Sashe 68
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da yamma bayan sun gama sallar la'asar sun sake cin abinci nuwaira ta dubi sumayya
"Anty,don Allah ki daure ki dawo gidanmu,abba yace mu roqeki,muna sonki wallahi anty,baki ga yadda hajiya ma ke son ki dawo ba,naji tana cewa ne ba zata sanya baki ba tun yanzun,kada nauyinta ya sanya kiyi abinda bakiyi niyya ba ta shiga haqqinki,don Allah anty ki dawo" ta fada tana karkatar da kai,sai islam ma ta matso
"Eh wallahi anty tunda kika tafi baki daya gidan babu dadi,ko abba ma barin garin yayi,baifi wata daya da dawowa na,da ya dawo kuma kullum masifa suke da mama,gidan ba dadi muna gun hajiya ko yaushe,ki dawo anty don Allah kinji" kasa magana tayi baki daya,wato lukman kwaso mata yaransa yayi kenan su masa campaign ko su daure ta da jijiyar jikinta?
"Anty baki ce komai ba" cewar nuwaira wadda ta qagu taji sumayyan ta amsa,murmushi ta sanya ta kama hannayensu ta hade waje guda
"Kunsan komai nufin Allah ne,kuma ko wanne bawa da irin tasa qaddarar,to ku yita addu'a idan akwai alkhairi zan dawo in sha Allah kunji?"
"To anty" suka fada jikinsu a sanyaye,duka sai suka bata tausayi,babu shakka yaran abun tausayi ne,su masu uwa ma kenan bare mara uwa a gidan,ko da yake dace da uwa ta qwarai shine jigon farinciki da jin dadin rayuwar 'ya'ya duniya da lahira.
Qarfe biyar saura yaro yayi sallama gidan yace su nuwaira su fito,tuni basma ta sheqa da gudu ta gano abban nasu sannan ta dawo
"Abba ne,yace ku fito",kyautar humra da kwalakca ta yiwa kowannansu,sannan ta zuba wata da yawa ta hada da turaren wuta tace su kaiwa hajiya.
A bakin qofar soro ta ja tunga tana musu sallama,nuwaira ta dubeta tana narai narai da idanuwa
"anty iya nan ko qofar gida ma ba zaki rakamu ba?"dariya tayi,ta fuskanci wayo wai yarinyar keson yi mata
"shikenan muje"ta fada don faranta musu,yana tsaye bakin mota ya bubbude qofofin,da dai dai yaran suka dinga shiga tana musu sallama sannan ta rufe musu qofar motar,tana dagowa suka hada idanu
"Ku gaida gida ku gaidamin hajiya" ta fada tana juyawa da niyyar shigewa ciki,da sauri ya tari gabanta
"Haba mana sumayya,ko gaisuwa ai kya tsaya kuyi ko?" Ta tabbata idon yaran yana kanta hakan ya sanyata tsayawa tana dubansa
"Don girman Allah sumayya kimin alfarma ki koma gida na,kimin alfarma ko don rayuwar yara na"
"Ni kuma tawa rayuwar fa?" Ta masa tambaya kai tsaye
"Sumayya gida na ya sauya a yanzu,da qafafuna nake tsaye,hijabin dake lullube da idanuwa Allah ya yamin shi,ki taimaka ki koma gidana ki sa cikasa mana sauran haske da farincikin da muke da buqata,kowa a gida na na buqatarki sumayya,don Allah kada ki gujemu". Kai ta kada
" lukman,bani da buqatar nayi aure har na koma ga mahalicci na,domin ina fata naje na hadu da mijina uban 'ya'yana,ina mai baka shawara tun wuri kayi haquri da ni"ta qarashe zancan zuciyarta na raurawa ta kewayeshi ta wuce ciki,jiki babu qwari a sanyaye shima ya koma cikin motar ya tada ita ya bar layin.
Tana shiga zainab na miqa mata waya,bata san ko waye ba haka bata tambaya ba,tama yi tsammanin anty dije ce don tace anjima zata kira ta,wayar ta maqala a kunne,muryar abdur rahman ta mamayi dodon kunnen nata
"Ba mukhtar kadai ba,ashe har lukman ma na raye a zuciyarki?" Tambayar da ya fara jefo mata kenan wadda ta sanyata saurin janye wayar daga dodon kunnenta,yaushe abdur rahman ya ganta da lukman?,tambayar data yiwa kanta kenan,kawai sai ta tsinci kanta da fashewa da kuka,saman katifarta ta fada tana kife kanta a saman filo,baki daya cikin kwanaki hudu zuwa biyar kacal suna son lalata zaman lafiyar zuciyarta ruhinta da ma gangar jikinta?,wa yace musu tana da buqatar aure a yanzu?,wa yace musu tana buqatar wani daga cikinsu?,akan me zasu yi mata kutse cikin rayuwar data lallabata ta fara samun nutsuwa da dangana?su suke suce ta mance da mukhtar ta fara sabuwar rayuwa da su?,ta mance da mutumin da shi ya fara gina tunani da zuciyarta?.
Qarar wayarta karo na biyu ya sake katse mata tunanin da ya karade ilahirin qwaqwalwarra,kamar ba zata daga ba sai taga lambar anty dije ke yawo bisa fuskar wayar,qara fashewa tayi da kuka da taga sunanta,zuciyarta ta sake karyewa,tasan a irin wannan yanayin babu wanda take budewa damuwarta irin anty dijen,taso ace a yanzu tana kusa da ita,sai ta daga kiran da sauri,saidai maimakon sallama da anty dijen ta tsammata sai taji sautin kukan sumayya ya karade kunnuwanta.
*mrs muhammad ce*👑
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5⃣4⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*Rabbukum a'alamu bima fi nufusikum*
*(haqiqa)ubangijinku shine mafi sani ga abinda yake cikin zukutanku*
_________________________________
A rude anty dije ta soma tambayarta
"Lafiya sumayya?,me yake faruwa?,ko wani ne ya mutu?" Ta jero mata tambayoyin baki daya,jin tayi shiru bata tanka ba ya sanyata itama shirun tana sauraren kukanta,ta tabbatar wata matsalarce ta taso mata haka jikinta ya bata,tausayin yarinyar take ji,sai yaushe ne zata fita daga matsala,sai data dauki a qalla minti goma sannan ta soma magana cikin karayar zuciya
"Anty,lukman da abdur rahman"
"Me ya samesu?"
"Anty......dukkaninsu sun dawo,kowanne so yake na aureshi,fisabilillahi anty ni bazan huta ba?,duka duka yaushe na soma samun nutsuwa?,anty bana buqatar sake wani auren yanzu,tsoro nake ji kada su nufi malam da maganar,idan malam ya umarceni anty bazan iya bijire masa ba" sai ta fashe da kuka,tsaki anty dijen tayi sannan tace
"Zancan banza,kema kin riga da kinsan cewa malam yasan haqqinki na hannunki yanzu,ke zaki zabawa kanki miji ko?,sannan tsakanin lukman da abdur rahman akwai wanda ya isa ya aureki ne bada amincewarki ba da zaki tadawa kanki hankali ki dinga zubda hawayenki?,duk wanda kika zubar a baya bai isheki bane sumayya?,ko so kike wani ciwon ya sokeki?,to nikam na gaji da ji da gani,kishirya da gaske idan nazi tare zamu koma,idan yaso naga wanda zai qara bata ranki" ta fada tana katse wayar.
Shiru tayi tana juya wayar a hannunta,ba haka taso anty dije tace ba shawarar yadda zata kubuce daga tsakanin da lukman da abdurrahman suka sanyata take so ta bata,amma da tayi tsai sai ta lura lallai babu hanyar da zata zille musun idan ba barin garin kanon zata yi ba kamar yadda anty dije tace,sai ta sauke ajiyat zuciya tana goge hawayenta,tana qiyasta idan ta bar kano koda na tsawon wata daya ne itama ta samu hutu,ta samu ta manta da wasu lamuran ta manta da damuwoyinta.
******* ******* *******
Washegari ta shirya don zuwa gidan yaya yahanasu ta dauko abdallah tunda duka duka saura kwana biyu anty dije tazo,tana tsaye a falon mama tana sanya hijabinta tare da yiwa mama sallama suka ji sallamar abdur rahman,kamar ta juya ta shige daki amma tasan idan tayi hakan kamar ta nunawa mama akwai wani lamari tsakaninsu irin wanda ya faru a baya,abinda bata da buri ko fatan kowa ya fahimta kenan
"Ina yini" sumayyan ta gaisheshi tana shirin ficewa bayan sun gaisa da mama
"Lafiya......ina zuwa haka?" Ya tambayeta yana dan dubanta,cikin hanzari ta soma sanya takalmanta tana bashi amsa
"Zan dauko abdallah he gidan ya yahanasu"
"Yauwa,nafi jin dadin tafiya,dama jiya da naje na yiwa abdallah alqawarin yoghourt" ya fada yana miqewa tsaye,kamar ta zura da gudu haka taji,take yanayin fuskarta ya sauya wanda tashin farko ya fahimci bata ji dadin shishshigin da ya mata ba,saidai sam bashi da damuwa matuqar zai kasance da ita,inda zata iya zata ce masa bata so amma idanuwan mama ya sanya ta kasa cewa komai
"Sai mun dawo mama"
"Allah ya kiyaye hanya ku gaida min yahanasun"maman ta fada ba don son ranta ba,don ba kasafai take barinsu suna shiga motocin gida ba koda na 'yan uwa ne,tafi ganewa su hau ta haya
"Zataji" inji zainab wadda ita ce 'yar rakiyar.
Gaban motar ya bude mata da kansa,sai da yaga ta shiga ta zauna sannan ya zagaya nashi mazaunin ya tashi motar suka tafu,shiru ya ratsa motar,babu mai magana tsakaninsu,sai ya sanya hannunshi ya dannan plate jikin redion motar,cikin sakanni lacture malamin dake cikin fefan ta fara tashi,ya daj qaro volume din sannan ya dauke hannayensa ya maida kan sitiyarin motar
"Nikam bansan wanne irin baqin jini ne da ni ba" ya fada qasa qasa yadda ita da shi ne kawai zasu iya jin me yake fadi,ta gefen ido ta kalleshi don ta tabbatar da ita yake ko kuwa,sai ta gane da ita din yake saboda yadda yake kallonta kadan kadan,shiru tayi bata da niyyar tankawa saboda bata fuskanci ma inda zaurancen nasa ya sa gaba ba
"Sumayya me nayi da jiya baki sona,yau ma kinqi karbata,ko na aikata miki wani laifi ne?,ko ina da wani aibu da ban cancanci a soni ba?" Ya tambayeta yana mai muradin jin amsarta
"Baka aikata komai ba,amma don son annabi mubar maganar nan,kada ka manta har yau jinyar zuciyata nake bata warke ba,ban kuma san ranar warkewarta ba" ta fadi tana duban gabanta ba tare da ta dubeshi ba.
Shuru yayi yana jin yadda ransa ya quntata,karo na farko da ya soma jin kishin nukhtar har cikin ransa,mukhtar jininsa ne wanda har ya mutu babu wani abu mara dadi da ya taba hadasu,hakan ya sanya bai sake tofa komai ba har suka iso gidan yaya yahanasun,tayi zaton zai shigo ne da ya ajjiyesu,sai taga ya juya kan motar yayi gaba.
A tsakar gida suka samu abdallan,yana ta wasa da dan qaramin keke da yaya yahansun ta siya masa,jamila na faman binsa tana sauya masa kayansa da yayi kaca kaca da su da miya amma yaqi yarda,ya maidata abar wasansa sai zagaye suke yana dariya,yana ganinta yayi cilli da keken ya taho a guje ya dafeta yana dariya,itama dariyar take,sai taji sanyi a cikin zuciyarta,yaya yahanasu da taji muryarsu ta fito cikin fara'a tana musu sannu da zuwa.
Ina ka saka ina ka ajjiye take tayi da su,kamar zata goya sumayyan,abdallah ya wani ajiye kumatu,abinda yakeso kawai yake cikin gidan,sai bayan sallar magariba sannan suka shirya tafiya,qeme me abdallah yace ba zai bisu ba,saidai sumayyan itama ta dauko kayanta ta zauna anan,dariya suka dinga yi,ganin haka ya sanya sumayyan tace a barshi,duk sanda ya gaji ya dawo.
"Anty,don Allah ki daure ki dawo gidanmu,abba yace mu roqeki,muna sonki wallahi anty,baki ga yadda hajiya ma ke son ki dawo ba,naji tana cewa ne ba zata sanya baki ba tun yanzun,kada nauyinta ya sanya kiyi abinda bakiyi niyya ba ta shiga haqqinki,don Allah anty ki dawo" ta fada tana karkatar da kai,sai islam ma ta matso
"Eh wallahi anty tunda kika tafi baki daya gidan babu dadi,ko abba ma barin garin yayi,baifi wata daya da dawowa na,da ya dawo kuma kullum masifa suke da mama,gidan ba dadi muna gun hajiya ko yaushe,ki dawo anty don Allah kinji" kasa magana tayi baki daya,wato lukman kwaso mata yaransa yayi kenan su masa campaign ko su daure ta da jijiyar jikinta?
"Anty baki ce komai ba" cewar nuwaira wadda ta qagu taji sumayyan ta amsa,murmushi ta sanya ta kama hannayensu ta hade waje guda
"Kunsan komai nufin Allah ne,kuma ko wanne bawa da irin tasa qaddarar,to ku yita addu'a idan akwai alkhairi zan dawo in sha Allah kunji?"
"To anty" suka fada jikinsu a sanyaye,duka sai suka bata tausayi,babu shakka yaran abun tausayi ne,su masu uwa ma kenan bare mara uwa a gidan,ko da yake dace da uwa ta qwarai shine jigon farinciki da jin dadin rayuwar 'ya'ya duniya da lahira.
Qarfe biyar saura yaro yayi sallama gidan yace su nuwaira su fito,tuni basma ta sheqa da gudu ta gano abban nasu sannan ta dawo
"Abba ne,yace ku fito",kyautar humra da kwalakca ta yiwa kowannansu,sannan ta zuba wata da yawa ta hada da turaren wuta tace su kaiwa hajiya.
A bakin qofar soro ta ja tunga tana musu sallama,nuwaira ta dubeta tana narai narai da idanuwa
"anty iya nan ko qofar gida ma ba zaki rakamu ba?"dariya tayi,ta fuskanci wayo wai yarinyar keson yi mata
"shikenan muje"ta fada don faranta musu,yana tsaye bakin mota ya bubbude qofofin,da dai dai yaran suka dinga shiga tana musu sallama sannan ta rufe musu qofar motar,tana dagowa suka hada idanu
"Ku gaida gida ku gaidamin hajiya" ta fada tana juyawa da niyyar shigewa ciki,da sauri ya tari gabanta
"Haba mana sumayya,ko gaisuwa ai kya tsaya kuyi ko?" Ta tabbata idon yaran yana kanta hakan ya sanyata tsayawa tana dubansa
"Don girman Allah sumayya kimin alfarma ki koma gida na,kimin alfarma ko don rayuwar yara na"
"Ni kuma tawa rayuwar fa?" Ta masa tambaya kai tsaye
"Sumayya gida na ya sauya a yanzu,da qafafuna nake tsaye,hijabin dake lullube da idanuwa Allah ya yamin shi,ki taimaka ki koma gidana ki sa cikasa mana sauran haske da farincikin da muke da buqata,kowa a gida na na buqatarki sumayya,don Allah kada ki gujemu". Kai ta kada
" lukman,bani da buqatar nayi aure har na koma ga mahalicci na,domin ina fata naje na hadu da mijina uban 'ya'yana,ina mai baka shawara tun wuri kayi haquri da ni"ta qarashe zancan zuciyarta na raurawa ta kewayeshi ta wuce ciki,jiki babu qwari a sanyaye shima ya koma cikin motar ya tada ita ya bar layin.
Tana shiga zainab na miqa mata waya,bata san ko waye ba haka bata tambaya ba,tama yi tsammanin anty dije ce don tace anjima zata kira ta,wayar ta maqala a kunne,muryar abdur rahman ta mamayi dodon kunnen nata
"Ba mukhtar kadai ba,ashe har lukman ma na raye a zuciyarki?" Tambayar da ya fara jefo mata kenan wadda ta sanyata saurin janye wayar daga dodon kunnenta,yaushe abdur rahman ya ganta da lukman?,tambayar data yiwa kanta kenan,kawai sai ta tsinci kanta da fashewa da kuka,saman katifarta ta fada tana kife kanta a saman filo,baki daya cikin kwanaki hudu zuwa biyar kacal suna son lalata zaman lafiyar zuciyarta ruhinta da ma gangar jikinta?,wa yace musu tana da buqatar aure a yanzu?,wa yace musu tana buqatar wani daga cikinsu?,akan me zasu yi mata kutse cikin rayuwar data lallabata ta fara samun nutsuwa da dangana?su suke suce ta mance da mukhtar ta fara sabuwar rayuwa da su?,ta mance da mutumin da shi ya fara gina tunani da zuciyarta?.
Qarar wayarta karo na biyu ya sake katse mata tunanin da ya karade ilahirin qwaqwalwarra,kamar ba zata daga ba sai taga lambar anty dije ke yawo bisa fuskar wayar,qara fashewa tayi da kuka da taga sunanta,zuciyarta ta sake karyewa,tasan a irin wannan yanayin babu wanda take budewa damuwarta irin anty dijen,taso ace a yanzu tana kusa da ita,sai ta daga kiran da sauri,saidai maimakon sallama da anty dijen ta tsammata sai taji sautin kukan sumayya ya karade kunnuwanta.
*mrs muhammad ce*👑
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5⃣4⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*Rabbukum a'alamu bima fi nufusikum*
*(haqiqa)ubangijinku shine mafi sani ga abinda yake cikin zukutanku*
_________________________________
A rude anty dije ta soma tambayarta
"Lafiya sumayya?,me yake faruwa?,ko wani ne ya mutu?" Ta jero mata tambayoyin baki daya,jin tayi shiru bata tanka ba ya sanyata itama shirun tana sauraren kukanta,ta tabbatar wata matsalarce ta taso mata haka jikinta ya bata,tausayin yarinyar take ji,sai yaushe ne zata fita daga matsala,sai data dauki a qalla minti goma sannan ta soma magana cikin karayar zuciya
"Anty,lukman da abdur rahman"
"Me ya samesu?"
"Anty......dukkaninsu sun dawo,kowanne so yake na aureshi,fisabilillahi anty ni bazan huta ba?,duka duka yaushe na soma samun nutsuwa?,anty bana buqatar sake wani auren yanzu,tsoro nake ji kada su nufi malam da maganar,idan malam ya umarceni anty bazan iya bijire masa ba" sai ta fashe da kuka,tsaki anty dijen tayi sannan tace
"Zancan banza,kema kin riga da kinsan cewa malam yasan haqqinki na hannunki yanzu,ke zaki zabawa kanki miji ko?,sannan tsakanin lukman da abdur rahman akwai wanda ya isa ya aureki ne bada amincewarki ba da zaki tadawa kanki hankali ki dinga zubda hawayenki?,duk wanda kika zubar a baya bai isheki bane sumayya?,ko so kike wani ciwon ya sokeki?,to nikam na gaji da ji da gani,kishirya da gaske idan nazi tare zamu koma,idan yaso naga wanda zai qara bata ranki" ta fada tana katse wayar.
Shiru tayi tana juya wayar a hannunta,ba haka taso anty dije tace ba shawarar yadda zata kubuce daga tsakanin da lukman da abdurrahman suka sanyata take so ta bata,amma da tayi tsai sai ta lura lallai babu hanyar da zata zille musun idan ba barin garin kanon zata yi ba kamar yadda anty dije tace,sai ta sauke ajiyat zuciya tana goge hawayenta,tana qiyasta idan ta bar kano koda na tsawon wata daya ne itama ta samu hutu,ta samu ta manta da wasu lamuran ta manta da damuwoyinta.
******* ******* *******
Washegari ta shirya don zuwa gidan yaya yahanasu ta dauko abdallah tunda duka duka saura kwana biyu anty dije tazo,tana tsaye a falon mama tana sanya hijabinta tare da yiwa mama sallama suka ji sallamar abdur rahman,kamar ta juya ta shige daki amma tasan idan tayi hakan kamar ta nunawa mama akwai wani lamari tsakaninsu irin wanda ya faru a baya,abinda bata da buri ko fatan kowa ya fahimta kenan
"Ina yini" sumayyan ta gaisheshi tana shirin ficewa bayan sun gaisa da mama
"Lafiya......ina zuwa haka?" Ya tambayeta yana dan dubanta,cikin hanzari ta soma sanya takalmanta tana bashi amsa
"Zan dauko abdallah he gidan ya yahanasu"
"Yauwa,nafi jin dadin tafiya,dama jiya da naje na yiwa abdallah alqawarin yoghourt" ya fada yana miqewa tsaye,kamar ta zura da gudu haka taji,take yanayin fuskarta ya sauya wanda tashin farko ya fahimci bata ji dadin shishshigin da ya mata ba,saidai sam bashi da damuwa matuqar zai kasance da ita,inda zata iya zata ce masa bata so amma idanuwan mama ya sanya ta kasa cewa komai
"Sai mun dawo mama"
"Allah ya kiyaye hanya ku gaida min yahanasun"maman ta fada ba don son ranta ba,don ba kasafai take barinsu suna shiga motocin gida ba koda na 'yan uwa ne,tafi ganewa su hau ta haya
"Zataji" inji zainab wadda ita ce 'yar rakiyar.
Gaban motar ya bude mata da kansa,sai da yaga ta shiga ta zauna sannan ya zagaya nashi mazaunin ya tashi motar suka tafu,shiru ya ratsa motar,babu mai magana tsakaninsu,sai ya sanya hannunshi ya dannan plate jikin redion motar,cikin sakanni lacture malamin dake cikin fefan ta fara tashi,ya daj qaro volume din sannan ya dauke hannayensa ya maida kan sitiyarin motar
"Nikam bansan wanne irin baqin jini ne da ni ba" ya fada qasa qasa yadda ita da shi ne kawai zasu iya jin me yake fadi,ta gefen ido ta kalleshi don ta tabbatar da ita yake ko kuwa,sai ta gane da ita din yake saboda yadda yake kallonta kadan kadan,shiru tayi bata da niyyar tankawa saboda bata fuskanci ma inda zaurancen nasa ya sa gaba ba
"Sumayya me nayi da jiya baki sona,yau ma kinqi karbata,ko na aikata miki wani laifi ne?,ko ina da wani aibu da ban cancanci a soni ba?" Ya tambayeta yana mai muradin jin amsarta
"Baka aikata komai ba,amma don son annabi mubar maganar nan,kada ka manta har yau jinyar zuciyata nake bata warke ba,ban kuma san ranar warkewarta ba" ta fadi tana duban gabanta ba tare da ta dubeshi ba.
Shuru yayi yana jin yadda ransa ya quntata,karo na farko da ya soma jin kishin nukhtar har cikin ransa,mukhtar jininsa ne wanda har ya mutu babu wani abu mara dadi da ya taba hadasu,hakan ya sanya bai sake tofa komai ba har suka iso gidan yaya yahanasun,tayi zaton zai shigo ne da ya ajjiyesu,sai taga ya juya kan motar yayi gaba.
A tsakar gida suka samu abdallan,yana ta wasa da dan qaramin keke da yaya yahansun ta siya masa,jamila na faman binsa tana sauya masa kayansa da yayi kaca kaca da su da miya amma yaqi yarda,ya maidata abar wasansa sai zagaye suke yana dariya,yana ganinta yayi cilli da keken ya taho a guje ya dafeta yana dariya,itama dariyar take,sai taji sanyi a cikin zuciyarta,yaya yahanasu da taji muryarsu ta fito cikin fara'a tana musu sannu da zuwa.
Ina ka saka ina ka ajjiye take tayi da su,kamar zata goya sumayyan,abdallah ya wani ajiye kumatu,abinda yakeso kawai yake cikin gidan,sai bayan sallar magariba sannan suka shirya tafiya,qeme me abdallah yace ba zai bisu ba,saidai sumayyan itama ta dauko kayanta ta zauna anan,dariya suka dinga yi,ganin haka ya sanya sumayyan tace a barshi,duk sanda ya gaji ya dawo.