Sashe 34
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsawon minti talatin ta dauka kan layin wayar suna qulla saqa a mugun zare,sosai taji dadi da shawarar data baga,shi yasa bata da kamarta,shawara ce mai sauqi wadda babu zuwa gun boka ko malami,hakanan babu barnar kudi,amma fa buqata zata biya,don dama babbar matsalarta yanzun duka jarinta ya karye warwas,saboda ribar da uwar kudin duka sun tafi gun 'yan tsubbu,bata kwana arba'in bata je an mata service ba,tun tana tsoron hadisin data taba tsintar wasu yaran 'yan makarantar islamiya na karantawa na cewa duk wanda yaje gun boka ko dan duba,to sallarsa ta kwana arba'in Allah bazai karbeta har tazo ta dake tama manta da hadisin baki daya bare ta tunoshi ya zame mata birki. (daya daga cikin abinda Allah ke jarabtar masu biye biyen malamai kenan,basu taba tara abun hannunsu,kullum suna kan hanyar rabawa matsubbata da 'yan duba,ko kishiya gareki mai irin wannan biye biyen ki lura da kyau,duk abinda miji zai baku sai ki nemi nata ki rasa,kullum cikin babu da bani bani take,ba zaki taba ganin burbushin abun ba ko a dakinta ko a jikinta ko a jikin yaranta,Allah ka kiyashemu ka tsare mana imaninmu).
Tana kammala wayar ta saki murmushi ita daya take magana da kanta
"Kissa ai tafi magani,ba shakka quruciyarki ta yimin rana,zan amfana da ita sosai" ta fada tana ficewa a dakin inda kai tsaye ta nufi dakin sumayya.
Tana kwance saman carfet din dakin nata tayi matashin kai da pillow,duk da ba yadda mukhtar baiyi ta dora kan nata saman cinyansa ba amma ta qiya,yana zaune dirshan gabanta da faranti a tsakiyarsu wanda ke dauke da kankana da tuffa da gwanda,ayaba yake bare mata yana miqa mata tana daga kashingide take amsa tana ci,dubansa take kawai cike da mamaki,yana son dawo mata mukhtar dinta,"Allah yasa ba yaudara bace,ya Allah kasa kada ya juyan baya"haka ta dinga fada cikin ranta tana binsa da kallo wanda shi sam bai ma kula ba,hannu ta sanya ta shafi cikinta wansa daga can qasa ta fara jin dan tudu kadan,lumshe idonta tayi tana jin qauna cakude da farinciki na ratsata,duk kwanan duniya takan shafa cikin sau babu adadi,wani lokaci takan tsaya gaban madubi ta dage rigarta tayita kallon fatar cikinta tana mamaki yau ita ke dauke da juna biyu,idanu ya zuba mata shima yana kallonta farinciki na bibiyar duk wara gaba ta jikinsa,a haka ta bude idanunta karaf cikin nashi,sai kunya taso kamata,murmushi yayi sannan yace
"Bakiyi laifi ba sumayya ki qaunaceshi yadda ya kamata,wallahi Allah a duniya ban taba jin son wani abu a rayuwata ba kamar yadda nakejin son cikin dake jikinki ba,zan iya rasa komai sabida shi,zan iya rabuwa da komai saboda shi,don Allah ki kularmin da kanki da abinda ke cikinki komai runtsi" ko bai fadi ba tasan zancan daga zuciyarsa kai tsaye yake fitowa,ita kanta bata san irin son da takewa cikin ba,kai ta sunkuyar tana murmushi tare da furta
"In sha Allah ya mukhtar".
Dukkan wannan maganganun cikin kunnen zainab suka yisu wadda ta sawo kai don shigowa dakin
" ka nunawa kucciya baka"ta fada sannan ta shigo dakin da sallama tana sake sai saita nutsuwarta,gaban sumayya ya fadi har sai data runtse ido cikin zuciyarta tana fadin
"Allahummakh finihim bima shi'ita(Allah ka isar min da su da abinda kaso)(addu'a ce mai kyau ga wanda yaji tsoron zaluncin wasu mutane)" murmushi taje jifarsu da shi wanda shi kansa mukhtar din sai da yayi mamaki
"Ashe kana gun uwar gidanmu my mukhtar" ta fada tana zama kusa da shi,amsa mata yayi sannan ta dora
"Gwara ai ka kular mana da ita sosai musamman da take dauke da cikar muradinmu,Allah mun gode maka daka nuna mana wannan lokaci" ta fada tana maida hankalinta ga sumayya,hannunta tasa ta riqe nata hannun,ji take kamar ta kama garwashin wuta amma sai ta dake
"Sannu sumayya ya jikin naki?" Da qyar ta bude labbanta tace
"Da sauqi"
"Allah ya inganta ya qara miki lafiya kinji,na godewa Allah da zaki samarwa mukhtar sanyin idaniya,naji dadi qwarai dama ke ya cancanta ki fara samun wannan matsayin,don Allah duk abinda kike da buqata ki sanarmin kada kice zaki yiwa kanki wani abu,kada ki duba duka wasu abubuwa da suka faru a baya,sharrin shaidan ne da kuma zuciya wadda bata da qashi,in sha Allah ba zasu sake faruwa ba,sai yanzu na fahimci kyakkyawar zuciya da kuma haqurin da kike da shi,don Allah mu hada kai mu zauna lafiya kinji?" Duk da bata gama gamsuwa ba amma taji dadin maganganun zainab din,ko babu komai wake son tashin hankali?,ai babu abinda yafi zaman lafiya dadi
"Ba komai maman nafi'u,Allah ya sake hada kanmu"
"Ba amin ba,don wallahi da kai na ya hadu da na kishiya gwara na qare rayuwata kan nawa na ciwo" ta fada a zuciyarta,amma afili sai ta saki murmushi tana fadin amin.
Sake matsowa tayi ta karbi bare ayabar daga hannun mukhtar din,ita ta dinga barewa sumayyan tana miqa mata,tanayi can qasan zuciyarta na mata suya,amma fuskarta kuwa murmushi da kulawa ne kwance a cikinsu.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
3⃣0⃣
___________________________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*iy yansur kumullahu fala gaaliba lakum,wa iy yakzulkum faman zal lazi yansur kum min ba'a dih,wa'alal lahi fal yatawakkalil mu'uminin*
*_idan ubangiji ya taimakeku babu wanda ya isa yaci nasara a kanku,idan kuma Allah ya qyaleku(ya fita daga sha'aninku) waye zai taimakeku bayan shi?,ga Allah kawai muminai na qwarai suke dogaro_*
*Ya Allah ka taimakemu cikin dukka lamarun mu*
_________________________________
Kulawa ta musammanzainab ke bawa sumayya wadda zata kwantar da hankalin dukkan wani mai zargi,ta hanata komai,babu abinda sumayyan keyi cikin gidan banda wanke goma ta tsoma biyar,hatta da ruwan wanka ita ke dafa mata ta ajjiye mata a bandaki,girki kowa saidai kawai taci kuma mukhtar ya kwana dakinta,sau tari zainab din kan yafewa sumayya kwananta a zuwan yaje su kwana tare tafi samun kulawa,ta dauke dukka ayyukan gidan bisa wuyanta,ita kadai tasan me take ji cikin zuciyarta,wani lokaci zuciya kan raya mata ta shaqe sumayyan kawai ta mutu ta huta da ganinta da ganin abinda ke cikinta,saidai mardiyya qawarta kan yawaita ja mata kunne da cewa,matuqar ba zatayi haquri ba to kuwa ba zata cimma nasara ba,hakan shike yawaita taka mata burki tana jira har zuwa lokacin da zata kammala qudirinta.
Qwarai mukhtar na jin dadin yadda take kula da sumayyan,yana yaba mata sosai,hankalinsa ya kwanta,duk da cewa har ya zuwa yanzu akwai tasirin ragowar sihirinta a jikinsa,a duniya yanzu babu abinda yake so irin cikin jikin sumayyan,shi yasa hakan da takeyi yake sake saka farinta a idonsa,shi din ma ba'a barshi a baya,hidima da tattali yake mata kan jiki kan qarfi,duk da sai data masa tutsun abinda ya dinga mata a baya,saidai abun mamaki yaje bashi,ya sanar mata sam baisan sadda hakan ta dinga faruwa ba,kallon ya raina mata hankali ta dinga masa,hakan da ya lura da shi ya sanya ya karbi lefin kawai ya kuma bata haquri.
Ita din ma sumayyan ba'a barta a baya ba wajen tattalin kanta da abinda ke cikinta,duk wani abu da tasan zaya kawo tarnaqi ga lafiyar cikinta tana kauce masa,har yau bata bar mamaki ba wai itace yau da ciki bayan shekaru kusan takwas cikin na tara da aurenta,bayan da ta riga ta debe haso?,lallai rabon kwado baya taba hawa saka ko ya hau din ma rabi zaya sauko da shi,babu ranar da zata fito ta fadi bata godewa ubangiji ba.
Mama mahaufiyarta kuwa kullum cikin kiranta a waya take da turowa a duba mata ita,duk sanda zata aiko da abinda zata kawo mata na kayan qwalama na masu ciki,ita kanta yaya yahanasu da taji labarin laqwas jikinta yayi,sai ta rasa me take ciki farinciki ko baqinciki,amma jikinta yayi sanyi ta kuma taya mukhtar din murna,saidai har yau bata je ta ganta ba,tanq gudun wulaqancin da zata taras a gun zainab,don ta yanka musu gargadi kan zuwa gidan duk sadda suka ga dama.
*.........KAYAN KWALABA*
_MAFARI_
Zaune yake gefan gadon dakinsa yana sanya maballan rigarsa a shirin sa na fita kasuwa. Ahankali zainab ra bude qofar dakin ta turo ta a hankali kamar wadda qwai ya fashewa a ciki,kujerar madubu ta janyo ta zauna tana fuskantar mukhtar idanunta a kansa,shi ya soma magana
"Lafiya dai ko?,na lura tun jiya jikinki a sanyaye yake,mu da muke cikin farinciki a kwanakin nan"
"Kake cikin farinciki dai,kuma na kusa datse igiyar farincikin". A zahiri sai ta soma goge qwalla da ta fara sakkowa a idanunta tana kallon mukhtar din
" mukhtar,wannan farincikin da muka samu idan bamuyi wasa ba yana gab da qwacewa daga cikin gidan nan,bansan me yasa take ta qoqarin aikata haka ba,bansan me yake damunta ba"barin sanya takalman da yake qoqarin yi yayi,ya dago ya dubeta idanunsa cike fal da tambaya,har ya gaza boye hakan sai da ya furta
"Kamar yaya fa?,me yake faruwa ne?" Kai ta shiga girgizawa cike kirsa
"A'ah mukhtar,barin maganar nan shi yafi alkhairi,don bansan ya zaka dauketa ba"
"Idan kina tunanin wani abu ne da zai cutar da ni qauna ce ki boyemin kiqi gayan,gaya min zainab" dan shiru tayi a zahiri fuskarta dauke da tashin hankali,yayin da zuciyarta ke cike fal da murna da farinciki tare da fata da addu'ar samu nasara tamkar wata wadda zata aikata abun arziqi,bata kuma magana ba har sai da mukhtar din ya jaddada sake tambayarta,taba goge qwalla tace
"Mukhtar,sumayya ce......sumayya ce naji tana magana da wata baquwa da tayi,bansanta ba,ina tunani ko qawarta ce ko qanwarta ko 'yar uwarsu,wai wallahi sam batayi farinciki da samuwar wannan ciki ba,ina ita ina haihuwa bayan ko shekara ashirim baga gama rufawa ba,dama ita can kawai nunawa take tana son haihuwa amma wlh sam bata qaunarta,bare wai ta lura ba wani kulawa take samu yanzu daga gareka ba,tunda kwanakin baya ka juya mata baya yanzu haka data haihu qila ka sake komawa halayyarka,yanzu haka maganar da nake maka har ta bata shawarar ta sha maganin da zai barar da cikin kawai ta huta".
Tana kammala wayar ta saki murmushi ita daya take magana da kanta
"Kissa ai tafi magani,ba shakka quruciyarki ta yimin rana,zan amfana da ita sosai" ta fada tana ficewa a dakin inda kai tsaye ta nufi dakin sumayya.
Tana kwance saman carfet din dakin nata tayi matashin kai da pillow,duk da ba yadda mukhtar baiyi ta dora kan nata saman cinyansa ba amma ta qiya,yana zaune dirshan gabanta da faranti a tsakiyarsu wanda ke dauke da kankana da tuffa da gwanda,ayaba yake bare mata yana miqa mata tana daga kashingide take amsa tana ci,dubansa take kawai cike da mamaki,yana son dawo mata mukhtar dinta,"Allah yasa ba yaudara bace,ya Allah kasa kada ya juyan baya"haka ta dinga fada cikin ranta tana binsa da kallo wanda shi sam bai ma kula ba,hannu ta sanya ta shafi cikinta wansa daga can qasa ta fara jin dan tudu kadan,lumshe idonta tayi tana jin qauna cakude da farinciki na ratsata,duk kwanan duniya takan shafa cikin sau babu adadi,wani lokaci takan tsaya gaban madubi ta dage rigarta tayita kallon fatar cikinta tana mamaki yau ita ke dauke da juna biyu,idanu ya zuba mata shima yana kallonta farinciki na bibiyar duk wara gaba ta jikinsa,a haka ta bude idanunta karaf cikin nashi,sai kunya taso kamata,murmushi yayi sannan yace
"Bakiyi laifi ba sumayya ki qaunaceshi yadda ya kamata,wallahi Allah a duniya ban taba jin son wani abu a rayuwata ba kamar yadda nakejin son cikin dake jikinki ba,zan iya rasa komai sabida shi,zan iya rabuwa da komai saboda shi,don Allah ki kularmin da kanki da abinda ke cikinki komai runtsi" ko bai fadi ba tasan zancan daga zuciyarsa kai tsaye yake fitowa,ita kanta bata san irin son da takewa cikin ba,kai ta sunkuyar tana murmushi tare da furta
"In sha Allah ya mukhtar".
Dukkan wannan maganganun cikin kunnen zainab suka yisu wadda ta sawo kai don shigowa dakin
" ka nunawa kucciya baka"ta fada sannan ta shigo dakin da sallama tana sake sai saita nutsuwarta,gaban sumayya ya fadi har sai data runtse ido cikin zuciyarta tana fadin
"Allahummakh finihim bima shi'ita(Allah ka isar min da su da abinda kaso)(addu'a ce mai kyau ga wanda yaji tsoron zaluncin wasu mutane)" murmushi taje jifarsu da shi wanda shi kansa mukhtar din sai da yayi mamaki
"Ashe kana gun uwar gidanmu my mukhtar" ta fada tana zama kusa da shi,amsa mata yayi sannan ta dora
"Gwara ai ka kular mana da ita sosai musamman da take dauke da cikar muradinmu,Allah mun gode maka daka nuna mana wannan lokaci" ta fada tana maida hankalinta ga sumayya,hannunta tasa ta riqe nata hannun,ji take kamar ta kama garwashin wuta amma sai ta dake
"Sannu sumayya ya jikin naki?" Da qyar ta bude labbanta tace
"Da sauqi"
"Allah ya inganta ya qara miki lafiya kinji,na godewa Allah da zaki samarwa mukhtar sanyin idaniya,naji dadi qwarai dama ke ya cancanta ki fara samun wannan matsayin,don Allah duk abinda kike da buqata ki sanarmin kada kice zaki yiwa kanki wani abu,kada ki duba duka wasu abubuwa da suka faru a baya,sharrin shaidan ne da kuma zuciya wadda bata da qashi,in sha Allah ba zasu sake faruwa ba,sai yanzu na fahimci kyakkyawar zuciya da kuma haqurin da kike da shi,don Allah mu hada kai mu zauna lafiya kinji?" Duk da bata gama gamsuwa ba amma taji dadin maganganun zainab din,ko babu komai wake son tashin hankali?,ai babu abinda yafi zaman lafiya dadi
"Ba komai maman nafi'u,Allah ya sake hada kanmu"
"Ba amin ba,don wallahi da kai na ya hadu da na kishiya gwara na qare rayuwata kan nawa na ciwo" ta fada a zuciyarta,amma afili sai ta saki murmushi tana fadin amin.
Sake matsowa tayi ta karbi bare ayabar daga hannun mukhtar din,ita ta dinga barewa sumayyan tana miqa mata,tanayi can qasan zuciyarta na mata suya,amma fuskarta kuwa murmushi da kulawa ne kwance a cikinsu.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
3⃣0⃣
___________________________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*iy yansur kumullahu fala gaaliba lakum,wa iy yakzulkum faman zal lazi yansur kum min ba'a dih,wa'alal lahi fal yatawakkalil mu'uminin*
*_idan ubangiji ya taimakeku babu wanda ya isa yaci nasara a kanku,idan kuma Allah ya qyaleku(ya fita daga sha'aninku) waye zai taimakeku bayan shi?,ga Allah kawai muminai na qwarai suke dogaro_*
*Ya Allah ka taimakemu cikin dukka lamarun mu*
_________________________________
Kulawa ta musammanzainab ke bawa sumayya wadda zata kwantar da hankalin dukkan wani mai zargi,ta hanata komai,babu abinda sumayyan keyi cikin gidan banda wanke goma ta tsoma biyar,hatta da ruwan wanka ita ke dafa mata ta ajjiye mata a bandaki,girki kowa saidai kawai taci kuma mukhtar ya kwana dakinta,sau tari zainab din kan yafewa sumayya kwananta a zuwan yaje su kwana tare tafi samun kulawa,ta dauke dukka ayyukan gidan bisa wuyanta,ita kadai tasan me take ji cikin zuciyarta,wani lokaci zuciya kan raya mata ta shaqe sumayyan kawai ta mutu ta huta da ganinta da ganin abinda ke cikinta,saidai mardiyya qawarta kan yawaita ja mata kunne da cewa,matuqar ba zatayi haquri ba to kuwa ba zata cimma nasara ba,hakan shike yawaita taka mata burki tana jira har zuwa lokacin da zata kammala qudirinta.
Qwarai mukhtar na jin dadin yadda take kula da sumayyan,yana yaba mata sosai,hankalinsa ya kwanta,duk da cewa har ya zuwa yanzu akwai tasirin ragowar sihirinta a jikinsa,a duniya yanzu babu abinda yake so irin cikin jikin sumayyan,shi yasa hakan da takeyi yake sake saka farinta a idonsa,shi din ma ba'a barshi a baya,hidima da tattali yake mata kan jiki kan qarfi,duk da sai data masa tutsun abinda ya dinga mata a baya,saidai abun mamaki yaje bashi,ya sanar mata sam baisan sadda hakan ta dinga faruwa ba,kallon ya raina mata hankali ta dinga masa,hakan da ya lura da shi ya sanya ya karbi lefin kawai ya kuma bata haquri.
Ita din ma sumayyan ba'a barta a baya ba wajen tattalin kanta da abinda ke cikinta,duk wani abu da tasan zaya kawo tarnaqi ga lafiyar cikinta tana kauce masa,har yau bata bar mamaki ba wai itace yau da ciki bayan shekaru kusan takwas cikin na tara da aurenta,bayan da ta riga ta debe haso?,lallai rabon kwado baya taba hawa saka ko ya hau din ma rabi zaya sauko da shi,babu ranar da zata fito ta fadi bata godewa ubangiji ba.
Mama mahaufiyarta kuwa kullum cikin kiranta a waya take da turowa a duba mata ita,duk sanda zata aiko da abinda zata kawo mata na kayan qwalama na masu ciki,ita kanta yaya yahanasu da taji labarin laqwas jikinta yayi,sai ta rasa me take ciki farinciki ko baqinciki,amma jikinta yayi sanyi ta kuma taya mukhtar din murna,saidai har yau bata je ta ganta ba,tanq gudun wulaqancin da zata taras a gun zainab,don ta yanka musu gargadi kan zuwa gidan duk sadda suka ga dama.
*.........KAYAN KWALABA*
_MAFARI_
Zaune yake gefan gadon dakinsa yana sanya maballan rigarsa a shirin sa na fita kasuwa. Ahankali zainab ra bude qofar dakin ta turo ta a hankali kamar wadda qwai ya fashewa a ciki,kujerar madubu ta janyo ta zauna tana fuskantar mukhtar idanunta a kansa,shi ya soma magana
"Lafiya dai ko?,na lura tun jiya jikinki a sanyaye yake,mu da muke cikin farinciki a kwanakin nan"
"Kake cikin farinciki dai,kuma na kusa datse igiyar farincikin". A zahiri sai ta soma goge qwalla da ta fara sakkowa a idanunta tana kallon mukhtar din
" mukhtar,wannan farincikin da muka samu idan bamuyi wasa ba yana gab da qwacewa daga cikin gidan nan,bansan me yasa take ta qoqarin aikata haka ba,bansan me yake damunta ba"barin sanya takalman da yake qoqarin yi yayi,ya dago ya dubeta idanunsa cike fal da tambaya,har ya gaza boye hakan sai da ya furta
"Kamar yaya fa?,me yake faruwa ne?" Kai ta shiga girgizawa cike kirsa
"A'ah mukhtar,barin maganar nan shi yafi alkhairi,don bansan ya zaka dauketa ba"
"Idan kina tunanin wani abu ne da zai cutar da ni qauna ce ki boyemin kiqi gayan,gaya min zainab" dan shiru tayi a zahiri fuskarta dauke da tashin hankali,yayin da zuciyarta ke cike fal da murna da farinciki tare da fata da addu'ar samu nasara tamkar wata wadda zata aikata abun arziqi,bata kuma magana ba har sai da mukhtar din ya jaddada sake tambayarta,taba goge qwalla tace
"Mukhtar,sumayya ce......sumayya ce naji tana magana da wata baquwa da tayi,bansanta ba,ina tunani ko qawarta ce ko qanwarta ko 'yar uwarsu,wai wallahi sam batayi farinciki da samuwar wannan ciki ba,ina ita ina haihuwa bayan ko shekara ashirim baga gama rufawa ba,dama ita can kawai nunawa take tana son haihuwa amma wlh sam bata qaunarta,bare wai ta lura ba wani kulawa take samu yanzu daga gareka ba,tunda kwanakin baya ka juya mata baya yanzu haka data haihu qila ka sake komawa halayyarka,yanzu haka maganar da nake maka har ta bata shawarar ta sha maganin da zai barar da cikin kawai ta huta".