← Book details Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 102 OF 226

Sashe 102

Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

A hankali ya miqe yana shafa sumar kanshi,jin maganansu yake kamar a tsakiyan kanshi kasancewar bai son hayaniya,baabaan ya fuskanci me yake son fadi,saboda haka yace
"Shikenan,kana iya tafiya" juyawa yai a hankali ya fice a falon fuska a daure kamar ko yaushe,eesha ji take kamar ta bishi ta rungumeshi,saboda yadda kullum kwanan duniya yake sake tafiya da ita,yayin da sumayya kanta ke qasa tana wasa da yatsunta zuciyarta na bugawa,amira ta bishi da kallo kamar yadda baaba shima ya bishi da kallo,shiru yaci gaba da ratsa falon har ya fice din sannan baabaa ya dauke idanuwansa daga kanshi ya maida kansu,ya dubi amira
"Aishatu ta rakaki amira kuje ku amso min saqo wajen ummenku"
"To abba" ta fada tana miqewa,tasan babanta sosai,hakan ya sanya bata ce sumayya ta taso na,tunda taga haka tasan akwai manufarsa na aikensu su biyu,baki daya taji wani nauyi ya sake kamata bayan fitar tasu,falon yayi shiru ta kasa motsawa sai kanta dake qasa har yanzu
"Mamana,ki saki jiki mana,nima fa babanki ne ko ba haka bane" murmushi tayi
"Haka ne abba" shiru ya sake ratsa falon na wasu sakanni kafin ta sake jin muryarsa
"Mama na,wata alfarma nakeson na roqeki,saidai ina jin nauyin haka" mamaki ya kamata,ita din wace?,wacce alfarma babban mutum kamar baabaa prof din zai nema daga gareta,bayan ita din ba kowa bace,bata kuma mallaki komai ba
"Baabaa,yanzu kace kai abbana ne,kuma na yarda haka ne,me yasa uba zaiji nauyin bawa diyarsa umarni" sosai wani irin qima da darajarta ya qaru a idanuwanshi,ya jima baiga nutsuwa da hankali tattare da yarinya mai makamancin shekaru irin nata ba,nutsuwarta da kaifin hankalinta shine abu na farko daya fara bashi mamaki tattare da ita,tana da wani irin dattako kunya nutsuwa da ganin darajar manya,wanda zaiyi wuya a wannan zamani ka samu mace kamarta da wannan qualities din
"Allah yayi miki albarka maman,haqiqa iyayenki sunyi nasara wajen tarbiyyarki,sun rabauta da diya ta qwarai,mamana.....kinga yayankun nan da ya fice yanzu?" Gabanta ya buga,sai ta kasa daga kai ta kalli baabaan,Allah yasa ba wani sharrin yayi mata wajen baban ba,kai kawai ta kada
"Mamana,zaki taimaka min ki taimaka masa wajen inganta rayuwarsa?" Duburburcewa tunanunta yayi,sam bata gano me baban ke nufi ba,inganta rayuwarsa kamar yaya,ya manta bata da komai ne qarqashin wasu take itama,duk yadda taso ta fassara maganar tsakaninta da qwaqwalwarta ta gaza gano ainihin ma'anar maganar,har rudun hakan ya bayyana saman fuskarta.

Murmushi baaban ya saki,ya yadda har yau ita dinma akwai sauran quruciya tattare da ita,baison rudata,saboda haka yace
"Baki fahimci baaba ko,shikenan,tashi kije kuci gaba da sabgoginku,idan kika fahimci ma'anar maganar ina son ganinki a lokacin,amma fa kada ki zurfafa tunani,kune qawayen amarya,kusha bikinku kinji mamana,Allah yayi miki albarka"
"Amin baabaa,na gode" ta fada tana miqewa,hakanan taji jikinta yayi wani mugun sanyi,rashin jin dadin kasa fahintar maganar baban ce har ya dago haka ko kuwa mene?.

Naso yafi haka but am busy fans.

#mrs muhammad ce

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:51] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖

*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)

7⃣1⃣

*Bismillahir rahmanir rahim*

Allah S W T yana cewa

*"DUK INDA KUKE SAI MUTUWA TA RUSKEKU"*

Allah kasa mu cika da imani

____________________________________

     Qarfe biyar na yammacin ranar baki daya gidan ya sake dinkewa da jama'a saboda shirin fara gabatar da kamun amarya,sumayya na tare da amiran duk inda ta sanya qafarta sai ta janyota,kamar yanzu da suke can uwar dakan anty maamaa suna shiryawa,daga sumayyan sai amira sai humaida da humaira,amiran akewa kwalliya an kusa kammala mata,tayi kyau qwarai da gaske cikin wani irin yadin saqi na fulani mai azqbar kyau da daukan hankali,saqin fulani je wanda aka zamanantar da shi da kayan ado dana qawa,maroon ne sosai da yarfin kwalliyar golden a jiki,walwali kawai take zubawa,ta lura da yadda sumayyan ke yawaita shiru,saka bakinta cikim hirarta yayu qaranci sosai,hannu ta sanya ta tabota,ta daga kai ta dubeta tana murmushi,da hannu ta yi mata alamar lafiya,sai kawai ta girgiza kai ba tare data ce komai ba,duk yadda taso barin zancan da baabaa yayi mata abun yaqi barin kwanyarta,zuciyarta ta nace da son gano ainihin me maganar tashi ke nufi
"An gama min,saura ke" inji amira tana isa bakin mudubi tana duba kwalliyar tata,kai ta kada
"Powder kawai za'a shafa min a jamin jagira sun isa" idanu amira ga watso mata
"Bazaiyiwu ba wallahi,kina babbar qawar amarya?"
"Ki barni ayimin hakan don Allah,naga dai yau aka fara abin nan ko?,gaba a yimin" ta fada tana zama gaban mai kwalliyat,dariya humaida ta saka,yanayi da halayen sumayyan ke qara bata sha'awa,sam bata da rawar kai ko iyayi irin na 'yammata.

       Duk da cewa ba wani kwalliyar azo a gani aka mata ba amma tashi daya ta sauya,tayi wani sihirtaccen kyau mai sanyi wanda babu hayaniya a cikinshi,su kansu sai da suka yaba,biyar da kwata kiran ango saifudden ya shigo wayarta,yake sanar mata sun iso,da yake tare za'a kama su shi da ita,falon anty maamaan suka sauko sannan suka hadu sa sauran qawaye da 'yan uwa suka fito.

       Qyashi da hassada fal ran eesha,duk yadda taso taga ta wuce sumayyan a kwalliya abun yacu tura,ira kadai ta tsone mata duk taton 'yammatan nan,saboda kaf cikinsu bata ga wadda tayi ya kyawunta ba,duk da yake akwai wadanda suka saka suturar da suka fi nata kayan qaawa da tsada,amma ba'a nan take ba wai aj dannewa bodari kai,abinda bata sani ba baki daya sumayyan jinta take a wani mugun takure,karo na farko a rayuwarta data taba shiga makamanciyar wannan,qememe amira ta hanata sanya mayafi sai ratayashi kawai tayi gefan kafadarta guda daya,kayan sunyi masifar amsarta kamar wanda ya saqa su ya saqasu ne musamman saboda ita,takalmin ne kawai ya gagareta tafiya,subaleshi tayi ta nemi plat cikin na amiran ta saka,a ranar tayi adon gashinta wanda yasha gyara aka fito mata da shi cikin daurinta sai sheqi sa walwali yake,ta saje cikin 'yammatan amaryar har ta zama kamar wata fitila ta daban cikinsu.

        Bata gane wautar data tafka ba sai bayan da suka iso gurin taron,wanda a cikin gidan aka shirya kujeru rumfuna da decoration na alfarma da kece raini,saika rantse da Allah wani event center ne mai tsada aka kama,ita ke riqe da amiran amma sai ta kusa faduwa saboda yadda idanuwa suka mata caaa,idanunta ta lumshe tana kiran sunayen Allah,ko ina abokan ango ne gogaggu kuma wayayyu tsaitsaye suna jira a qaraso musu da amaryar,hannun anty huda ta danqa ta sannan ta juya har tana hardewa saboda ido ta juya,su'adah na tsaye gefan huda din,india ta tafi baki daya,sari ne a jikinta wanda ya amsa sunansa,sak irin dinki 'yan qasar hindun ne jikinya skert da 'yar fingilar riga,sai mayafin kayan a jikin skert din ta nannade jikinta,yayin da kanta ke a bude kamar nasu,sai gashin dokin da aka dinkeshi da ainihin nata ya tashi tamkar nata,ta rabashi kafadar hagu da dama kakar yadda 'yan qasar hindun keyi.

     Tana juyawa suka ci karo da anty farida umman husna,bakinta a washe take duban sumayya
"Wai wai,kunyi wuyar gani,ko diyarki baku hadu ba" murmushi sosai kan fuskarta cikin girmamawa ta gaida anty farida sanan ta wuce ummee dake cikin gida bata fito ba ta aikota wajen amiran.

       Wayarta dake hannunta ta dauki vibration sanda amarya ta samu zama a gurbinta ita da angonta,sunan nafisa ta gani,mamaki ya cikata ganin number dinta ce ta nijeria,qarar lasifiqan wajen bazai barta taji ba,hakan ya sanya ta soma takawa don barin wajen tana duban kiran,can baya inda zata iya jin ta ta tsaya ta soma lalubarta saboda kiran ya riga da ya katse
"Am at home sisi" idanu ta fiddo waje
"Da gaske?"
"Suprise wlh naso baki,shigo gidan anty ki shigo dani yau traditional setting na amira ina lissafe dama"
"Wayyo sis,gani nan" ta fada cikin zumudi da murna ta kashe wayar,daidai sanda kida ya soma tashi daga inda ake gabatar da bikin,tsalle ta dan saki kadan farinciki fak ranta
"Yi a hankali gimbiya kada ki fadi ki batan kwalliyar" abinda taji an ambata kenan,da sauri ta waiwayo,alqasim ne tsaye sanye da shadda ya kawo hula gaban goshinsa yana qare mata kallo yana murmushi,daidaita natsuwarta tayi sannan ta juya da niyyar ci gaba da tafiya,saurin shan gabanta yayi,ya wani karyar da kai
"Haba sumayya,ko gaisawa i kya tsaya muyi ko?" shiru tayi tana dubansa ba tare data ce komai ba,ji take kawai zai bata mata lokaci ne,bata da buqatar wani abu a yanzu,tana cewa ta gama da babinsa,tunda tuni ta gaya masa ita din ba budurwa bace bare ya saka ran zata biye masa,idanunta tarufe tare da yin banza da shi,tana jinshi yana magana ci kanka bata ce masa ba.

       Tunda suka fara tashin kidan ya tashi ya shiga bathroom ya sake wanka,jin kidan yake kamar a tsakiyar kanshi,duk wani abu da zai zama tamkar hayaniya bai qaunarsa,ko qwaqwaran motsi ne ya fiya yawa yanzun zai dameshi,sau tari babban wansi adam kance
"Kai ko mustapha kamar mai aljanu,koyaya motsi yake sai ya dameka" amma hakan bai rasa nasaba da ciwon kan da yake fama da shi tsawon shekaru,wanda idan ya tayar masa baya masa ta dadi.
Chapter 102 · 0% Book details