya bar gidan yaso tilastawa kansa cireta daga zuciyarsa saidai ya gaza hakan,wata sabuwar soyayya da qaunarta ke yawo ko ina cikin jinin jikinsa fiye da irin qaunarta da yake ji a da,sai ya soma komawa wani iri,ko da yaushe cikin tunani,ga wani matsanancin ciwon kai dake matsanta masa wanda ke kwantar da shi,yana mamakin yadda ya kasa haqura da ita,ji yake tamkar idan ya haqura da ita din zai rasa numfashinsa,hakan ya sanya ya shirya da kansa wani dare bayan ya yiwa abbakar waya ya sanar masa ya gayawa malam zaizo zasu tattauna,idan da hali abubakar din ma ya zauna.
Qarfe takwas yana sitring room din malam din dake qofar gidansu,hakan ne ya sanya babu wanda yasan da zuwansa a cikin gidan
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣6⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa yuhazzirikumul lahu nafsah*
*_Allah yana tsoratar da ku game da kansa_*
_______________________________
Duk yadda ta kai ga tunanin duniyar gidanta zata sameta yadda takeso ba haka abun yazo mata ba,komai na neman lalace mata bayan ta tabbatar da cewa tayi nasarar tuge sumayya daga gidan,gaba daya yaranta yadda ta sansu a yanzu ba haka suke ba,baki dayansu kansu a hade yake,qarami na girmama babba,haka babba na tausayin qarami,nuwaira na cikinsu tamkar cikinsu daya da ita,ita ke jagorancin ragamar sauran a matsayinta na babba,duk yadda taso ga sake raba kansu abun yaci tura,duka ne a yanzu basa tsoron dukanta,da tayi abu zasu ce mama babu kyau fa abu kaza,ko daya daga cikin tarbiyyar da sumayya ta dorasu babu wadda suka watsar,a yanzu haka sunfi qaunar zama wajen hajiya akan wurinta,saboda babu abinda ke shiga tsakaninsu sai duka hantara da tsawa saboda basa mata yadda takeso,babu mai bin umarninta cikinsu matuqar ba kan dai dai bane hatta da qaramarsu basma,bata fuskanci sumayya ta gama da rayuwar gidanta ba sai da yaran suka dinga gudunta,idan ranar makaranta ne ba zata sanyasu a idanunta ba sai dare,don idan suka dawo daga boko don kada ta hanasu zuwa uslamiyya gun hajiya suke togewa su shirya su wuce abinsu,ranakun qarshen mako kuwa gun hajiyar suke wuni,idan ka gansu a bangarensu to wani abu suka zo yi suyi su sake komawa.
Lukman kuwa mallakar data yi masa sai ra soma damunta,ba irinta take buqata daga gunsa ba,ya zama kamar irin dolayen nan,komai tace sai yace to,ya zama kamar qaramin yaro,hatta wanka da cin abinci sai tace yayi,sai ya zame mata qarin nauyi cikim rayuwarta,bashi da wani tunani ko kadan,ko wuta tace ya sanya hannunsa ba musu zai tsumbula,abinda ta fuskanta har yau sumayya na maqale cikin zuciyarsa,sau tari zai zauna ya yita kallon qofar dakinta babu qaqqautawa har sai tazo ta koreshi,hakanan ko sunan sumayya yaji an kira koda a hanya ne sai yayi firgigit kamar wanda aka tasa daga bacci,idan kuwa su nuwaira na zaune suna hirarta sai ya zauna daga gefansu yana saurararsu yana tambayarsu kan wasu abubuwa ko sanya musu baki,a kan hirarta da suke zama suyi sai da karima ta tara su ta musu dukan tsiya,ta kulle nuwaira kuma a daki sai da hajiya ta shigo taci mata mutunci ta bude ta tace kada kuma ta sake dukar mata jikoki itace abar a daka ai basu ba,nan ta saki baki ta dinga caccabawa hajiyan magana,bata bu ta kanta ba ta kada kan jikokinta suka fice.
Wannan shine halin da karima ke ciki.
******* ******* ********
Kansa na sunkuye a qasa yana mai jin nauyi da kunyar abinda zai fito daga bakinsa,saidau tilas ya furta din saboda yana mai cike da fata da burin inganta rayuwa ne ta mutum uku,shi abdallahnsa da sumayyarsa,kasa magana yayi har sai da malam ya maimaita fadin ina jinka,yayin da ya abubakar ya gyara zamansa,kawu sulaiman wanda yake qani ga malam ma yazo kawowa malam ziyara suyi hira kamar yadda suka saba kasancewar su biyu suka rage raye a duniya ya tadda zuwan mukhtar din
"Malam,ina mai jin kunyar neman wannan alfarma daga gunku,nasan cewa na muku laifin da dukkan iyaye zasu ji babu dadi a cikin ransu,saidai malam wannan alfarma da zan nema ina fatan zata shafe dukkan wani abu mara kyau da ya faru a baya,sannan zata inganta rayuwar mu baki daya" dan shiru yayi sannan daga bisani ya dora
"Malam,don Allah don annabi ina son ka bani auren sumayya karo na biyu" shiru dakin ya dauka kowa da abinda yake saqawa cikin zuciyarsa,tsawon wani lokaci babu wanda yayi magana,jinjina kai malam yake kafin ya motsa
"Mukhtar,babu shakka kai mutum ne na qwarai,wanda shine babban abinda yaja hankalina karon farko na baka auren sumayya,na sani na shaida cewa dukkan wani abu da ya faru tsakaninku sharri ne da makirci wanda babu wanda bazai iya fadawa cikinsa ba,abu na biyu kuma sakaci da addu'a,na ukunsu rashin game hankali guri guda tare da yin dogon nazari da bincike kan lamura,ammm....mukhtar"
Sai ya dago yana mai amsawa zuciyarsa na gudu daya bayan daya,duk da cewa yana da cikakken fata na cewa zai cimma nasara
"A qa'ida ta addinin musulunci bazawara ita ke da ikon zabawa kanta miji,saidai idan har anga tana neman jefa kanta wajen wanda bai cancanta ba bayan ga wanda ya cancanta a gefe,kada ka manta sumayya bazawara ce ita ke sa ikon zabawa kanta miji duk da nasan cewa ko a yanzu nayi mata zaben miji ba zata musanta min ba,to amma dai zan bata damarta,mukhtar,bazan hanaka neman sumayya ba,amma kadai zan amince ne idan ta yarda da aurenka".
Shiru yayi kafin daga bisani yace
" malam,na gode da wannan alfarmar da ka yimin,amma ina mai neman alfarma ta gaba"
"Uhmmm,ina jinka"
"Malam,don girman Allah ina neman alfarma a gunka da ka karbi sadakin sumayya daga gurina,nayi maka alqawari tsakanina da ubangiji na matuqar sumayya taqi aminta da ni zan karbi sadakina zan haqura,na maka wannan alqawarin" shiru ne ya sake biyowa baya,kowa da abinda yake nazarta qasan ransa,malam na gudun shiga haqqin sumayya,yayin da ya abbakar ke tunanin tabbas dama ce wannan,don shi kadai yake iya fahimtar yaren sumayya,saidai ya hango alamun rashin amincewa qarara a fuskar malam,yayin da mukhtar ke duqe yana mai cike da fatan samun nasara,ya abbakar ne yayi saurin yankan hanzarin malam din
"Malam,ina ga ka bawa mukhtar wannan damar,domin ni na shaida cewa sumayya na son mukhtar,hakanan na tabbata ba za'ayi nadamar karbar sadakin nan ba in sha Allahu gyara ne zai tabbata a tsakaninsu" kusan abinda kawu sulaiman ke ayyanawa cikin ransa kenan,don ko shi yana tausayin sumayya da abdallah,saboda haka ya ari bakin malam ya ci masa albasa
"Kaje muntari,an baka wannan damar,kaje ka kawo sadakin amma tare da manyanka zaka dawo". Jinsa yayi kamar ba a duniya yake ba,godiya ma rasa wacce iriya zaiyi,ya tabbata yana jin karsashin samun nasara da shawo kan sumayyansa.
**************
Kasancewar juma'a ce ta zamo washegarin ranar,qarfe hudu bayan sallar la'asar mukhtar ya iso gidan shida kawunsa wato mahaifin abdur rahman da kuma baffansa wanda yake wa ne ga innarsu da qanin innar yasu su hudu kenan,kawu sulaiman da babban dansa sai yaya abubakar su suka sake karbar sadakin sumayya karo na biyu,wanda ita wadda ma ake batun sam batasan ana yi ba,don a lokacin ta tafi kitso,ta dawo dai ta tadda mutane cikin sitting room din malam,saidai batasan ko su waye ba tunda bata shiga ciki ba cikin gida ta zarce,bayan malam din ya sallami kowa ya shigo cikin gida ya tadda mama ya buqaci ganinta sannan ya sanar mata tare sa gaya mata baya son ta sanrwa kowa har sai sun hada kansu da kansu,to ita din macace,kuna tasan burin kowacce mace ta zauna da uban 'ya'yanga,hakanan kowa ya san nagarta da kyawun halayen mukhtar tun kafin wannan qaddarar ta afkowa rayuwarsu.
*ZAINAB*
"Zan wuce malam" ta fada ranta a hade
"Kiyi haquri malama" ya fada da irin salon muryarta,kicin kicin tayi ganin yadda yake son maida lamarin wasa
"Ka bani hanya da Allah kana batamin lokaci bana son shirme" tsit yayi yana kallonta,ita kanta sai taji kalma ta mata nauyi,don haka ta basar ta hanyar gyara hannun hijabinta
"Sumayya" ya kirata da wani irin salo wanda ada can yake kiranta da shi,kira ke da idan yayi mata take jinsa har cikin jikinta
"Ki yafemim sumayya,a kullum tsahon wata biyar kenan cikin neman yafiyarki nake,idan na kira baki dauka,idan nayi miki saqo baki reply,kiyi haquri ki yafemin,na yadda nayi babban kuskure a rayuwata amma na girbe abinda na shuka ai,na rasaki na tsahon wasu shekaru,ban taba tunani a baya akwai abin zai rabani da ke ba idan ba mutuwa ba,tunda na rabu da ke sumayya ban taba samun nutsuwa ta minti guda ba,Allah ya hukuntani tunda har kin shiga gidan wani sumayya,ki zama mai afuwa da yafiya kamar yadda na sanki nasam halinki a baya,mukhtar dinki ne sumayya bazan daina neman yafiyarki ba matuqar baki yafemim ba har sai ranar da numfashina ya bar gangar jikina...."da sauri ta katseshi don yana neman karya mata zuciya
" don Allah ka bani hanya,na gaji da jin kalaman bakinka"murmushi ya saka yana kada kai
"Shikenam sumayya,idan kinso ma ba zaki sake gani na ba tunda haka kika buqata,amma bazan daina neman afuwarki ba,na barki lafiya"ya fada yana juyawa ya danqawa Abdallah wani dan madaidaicin kwali ya wuce motarsa,sai ta samu kanta da tsayawa cak a gun ta kasa tafiya har ya bar layin,tausayinsa nason rinjayar zuciyarta,tuna wahalhalun da tasha shi ya bijiro mata ya taurarar da zuciyarta,kama hannun abdallah tayi suka shige ciki.
***** ****** ******
Tunda ya bar gidan yaso tilastawa kansa cireta daga zuciyarsa saidai ya gaza hakan,wata sabuwar soyayya da qaunarta ke yawo ko ina cikin jinin jikinsa fiye da irin qaunarta da yake ji a da,sai ya soma komawa wani iri,ko da yaushe cikin tunani,ga wani matsanancin ciwon kai dake matsanta masa wanda ke kwantar da shi,yana mamakin yadda ya kasa haqura da ita,ji yake tamkar idan ya haqura da ita din zai rasa numfashinsa,hakan ya sanya ya shirya da kansa wani dare bayan ya yiwa abbakar waya ya sanar masa ya gayawa malam zaizo zasu tattauna,idan da hali abubakar din ma ya zauna.
Qarfe takwas yana sitring room din malam din dake qofar gidansu,hakan ne ya sanya babu wanda yasan da zuwansa a cikin gidan
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣6⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wa yuhazzirikumul lahu nafsah*
*_Allah yana tsoratar da ku game da kansa_*
_______________________________
Duk yadda ta kai ga tunanin duniyar gidanta zata sameta yadda takeso ba haka abun yazo mata ba,komai na neman lalace mata bayan ta tabbatar da cewa tayi nasarar tuge sumayya daga gidan,gaba daya yaranta yadda ta sansu a yanzu ba haka suke ba,baki dayansu kansu a hade yake,qarami na girmama babba,haka babba na tausayin qarami,nuwaira na cikinsu tamkar cikinsu daya da ita,ita ke jagorancin ragamar sauran a matsayinta na babba,duk yadda taso ga sake raba kansu abun yaci tura,duka ne a yanzu basa tsoron dukanta,da tayi abu zasu ce mama babu kyau fa abu kaza,ko daya daga cikin tarbiyyar da sumayya ta dorasu babu wadda suka watsar,a yanzu haka sunfi qaunar zama wajen hajiya akan wurinta,saboda babu abinda ke shiga tsakaninsu sai duka hantara da tsawa saboda basa mata yadda takeso,babu mai bin umarninta cikinsu matuqar ba kan dai dai bane hatta da qaramarsu basma,bata fuskanci sumayya ta gama da rayuwar gidanta ba sai da yaran suka dinga gudunta,idan ranar makaranta ne ba zata sanyasu a idanunta ba sai dare,don idan suka dawo daga boko don kada ta hanasu zuwa uslamiyya gun hajiya suke togewa su shirya su wuce abinsu,ranakun qarshen mako kuwa gun hajiyar suke wuni,idan ka gansu a bangarensu to wani abu suka zo yi suyi su sake komawa.
Lukman kuwa mallakar data yi masa sai ra soma damunta,ba irinta take buqata daga gunsa ba,ya zama kamar irin dolayen nan,komai tace sai yace to,ya zama kamar qaramin yaro,hatta wanka da cin abinci sai tace yayi,sai ya zame mata qarin nauyi cikim rayuwarta,bashi da wani tunani ko kadan,ko wuta tace ya sanya hannunsa ba musu zai tsumbula,abinda ta fuskanta har yau sumayya na maqale cikin zuciyarsa,sau tari zai zauna ya yita kallon qofar dakinta babu qaqqautawa har sai tazo ta koreshi,hakanan ko sunan sumayya yaji an kira koda a hanya ne sai yayi firgigit kamar wanda aka tasa daga bacci,idan kuwa su nuwaira na zaune suna hirarta sai ya zauna daga gefansu yana saurararsu yana tambayarsu kan wasu abubuwa ko sanya musu baki,a kan hirarta da suke zama suyi sai da karima ta tara su ta musu dukan tsiya,ta kulle nuwaira kuma a daki sai da hajiya ta shigo taci mata mutunci ta bude ta tace kada kuma ta sake dukar mata jikoki itace abar a daka ai basu ba,nan ta saki baki ta dinga caccabawa hajiyan magana,bata bu ta kanta ba ta kada kan jikokinta suka fice.
Wannan shine halin da karima ke ciki.
******* ******* ********
Kansa na sunkuye a qasa yana mai jin nauyi da kunyar abinda zai fito daga bakinsa,saidau tilas ya furta din saboda yana mai cike da fata da burin inganta rayuwa ne ta mutum uku,shi abdallahnsa da sumayyarsa,kasa magana yayi har sai da malam ya maimaita fadin ina jinka,yayin da ya abubakar ya gyara zamansa,kawu sulaiman wanda yake qani ga malam ma yazo kawowa malam ziyara suyi hira kamar yadda suka saba kasancewar su biyu suka rage raye a duniya ya tadda zuwan mukhtar din
"Malam,ina mai jin kunyar neman wannan alfarma daga gunku,nasan cewa na muku laifin da dukkan iyaye zasu ji babu dadi a cikin ransu,saidai malam wannan alfarma da zan nema ina fatan zata shafe dukkan wani abu mara kyau da ya faru a baya,sannan zata inganta rayuwar mu baki daya" dan shiru yayi sannan daga bisani ya dora
"Malam,don Allah don annabi ina son ka bani auren sumayya karo na biyu" shiru dakin ya dauka kowa da abinda yake saqawa cikin zuciyarsa,tsawon wani lokaci babu wanda yayi magana,jinjina kai malam yake kafin ya motsa
"Mukhtar,babu shakka kai mutum ne na qwarai,wanda shine babban abinda yaja hankalina karon farko na baka auren sumayya,na sani na shaida cewa dukkan wani abu da ya faru tsakaninku sharri ne da makirci wanda babu wanda bazai iya fadawa cikinsa ba,abu na biyu kuma sakaci da addu'a,na ukunsu rashin game hankali guri guda tare da yin dogon nazari da bincike kan lamura,ammm....mukhtar"
Sai ya dago yana mai amsawa zuciyarsa na gudu daya bayan daya,duk da cewa yana da cikakken fata na cewa zai cimma nasara
"A qa'ida ta addinin musulunci bazawara ita ke da ikon zabawa kanta miji,saidai idan har anga tana neman jefa kanta wajen wanda bai cancanta ba bayan ga wanda ya cancanta a gefe,kada ka manta sumayya bazawara ce ita ke sa ikon zabawa kanta miji duk da nasan cewa ko a yanzu nayi mata zaben miji ba zata musanta min ba,to amma dai zan bata damarta,mukhtar,bazan hanaka neman sumayya ba,amma kadai zan amince ne idan ta yarda da aurenka".
Shiru yayi kafin daga bisani yace
" malam,na gode da wannan alfarmar da ka yimin,amma ina mai neman alfarma ta gaba"
"Uhmmm,ina jinka"
"Malam,don girman Allah ina neman alfarma a gunka da ka karbi sadakin sumayya daga gurina,nayi maka alqawari tsakanina da ubangiji na matuqar sumayya taqi aminta da ni zan karbi sadakina zan haqura,na maka wannan alqawarin" shiru ne ya sake biyowa baya,kowa da abinda yake nazarta qasan ransa,malam na gudun shiga haqqin sumayya,yayin da ya abbakar ke tunanin tabbas dama ce wannan,don shi kadai yake iya fahimtar yaren sumayya,saidai ya hango alamun rashin amincewa qarara a fuskar malam,yayin da mukhtar ke duqe yana mai cike da fatan samun nasara,ya abbakar ne yayi saurin yankan hanzarin malam din
"Malam,ina ga ka bawa mukhtar wannan damar,domin ni na shaida cewa sumayya na son mukhtar,hakanan na tabbata ba za'ayi nadamar karbar sadakin nan ba in sha Allahu gyara ne zai tabbata a tsakaninsu" kusan abinda kawu sulaiman ke ayyanawa cikin ransa kenan,don ko shi yana tausayin sumayya da abdallah,saboda haka ya ari bakin malam ya ci masa albasa
"Kaje muntari,an baka wannan damar,kaje ka kawo sadakin amma tare da manyanka zaka dawo". Jinsa yayi kamar ba a duniya yake ba,godiya ma rasa wacce iriya zaiyi,ya tabbata yana jin karsashin samun nasara da shawo kan sumayyansa.
**************
Kasancewar juma'a ce ta zamo washegarin ranar,qarfe hudu bayan sallar la'asar mukhtar ya iso gidan shida kawunsa wato mahaifin abdur rahman da kuma baffansa wanda yake wa ne ga innarsu da qanin innar yasu su hudu kenan,kawu sulaiman da babban dansa sai yaya abubakar su suka sake karbar sadakin sumayya karo na biyu,wanda ita wadda ma ake batun sam batasan ana yi ba,don a lokacin ta tafi kitso,ta dawo dai ta tadda mutane cikin sitting room din malam,saidai batasan ko su waye ba tunda bata shiga ciki ba cikin gida ta zarce,bayan malam din ya sallami kowa ya shigo cikin gida ya tadda mama ya buqaci ganinta sannan ya sanar mata tare sa gaya mata baya son ta sanrwa kowa har sai sun hada kansu da kansu,to ita din macace,kuna tasan burin kowacce mace ta zauna da uban 'ya'yanga,hakanan kowa ya san nagarta da kyawun halayen mukhtar tun kafin wannan qaddarar ta afkowa rayuwarsu.
*ZAINAB*