Sashe 123
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Karon farko da sumayyan ta taba shigarshi,falo ne dan gaske,wanda ya mallaki duk wasu kayan alfarma,baki daya kwalliyar falon ta da duk abinda aka zuba mishi na sarauta ne,kama daga royal chairs zuwa fentin falon,yayi matuqar burge sumayyan ba kadan ba,ummen ma zaune kan daya cikin kujerun falon tana irga sabbabin kudi wanda suke daure a rafarsu,ita da wasu mata ne wadanda kusan cousin dinta ne da suka taso tare tun zamanin 'yammatanci,qarasawa amira tayi ta kwantar da abdallah kan daya cikin kujerun,ummee ta dubeshi tana musu sannu da qarasowa ita da sauran 'yan dakin,a ladabce sumayya ta qarasa gabanta ta duqa tana gaidata,ta amsa fuska sake tana cewa
"Amira ta hanaki sakat ko sai data daukoki" murmushi tayi kawai amiran tace
"Ummee ba'a shiga tsakaninmu"
"Au ai dama itaku amira" ta fada tana kiran daya daga cikin ma'aikatanta ta wayar hannu tana tambayarta an gama gyara dakin da tace,sai data gama wayar ta dubi amira
"Kije an gama gyara muku dakin,saiki sanya a kawo muku abinci,ki duba abinda kuke da buqata ki kira mama uwani ki sanar mata,su ummu salma ma ina zaton suna dakin tun dazun suke qorafin rashin dawowarki gashi gobe kamu"
"To ummee na" amiran ta fada tana miqewa
"Muje,ummee idan abdallah ya tashi ki bada shi a kawo mana shi" ta fada tana nuna abdallahn dake kwance yana baccinsa lakadan,kai ummim ta daga don bata son yin magana ta sake bata a lissafin.
Dakina babba sosai wanda ya babu komai cikinsa sai carfet da aka malale shi da shi,katifune saman carfet din ko ina aka kwakwkwantar,yayin da aka lullube kowacce katifa da zanin gado abun rufa da filo qwaya daya alamar kowacce ta kwanciyar mutum guda ce,sai toilet qwaya biyu cikin dakim,da qaton madubi da ya kusa cinye rabin bango,mutum biyar suka taras a dakin,wasunsu na hira wasu na cin abinci,shewa suka sanya da ganin shigowar amaryar,kowacce da abinda zata fadi,nan suka zube aka gaisa suna ci gaba da surutaj,itakam sumayya na gefe tana kallonsu,rayuwar wayewa kawai ake a wannan familyn,kowacce ka gani tana ji da wayewa kyau da arziqin gidansu,akwai alama dake nuna suna da zumunci da kara,sannan akwai sabo da fahimtar juna tsakaninsh,wanda hakan baya rasa nasaba da yadda baabaa prof ya hadasu baki daya ya rungume kowa,duk sallah babba da qarama duk 'ya'yan 'yan uwan na gidansa,baya banbantawa da nashi dangin dana matansa,shi ya sanya kowa yasan kowa,'yammata ne hadaddu wannan na wace wancan ta fada a ranta tana murmushi.
Agogon fata na kamfanin gucci purple dake daure a hannunta ta duba ganin ruwan ya tsagaita sai yayyafi wanda take iya gani ta window din dakin albarkacin hasken lanatarkin da yake tarwai kowane lungu da saqo na gidan
"Zan wuce fa amira" inji sumayya ganin yadda amiran ta bararraje tana kwasar hira,duka sai hankalin su ya dawo kanta har taji nauyin yadda kowa ya dora mata idonshi
"Wasa fa kike amirah,kin manta alqawarinmu,ai ga gun kwanaki nan har na bar gidan nan" sai ta karyar da wuya tana murmushi
"Amma dai ai kya bari naje naga anty ko?"
"Eh,wannan kuma,kuma ai ban ma gama ganinki ba,muje part din anty maamaa akwai abinda zaki gani idan kin dawo na nuna miki sauran" ta fada tana miqewa,itama tashin tayi suka fito,har sun kai qofa tace
"One minute don Allah sis,bari na dauko kayan waccan jarababbar na kai mata,Allah yasa ya musty bai nan" kafin tace komai har ta juya da sauri ta koma,tsayawa tayi tana jiranta gabanta na faduwa,tana addu'an kada Allah ya sa tace sai ta rakatan,don gaskiya ba abinda zai hanata ce mata ba zata ba.
Tana shiga ummu salma tace da ita
"Amira wai ina kika samu wannan babe din haka mai shegen class,wallahi tamun,ta burgeni da ganinta akwai nutsuwa"
"Ga kyau,muryarta ce ni kuma ta burgeni" inji hafsat,dariya suka bata,dukkansu 'ya'yan yar ummee ne,tasu ta bala'in zuwa daya da amira saboda halayyarsu kusan daya ce,ba ruwansu suna da matuqar kirki
"Nan fa gidan anty dije wadda ta muku fried rice da sunan hanan,a nan take"
"Masha Allah wallahi tayi"
"Ai baku ma san tayi ba sai mu da muka je gidansu...." Eesha da hassada ta cikata tace
"Me tayi,mr suke da shi a gidan nasu" amira wadda har ta sanya qafarta zata fita ta fasa ta dawo jin abinda eesham tace,dama tana lura da take takenta akan sumayya,wadda bata ga ita sumayyan abinda ta yi mata ko ta tsareta mata ba
"Basu da komai,amma suna da rufin asiri,suna da wadatar zuci,basu taba kuma roqon wani ba,baya ga haka suna da karamci kyautatawa da girmama baqo,wadan nan abubuwa sun basu komai na rayuwa koda basu da shi din" inji amira ranta a bace sannan ta juya ta fita ranta a bace,humaida ce wadda itama ke jin haushin abinda eeshan keyi ta dora
"Arziqi ba kudi bane eesha,wadatar zuci sanin darajar kai,mutunci yakana da karamci sune arziqin,kana da cin yau kana fa na gobe jibi wata ko shekara ma,kana sanya suturarka ta mutunci,baka taba roqa a baka ba,baka tashi ka rasa abin kaiwa baka me kake nema?"
"Kinga malama,ni ba wani nace mata ba da zaku isheni da dogon wa'azi,ha'an..." Ta qarashe tana jan tsaki,caaa suka mata sun fita yawa ala tilas tayi shiru.
A inda ta barta a nan ta taras da ita,suka ci gaba da takawa ba tare data nuna wa sumayyan akwai wani abu ba,bangaren anty maamaa suka soma shiga,itama bangaren nata masha Allah da mutane,suka gaisa sannan taja hannunta suka tsallake zuwa kitchen dinta,suna shiga tana yunqurin fitowa hannunta dauke da tray wanda aka jera tangaran mai garai garai guda daya wanda ke dauke da hadin salad mai kyau,sai wata qaramar butar shayi irin ta larabawa da cups dinta wanda ke dauke da baqin shayi wanda yasha kayan qamshi iri iri,su'ad ce,fuskar nan a hade tana faman kumburi,ko kunyar idon mutane bata ji,ta zama baturiyar qarfi da yaji,sanye take da dogon wando wanda ya kama jikinta da t.shirt mai gajeran hannu,kanta babu dankwali sai uban qarin gashi wanda aka dasa shi kamar nata na ainihi,ta sanya ribbom ta kameshi,takalmin qafarta kuwa irin mai igiyar nan je,wanda tsininsa ba kawai abun kallo ne,amma akace sabo da yi gawa da gatsine,da yake ta saba tafiya da abunta sam bai dameta ba,hannyenta kuwa farce ne wanda tasha nail polish,gefe suka janye bata ko kallesu ba ta wuce abinta,da kallo amira ta bita tana tabe baki kafin ta maida kallonta ga anty maamaa
"Kumburin banza kawai,shi wanda kike ma kumburin ma baisan kina yi ba,ba kuma ki isa kiyi masa a gabanshi ba,abincin ba bake zaki girki ba ki karba ki kai masa yaci kina baqinciki kamar da kudinki aka sarrafa,wallahi ni yanzu baiken ya musty ma nake gani,kana aure amma kamar ba magidanci ba,babu wani ci gaba da ka samu ko sauyi dangane da tsohuwar rayuwarka" daquwa anty maaman ta jefeta da ita tana fadin
"Sau nawa zan miki magana kan dauke ido daga rayuwarsu?,ke ke zaune da ita?,ko kinga ta kulaki sansa zata fita" shigin shagwaba amiran ke kumbure kumbure tana fadin
"Duk ku kuke sake bata su wallahi,ni da ganin wannan takacin gwara kayi aurenka ma kayi gaba a barku da su" dariya ma ta baiwa anty maaman sai ta dauke kanta tana duban sumayyan
"Qaraso amiran umman khalipha mu gaisa ki qyale wannan tuburarriyar qawar taki,rana iwar haka dai naga wanda zata yi mawa" dariya sumayyan ta saka itama tana qarasowa inda anty maman take,a ladabce ta gaidata tana tambayar yadda ta baro mutanan gidan,sai da suka gama gaisawa sannan tace
"Anty mama,bedroom dinki na bude,zamuga wadan nam kayan" kai ta kada mata suka juya suka fice.
Har bedroom din ta dangana da ita,aljannar duniya sumayya ta kira dakin,cupboard din antyn ta bude ta jawo wata akwati ta ajjiye gaban sumayyan,ta sake janyo wata ta ajjiye sannan ta fara hudewa tana fadin
"Ga kayan da zaki saka na biki baki daya,komai da komai,sarqa kawai zaki buqata bansan choice dinki ba" baki kawai sumayyan ta sake tana kallonta,ta soma ware mata wanda zata sanya gobe kamu,wani dandatsetsen lace ne brown mai yarfin milk wanda aka yiwa dinkin fitted gown,rigar ta dinku iyaka,sai takalmi milk na companyn vinci wanda ke da tsini dunduniya,sake dago wata doguwar riga tayi wadda ta tafi da imaninta,ire iren rigunan da baabaa ya basu da salla ita da laila mai dauke da tambarin companyn MM,itama da takalminta ruwan kwalliyar duwatsun dake jikin rigar tace wannan ta jibi ce ranar arabian night,sake janyo wani shegen yadi tayi wanda bata tantance wanne ba,baqi ne baki dayansa an masa ado da milk din zare tsalli tsalli da milk din qulalai a jiki,shima fitted gown ce,har tafi ta farko fitinuwa,sai wani shegen hill shoes mai igiyoyi ruwan adon jikin yadin da jaka purse mahadin kayan ga
"ankon dinner dinki" amira ta fada tana murmushi,rasa bakin magana kawai tayi tana duban amira,dariya ta sanya sanda ra motsa zata yi magana
"Wallahi idan kika ce wani abu sai mun bata,baabaa ne duka ya bada yace na zabi na dinkawa babbar qawata" kai kawai ta dinga kadawa kafin ta furta kalaman godiya,kunnuwanta ta tasihe da nufin bata son ji.
Daya akwatin kuwa baki daya kayan amarya ne da zata yi fitar biki,fadin irin kyawunsu ma bata baki ne,sai data daga mata su daya bayan daya sannan ta rufe ta maida ma'ajiyarsu tana cewa
"A nan zamu dinga shiryawa,don haka anan zamu bar kayanmu,sai muje kiga lefe dama baki gani ba" dariya tayi
"So kike dai dare yamin banje naga anty ba,ai basai na gani ba amira".
" shikenan,muje ki rakani na miqawa waccan kayanta,sai na rakaki qofa kije ki dawi din"fuska ta narke,ta langabe kai duk don amiran ta haqura da wannan rakiya
"Habbaaa amira,muje dai ki wuce ki kai mata ni kuma na wuce gida"
"Ke kika ce sai na amso mata dinkin ina zaman zamana,saboda haka dole ki rakani" tayi maganar tana gyara nadin mayafinta,miqewa tayi jikinta babu qwari tabi bayan amiran suka fice.
"Amira ta hanaki sakat ko sai data daukoki" murmushi tayi kawai amiran tace
"Ummee ba'a shiga tsakaninmu"
"Au ai dama itaku amira" ta fada tana kiran daya daga cikin ma'aikatanta ta wayar hannu tana tambayarta an gama gyara dakin da tace,sai data gama wayar ta dubi amira
"Kije an gama gyara muku dakin,saiki sanya a kawo muku abinci,ki duba abinda kuke da buqata ki kira mama uwani ki sanar mata,su ummu salma ma ina zaton suna dakin tun dazun suke qorafin rashin dawowarki gashi gobe kamu"
"To ummee na" amiran ta fada tana miqewa
"Muje,ummee idan abdallah ya tashi ki bada shi a kawo mana shi" ta fada tana nuna abdallahn dake kwance yana baccinsa lakadan,kai ummim ta daga don bata son yin magana ta sake bata a lissafin.
Dakina babba sosai wanda ya babu komai cikinsa sai carfet da aka malale shi da shi,katifune saman carfet din ko ina aka kwakwkwantar,yayin da aka lullube kowacce katifa da zanin gado abun rufa da filo qwaya daya alamar kowacce ta kwanciyar mutum guda ce,sai toilet qwaya biyu cikin dakim,da qaton madubi da ya kusa cinye rabin bango,mutum biyar suka taras a dakin,wasunsu na hira wasu na cin abinci,shewa suka sanya da ganin shigowar amaryar,kowacce da abinda zata fadi,nan suka zube aka gaisa suna ci gaba da surutaj,itakam sumayya na gefe tana kallonsu,rayuwar wayewa kawai ake a wannan familyn,kowacce ka gani tana ji da wayewa kyau da arziqin gidansu,akwai alama dake nuna suna da zumunci da kara,sannan akwai sabo da fahimtar juna tsakaninsh,wanda hakan baya rasa nasaba da yadda baabaa prof ya hadasu baki daya ya rungume kowa,duk sallah babba da qarama duk 'ya'yan 'yan uwan na gidansa,baya banbantawa da nashi dangin dana matansa,shi ya sanya kowa yasan kowa,'yammata ne hadaddu wannan na wace wancan ta fada a ranta tana murmushi.
Agogon fata na kamfanin gucci purple dake daure a hannunta ta duba ganin ruwan ya tsagaita sai yayyafi wanda take iya gani ta window din dakin albarkacin hasken lanatarkin da yake tarwai kowane lungu da saqo na gidan
"Zan wuce fa amira" inji sumayya ganin yadda amiran ta bararraje tana kwasar hira,duka sai hankalin su ya dawo kanta har taji nauyin yadda kowa ya dora mata idonshi
"Wasa fa kike amirah,kin manta alqawarinmu,ai ga gun kwanaki nan har na bar gidan nan" sai ta karyar da wuya tana murmushi
"Amma dai ai kya bari naje naga anty ko?"
"Eh,wannan kuma,kuma ai ban ma gama ganinki ba,muje part din anty maamaa akwai abinda zaki gani idan kin dawo na nuna miki sauran" ta fada tana miqewa,itama tashin tayi suka fito,har sun kai qofa tace
"One minute don Allah sis,bari na dauko kayan waccan jarababbar na kai mata,Allah yasa ya musty bai nan" kafin tace komai har ta juya da sauri ta koma,tsayawa tayi tana jiranta gabanta na faduwa,tana addu'an kada Allah ya sa tace sai ta rakatan,don gaskiya ba abinda zai hanata ce mata ba zata ba.
Tana shiga ummu salma tace da ita
"Amira wai ina kika samu wannan babe din haka mai shegen class,wallahi tamun,ta burgeni da ganinta akwai nutsuwa"
"Ga kyau,muryarta ce ni kuma ta burgeni" inji hafsat,dariya suka bata,dukkansu 'ya'yan yar ummee ne,tasu ta bala'in zuwa daya da amira saboda halayyarsu kusan daya ce,ba ruwansu suna da matuqar kirki
"Nan fa gidan anty dije wadda ta muku fried rice da sunan hanan,a nan take"
"Masha Allah wallahi tayi"
"Ai baku ma san tayi ba sai mu da muka je gidansu...." Eesha da hassada ta cikata tace
"Me tayi,mr suke da shi a gidan nasu" amira wadda har ta sanya qafarta zata fita ta fasa ta dawo jin abinda eesham tace,dama tana lura da take takenta akan sumayya,wadda bata ga ita sumayyan abinda ta yi mata ko ta tsareta mata ba
"Basu da komai,amma suna da rufin asiri,suna da wadatar zuci,basu taba kuma roqon wani ba,baya ga haka suna da karamci kyautatawa da girmama baqo,wadan nan abubuwa sun basu komai na rayuwa koda basu da shi din" inji amira ranta a bace sannan ta juya ta fita ranta a bace,humaida ce wadda itama ke jin haushin abinda eeshan keyi ta dora
"Arziqi ba kudi bane eesha,wadatar zuci sanin darajar kai,mutunci yakana da karamci sune arziqin,kana da cin yau kana fa na gobe jibi wata ko shekara ma,kana sanya suturarka ta mutunci,baka taba roqa a baka ba,baka tashi ka rasa abin kaiwa baka me kake nema?"
"Kinga malama,ni ba wani nace mata ba da zaku isheni da dogon wa'azi,ha'an..." Ta qarashe tana jan tsaki,caaa suka mata sun fita yawa ala tilas tayi shiru.
A inda ta barta a nan ta taras da ita,suka ci gaba da takawa ba tare data nuna wa sumayyan akwai wani abu ba,bangaren anty maamaa suka soma shiga,itama bangaren nata masha Allah da mutane,suka gaisa sannan taja hannunta suka tsallake zuwa kitchen dinta,suna shiga tana yunqurin fitowa hannunta dauke da tray wanda aka jera tangaran mai garai garai guda daya wanda ke dauke da hadin salad mai kyau,sai wata qaramar butar shayi irin ta larabawa da cups dinta wanda ke dauke da baqin shayi wanda yasha kayan qamshi iri iri,su'ad ce,fuskar nan a hade tana faman kumburi,ko kunyar idon mutane bata ji,ta zama baturiyar qarfi da yaji,sanye take da dogon wando wanda ya kama jikinta da t.shirt mai gajeran hannu,kanta babu dankwali sai uban qarin gashi wanda aka dasa shi kamar nata na ainihi,ta sanya ribbom ta kameshi,takalmin qafarta kuwa irin mai igiyar nan je,wanda tsininsa ba kawai abun kallo ne,amma akace sabo da yi gawa da gatsine,da yake ta saba tafiya da abunta sam bai dameta ba,hannyenta kuwa farce ne wanda tasha nail polish,gefe suka janye bata ko kallesu ba ta wuce abinta,da kallo amira ta bita tana tabe baki kafin ta maida kallonta ga anty maamaa
"Kumburin banza kawai,shi wanda kike ma kumburin ma baisan kina yi ba,ba kuma ki isa kiyi masa a gabanshi ba,abincin ba bake zaki girki ba ki karba ki kai masa yaci kina baqinciki kamar da kudinki aka sarrafa,wallahi ni yanzu baiken ya musty ma nake gani,kana aure amma kamar ba magidanci ba,babu wani ci gaba da ka samu ko sauyi dangane da tsohuwar rayuwarka" daquwa anty maaman ta jefeta da ita tana fadin
"Sau nawa zan miki magana kan dauke ido daga rayuwarsu?,ke ke zaune da ita?,ko kinga ta kulaki sansa zata fita" shigin shagwaba amiran ke kumbure kumbure tana fadin
"Duk ku kuke sake bata su wallahi,ni da ganin wannan takacin gwara kayi aurenka ma kayi gaba a barku da su" dariya ma ta baiwa anty maaman sai ta dauke kanta tana duban sumayyan
"Qaraso amiran umman khalipha mu gaisa ki qyale wannan tuburarriyar qawar taki,rana iwar haka dai naga wanda zata yi mawa" dariya sumayyan ta saka itama tana qarasowa inda anty maman take,a ladabce ta gaidata tana tambayar yadda ta baro mutanan gidan,sai da suka gama gaisawa sannan tace
"Anty mama,bedroom dinki na bude,zamuga wadan nam kayan" kai ta kada mata suka juya suka fice.
Har bedroom din ta dangana da ita,aljannar duniya sumayya ta kira dakin,cupboard din antyn ta bude ta jawo wata akwati ta ajjiye gaban sumayyan,ta sake janyo wata ta ajjiye sannan ta fara hudewa tana fadin
"Ga kayan da zaki saka na biki baki daya,komai da komai,sarqa kawai zaki buqata bansan choice dinki ba" baki kawai sumayyan ta sake tana kallonta,ta soma ware mata wanda zata sanya gobe kamu,wani dandatsetsen lace ne brown mai yarfin milk wanda aka yiwa dinkin fitted gown,rigar ta dinku iyaka,sai takalmi milk na companyn vinci wanda ke da tsini dunduniya,sake dago wata doguwar riga tayi wadda ta tafi da imaninta,ire iren rigunan da baabaa ya basu da salla ita da laila mai dauke da tambarin companyn MM,itama da takalminta ruwan kwalliyar duwatsun dake jikin rigar tace wannan ta jibi ce ranar arabian night,sake janyo wani shegen yadi tayi wanda bata tantance wanne ba,baqi ne baki dayansa an masa ado da milk din zare tsalli tsalli da milk din qulalai a jiki,shima fitted gown ce,har tafi ta farko fitinuwa,sai wani shegen hill shoes mai igiyoyi ruwan adon jikin yadin da jaka purse mahadin kayan ga
"ankon dinner dinki" amira ta fada tana murmushi,rasa bakin magana kawai tayi tana duban amira,dariya ta sanya sanda ra motsa zata yi magana
"Wallahi idan kika ce wani abu sai mun bata,baabaa ne duka ya bada yace na zabi na dinkawa babbar qawata" kai kawai ta dinga kadawa kafin ta furta kalaman godiya,kunnuwanta ta tasihe da nufin bata son ji.
Daya akwatin kuwa baki daya kayan amarya ne da zata yi fitar biki,fadin irin kyawunsu ma bata baki ne,sai data daga mata su daya bayan daya sannan ta rufe ta maida ma'ajiyarsu tana cewa
"A nan zamu dinga shiryawa,don haka anan zamu bar kayanmu,sai muje kiga lefe dama baki gani ba" dariya tayi
"So kike dai dare yamin banje naga anty ba,ai basai na gani ba amira".
" shikenan,muje ki rakani na miqawa waccan kayanta,sai na rakaki qofa kije ki dawi din"fuska ta narke,ta langabe kai duk don amiran ta haqura da wannan rakiya
"Habbaaa amira,muje dai ki wuce ki kai mata ni kuma na wuce gida"
"Ke kika ce sai na amso mata dinkin ina zaman zamana,saboda haka dole ki rakani" tayi maganar tana gyara nadin mayafinta,miqewa tayi jikinta babu qwari tabi bayan amiran suka fice.