Sashe 73
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Suna gab da fita daga gidan baba halliru cikin gaggawa ya budewa motar wadda aketa faman danna horn kamar za'a tashi unguwar,baqar motace wadda ke dauke da baqaqen glass baqi wanda har baka iya hango wanda ke ciki ta danno cikin gidan a guje wanda badan grass carfet dake harabar gidan ba da anga tashin qura
"Hmmm,gata nan ta dawo Allah yasa an tashi ma" laila ta fada tana hararar motar sanda suke qoqarin fita
"Anty su'ad ko?" Inji khalipha ya tambaya yana kallon laila tare da tabe bakinsa
"Itace mana,nifa shi yasa idan tana garin bana son shiga gidan baabaa wallahi anty sumayya" ta fadi tana duban sumayya tana son bata labari,saidai hararar ta sumayyan tayi
"Ke kam laila ke da khalipha bansan wanda yafi wani surutu ba wallahi"
"Wallahi ya fini" inji laila tana dariya,take musu ya sarqe tsakaninsu da khaliphan har suka qarasa cikin gidan.
Shigarta ta tadda wayar gidan nata faman ruri anty dije na kuma saukowa da alama fitowarta kenan daga wankan
"Qarar wayar nan ce ta isheni,tunda kika fita aka dinga kira,hafiz ya daga akace ke nema ya gaya musu baki kusa amma basu daina kira ba,don Allah jeki daga ko kunnuwanmu sa huta" bata fuska tayi ranta na baci,jikinta ya bata mai kiran jiya ne wanda ya kira kansa da alqasim
"Ni wa na sani anty da zai kirani da lambar wayar gidanku,na gaya musu bani bace amma anqi daina kira"
"To amma ya akayi haka?,shikenan....bari na daga na musu bayani" antyn ta fada tana nufar kitchen,sai sumayyan tayi saurin barin falon ta shige dakinta haushinsa na kamata,haka kawai don musiba yana son ya zame mata jarfa,ta bar kanon amma don ta samu hutu ta nutsu amma bata samu nutsuwar ba,ina dalili,su qarke qalau da anty dijen.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5⃣7⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wallahi tallahi billahil azim duk wanda baibi Allah ba ya shiga uku,duk wanda baiji tsoron Allah ba ya kade,duk wanda tsoron Allah bai hanashi bin son zuciyarsa ba yana cikin babbar musiba,dan adam ba kowa bane hakanan ba komai bane shi,kaji tsoron ubangijinka kayi biyayya a gareshi KAJI TSORON AZABARSA KAYI KWADAYIN RAHAMARSA sai ka samu rabauta,ka guji duk wani abu mara kyau,kayi riqo da kyawawan ayyuka, 'YAR UWA,KI KARANTA YADDA UBANGIJI DA MA'AIKI SUKA WASSAFA MANA JAHANNAMA,ALLAH KAYI MANA TSARI DA ITA BADON HALAYENMU BA,KADA KA NUNA MANA ITA KO NA QIFTAWAR IDO NE,KA BAMU IKON YIN BIYAYYA A GAREKA,KA KADE MANA ZUKATANMU DAGA TUNANI KO AIKATA DUK WANI SABO KO ZALUNCI*
______________________________________
Kwanaki nata tafiya,tun tana a takure da zaman garin har tazo ta fara sakin jiki,abu daya ke damunta kewar abdallah,tausayinsa take hakanam tausayinsa ya ninku a zuciyarta tun daga randa ya rasa mahaifinsa,kullum takan kira a bata shi su gaisa susha hirarsu,abinda ya sake kwantar mata da hankali a nan ba inda take zuwa bare ta gamu da wani yace mata yana sonta,hakanan kiran waya ma da ake ana nemanta tun ranar da anty dije tayi magana aka samu sauqim kiran,sai jifa jifa shi din ma ba dagawa take ba,abdur rahman ne kadai ke kiranta su sha hirarsu har ta riga da ta saba,babu wata rana da zata fito ta fadi bai kirata ba,ta sake sosai don bai qara yi mata wata magana daban ba banda ta zumunci,anty dije tayi ta mata tsiyar batasan muguwar kifin rijiya bace ita sai yanzu,bata son zuwa ko ina,ko gidan baabaa prof shigarta biyu kwata kwata shima da dalili na farkon kiran laila da taje,na biyu kuma da sumayyan tayi dambu gidan ba yara ta sata ta kaiwa anty maamaa da yake ita mai son dambu ce,kota shiga din ma bata wuce minti biyar ko goma ta fito,hakan ya sanya anty dije ta bada sautun kayan turare da humra aka kawowa sumayyan ta soma yi a nan,cikin designers kwalabe take zubawa,nan take kuwa ta soma ciniki,duk da wani gu ake kaiwa,'yan unguwar ne kawai ki zuwa siya cikin gida.
Yau ma kamar kullum babu yara a gidan suna makaranta,gab suke da fara jarabawa ayi musu hutu saboda gabatowar wata mai alfarma na azumin watan ramadan,suna zaune da anty dije a kitchen tana anty dijen ke girki yau sumayya na ganin yadda take yi din don bata iya irinsa ba,iya zamanta da anty dijen ta qaru da abubuwa da dama ta fannin zamantakewar gida,girki iri iri,gyaran jiki da kuma uwa uba iya gayu,wayarta anty dijen ta daga wadda ta fara ruri ta kara a kunne,ganin haka sumayya ta karbi yankan cabbage din da takeyi taci gaba,sai data gama sannan ta dubi sumayyan
"Sumayya,inaga fa ke zaki miqawa anty maamaa humrar nan,kaya take hadawa kuma kinga yaran basu dawo ba" kasaqe tayi,sarai anty dijen ta gane bata son zuwa ne,bata san me yasa bata qaunar shiga gidan ba amma sai ta shareta,ta gane mai anty dijen ke nufi tilas ta miqe tace to,dakinta ta shiga ta sanya dogon hijabinta har qasa sannan ta jawo ledar data jera humrorin wadda anty maamaa ta bata tayi mata,saboda umrar azumi da zasu tafi ita da maigidan da kuma ummee,sai babban yaron gidan shi da matansa biyu sai qaninsa da tashi matar,sai manyan jikokin gidan su biyar duk da basu wuce shekara sha hudu zuwa qasa ba,duk laila aku(sunan da idan taso take kiranta da shi kenan kusamman idan tayi hali ) ke bata wannan labarin tunda ita ba shiga take ba ballantana ta sani.
Kamar kullum a hankali ta dinga ratsa gidan bayan sun gaisa da mai gadin dake gadin wannan qofar sa suke shigowa da yake akwai wata qofar ta baya,mutumin ya haifeta shi yasa take ganin girmansa,mutum me mai faran faran da son jama'a,duk da ganinsa da sumayyan baifi uku ba amma yana yabawa hankalinta yadda take rusunawa ta gaidashi,duk da yasan iyalan gidan alhj umar farouq ba baya bane wajen tarbiyya.
Kanta a qasa qirjinta na bugawa ta dinga kutsawa cikin gidan,batasan me yasa take yawan faduwar gaba ba idan ta shigo gidan,ko don tana ganin kamar akwai banbancin matsayi tsakaninsu bai kamaci ta dinga shiga musu gida ba.
Tazo mararrabar sashin anty maamaa data ummee sai taso ta manta wane waje ne na anty maaman don bata rarrabewa da sunayensu,a hankali ta juya idanuwanta tana canki canki,karaf idanuwanta suka sauka a kansu,zaratan samari ne ke tsaye su biyu suna magana da junansu,dukkaninsu dogaye ne saidai daya yafi daya masu matsakaicin jiki,kowannensu na sanye da t.shirt da trouser masu mabanbantan kaloli kowa da kalar nasa,farare tas da su kamar yadda ta dan fahimci haka kalar fatar masu gidan take,fuskar daya kawai taje gani bata ganin ta dayan kasancewar ya juya baya ne yana magana da dayan,da alamu kuma duk hankalinsa na kanshi,shima ya ganta,idanu ya sanya yana kallonta har waccan ya kammala fadin abinda zaice yayi gaba ya shige daya sashen.
Rudewa tayi kamar mara gaskiya,jikinta ya soma rawa ta fara qoqarin juyawa ta koma inda ta fito ganin kamar yana takowa inda take
"Wa kike nema?" Ya tambayeta fuskarsa ba yabo ba fallasa,cikin qoqarin daidaita nutsuwarta ta hada kalmar
"Sashen anty maamaa nake nema"
"Ko gun amira kika zo?" Ya sake tambayarta yana kallon ledar hannunta,bata ma gane wace amirar ba,sai tave masa
"A'ah,saqo na kawowa anty maamaa" sai taga ya saki murmushi
"Yauwa,muje ma na rakaki,Allah yasa wannan turaren mai dadi aka kawo mata wanda tamin alqawari" ya fada yana yin gaba cikin mishadi,ta bishi a baya tana cike da mamakin sauqin kai irin nasa,batayi tsammanin haka ba.
Falon suka shiga yana sallama cikin daga murya,wannan budurwar da take zaton ita ce amirar ta fito da sauri daga kitchen tana dariya,bata lura da sumayya dake bayansa ba,ganinsa ya sanyata tsaya tana dubansa tana qyalqyala dariya,da alama wani abu da ya faru dazun tsakaninsu taje tunawa
"Ya akayi yaya mahmoud?" Ta fada tana sake tuntsira dariya
"Zaki zo hannu ai kin sani.....yanzu ba wannan ba ga baquwa nan tazo wajen anty maamaa" dan leqowa amiran tayi inda sumayya ke tsaye,sai tayi murmushi
"Ba baquwa bace a gidansu umman khlipha take,duk da dai baquwa ce a gidan nan saboda na fuskanci bata son mutane" ta fada tana murmushi
"Ke kuma gaki da shegen kwashe kwashe ko,ki bata guri parrot tukunna,ki gayawa anty zan dawo anjima,yanzun yaa man ya aikeni ne" ya fada yana juyawa zai fice,ganin haka yasa amira daga murya
"Don Allah ya mahmoud ka siyo min na tuba" ta fada a shagwabe tana kama kunnuwanta guda biyun,harara ya watsa mata yayi ficewarsa,sai ta narke fuska kamar zata yi kuka har ya bace a falon kafin ta maida kanta wajen sumayya.
Murmushi tayi mata sannan tace
"Ga waje zauna,amma sai kin dan jira antyn don tana wajen dan tsohon mijinta,kinsan ba'a kiranta idan ya shigo sai mutum ya jirata" ta fada cikin salon tsokana tana dariya,itama sumayyan sai ta saki murmushi,kusan haka halayyar anty dije take,take mukhtar ya fado mata,a hankali sai murmushin nata ya soma gushewa damuwa ta fara bijiro mata,take ta fada kogin tunani tana tuna wasu lokuta masu dadi daga cikin rayuwar da sukayi tare da shi.
"Hmmm,gata nan ta dawo Allah yasa an tashi ma" laila ta fada tana hararar motar sanda suke qoqarin fita
"Anty su'ad ko?" Inji khalipha ya tambaya yana kallon laila tare da tabe bakinsa
"Itace mana,nifa shi yasa idan tana garin bana son shiga gidan baabaa wallahi anty sumayya" ta fadi tana duban sumayya tana son bata labari,saidai hararar ta sumayyan tayi
"Ke kam laila ke da khalipha bansan wanda yafi wani surutu ba wallahi"
"Wallahi ya fini" inji laila tana dariya,take musu ya sarqe tsakaninsu da khaliphan har suka qarasa cikin gidan.
Shigarta ta tadda wayar gidan nata faman ruri anty dije na kuma saukowa da alama fitowarta kenan daga wankan
"Qarar wayar nan ce ta isheni,tunda kika fita aka dinga kira,hafiz ya daga akace ke nema ya gaya musu baki kusa amma basu daina kira ba,don Allah jeki daga ko kunnuwanmu sa huta" bata fuska tayi ranta na baci,jikinta ya bata mai kiran jiya ne wanda ya kira kansa da alqasim
"Ni wa na sani anty da zai kirani da lambar wayar gidanku,na gaya musu bani bace amma anqi daina kira"
"To amma ya akayi haka?,shikenan....bari na daga na musu bayani" antyn ta fada tana nufar kitchen,sai sumayyan tayi saurin barin falon ta shige dakinta haushinsa na kamata,haka kawai don musiba yana son ya zame mata jarfa,ta bar kanon amma don ta samu hutu ta nutsu amma bata samu nutsuwar ba,ina dalili,su qarke qalau da anty dijen.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5⃣7⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wallahi tallahi billahil azim duk wanda baibi Allah ba ya shiga uku,duk wanda baiji tsoron Allah ba ya kade,duk wanda tsoron Allah bai hanashi bin son zuciyarsa ba yana cikin babbar musiba,dan adam ba kowa bane hakanan ba komai bane shi,kaji tsoron ubangijinka kayi biyayya a gareshi KAJI TSORON AZABARSA KAYI KWADAYIN RAHAMARSA sai ka samu rabauta,ka guji duk wani abu mara kyau,kayi riqo da kyawawan ayyuka, 'YAR UWA,KI KARANTA YADDA UBANGIJI DA MA'AIKI SUKA WASSAFA MANA JAHANNAMA,ALLAH KAYI MANA TSARI DA ITA BADON HALAYENMU BA,KADA KA NUNA MANA ITA KO NA QIFTAWAR IDO NE,KA BAMU IKON YIN BIYAYYA A GAREKA,KA KADE MANA ZUKATANMU DAGA TUNANI KO AIKATA DUK WANI SABO KO ZALUNCI*
______________________________________
Kwanaki nata tafiya,tun tana a takure da zaman garin har tazo ta fara sakin jiki,abu daya ke damunta kewar abdallah,tausayinsa take hakanam tausayinsa ya ninku a zuciyarta tun daga randa ya rasa mahaifinsa,kullum takan kira a bata shi su gaisa susha hirarsu,abinda ya sake kwantar mata da hankali a nan ba inda take zuwa bare ta gamu da wani yace mata yana sonta,hakanan kiran waya ma da ake ana nemanta tun ranar da anty dije tayi magana aka samu sauqim kiran,sai jifa jifa shi din ma ba dagawa take ba,abdur rahman ne kadai ke kiranta su sha hirarsu har ta riga da ta saba,babu wata rana da zata fito ta fadi bai kirata ba,ta sake sosai don bai qara yi mata wata magana daban ba banda ta zumunci,anty dije tayi ta mata tsiyar batasan muguwar kifin rijiya bace ita sai yanzu,bata son zuwa ko ina,ko gidan baabaa prof shigarta biyu kwata kwata shima da dalili na farkon kiran laila da taje,na biyu kuma da sumayyan tayi dambu gidan ba yara ta sata ta kaiwa anty maamaa da yake ita mai son dambu ce,kota shiga din ma bata wuce minti biyar ko goma ta fito,hakan ya sanya anty dije ta bada sautun kayan turare da humra aka kawowa sumayyan ta soma yi a nan,cikin designers kwalabe take zubawa,nan take kuwa ta soma ciniki,duk da wani gu ake kaiwa,'yan unguwar ne kawai ki zuwa siya cikin gida.
Yau ma kamar kullum babu yara a gidan suna makaranta,gab suke da fara jarabawa ayi musu hutu saboda gabatowar wata mai alfarma na azumin watan ramadan,suna zaune da anty dije a kitchen tana anty dijen ke girki yau sumayya na ganin yadda take yi din don bata iya irinsa ba,iya zamanta da anty dijen ta qaru da abubuwa da dama ta fannin zamantakewar gida,girki iri iri,gyaran jiki da kuma uwa uba iya gayu,wayarta anty dijen ta daga wadda ta fara ruri ta kara a kunne,ganin haka sumayya ta karbi yankan cabbage din da takeyi taci gaba,sai data gama sannan ta dubi sumayyan
"Sumayya,inaga fa ke zaki miqawa anty maamaa humrar nan,kaya take hadawa kuma kinga yaran basu dawo ba" kasaqe tayi,sarai anty dijen ta gane bata son zuwa ne,bata san me yasa bata qaunar shiga gidan ba amma sai ta shareta,ta gane mai anty dijen ke nufi tilas ta miqe tace to,dakinta ta shiga ta sanya dogon hijabinta har qasa sannan ta jawo ledar data jera humrorin wadda anty maamaa ta bata tayi mata,saboda umrar azumi da zasu tafi ita da maigidan da kuma ummee,sai babban yaron gidan shi da matansa biyu sai qaninsa da tashi matar,sai manyan jikokin gidan su biyar duk da basu wuce shekara sha hudu zuwa qasa ba,duk laila aku(sunan da idan taso take kiranta da shi kenan kusamman idan tayi hali ) ke bata wannan labarin tunda ita ba shiga take ba ballantana ta sani.
Kamar kullum a hankali ta dinga ratsa gidan bayan sun gaisa da mai gadin dake gadin wannan qofar sa suke shigowa da yake akwai wata qofar ta baya,mutumin ya haifeta shi yasa take ganin girmansa,mutum me mai faran faran da son jama'a,duk da ganinsa da sumayyan baifi uku ba amma yana yabawa hankalinta yadda take rusunawa ta gaidashi,duk da yasan iyalan gidan alhj umar farouq ba baya bane wajen tarbiyya.
Kanta a qasa qirjinta na bugawa ta dinga kutsawa cikin gidan,batasan me yasa take yawan faduwar gaba ba idan ta shigo gidan,ko don tana ganin kamar akwai banbancin matsayi tsakaninsu bai kamaci ta dinga shiga musu gida ba.
Tazo mararrabar sashin anty maamaa data ummee sai taso ta manta wane waje ne na anty maaman don bata rarrabewa da sunayensu,a hankali ta juya idanuwanta tana canki canki,karaf idanuwanta suka sauka a kansu,zaratan samari ne ke tsaye su biyu suna magana da junansu,dukkaninsu dogaye ne saidai daya yafi daya masu matsakaicin jiki,kowannensu na sanye da t.shirt da trouser masu mabanbantan kaloli kowa da kalar nasa,farare tas da su kamar yadda ta dan fahimci haka kalar fatar masu gidan take,fuskar daya kawai taje gani bata ganin ta dayan kasancewar ya juya baya ne yana magana da dayan,da alamu kuma duk hankalinsa na kanshi,shima ya ganta,idanu ya sanya yana kallonta har waccan ya kammala fadin abinda zaice yayi gaba ya shige daya sashen.
Rudewa tayi kamar mara gaskiya,jikinta ya soma rawa ta fara qoqarin juyawa ta koma inda ta fito ganin kamar yana takowa inda take
"Wa kike nema?" Ya tambayeta fuskarsa ba yabo ba fallasa,cikin qoqarin daidaita nutsuwarta ta hada kalmar
"Sashen anty maamaa nake nema"
"Ko gun amira kika zo?" Ya sake tambayarta yana kallon ledar hannunta,bata ma gane wace amirar ba,sai tave masa
"A'ah,saqo na kawowa anty maamaa" sai taga ya saki murmushi
"Yauwa,muje ma na rakaki,Allah yasa wannan turaren mai dadi aka kawo mata wanda tamin alqawari" ya fada yana yin gaba cikin mishadi,ta bishi a baya tana cike da mamakin sauqin kai irin nasa,batayi tsammanin haka ba.
Falon suka shiga yana sallama cikin daga murya,wannan budurwar da take zaton ita ce amirar ta fito da sauri daga kitchen tana dariya,bata lura da sumayya dake bayansa ba,ganinsa ya sanyata tsaya tana dubansa tana qyalqyala dariya,da alama wani abu da ya faru dazun tsakaninsu taje tunawa
"Ya akayi yaya mahmoud?" Ta fada tana sake tuntsira dariya
"Zaki zo hannu ai kin sani.....yanzu ba wannan ba ga baquwa nan tazo wajen anty maamaa" dan leqowa amiran tayi inda sumayya ke tsaye,sai tayi murmushi
"Ba baquwa bace a gidansu umman khlipha take,duk da dai baquwa ce a gidan nan saboda na fuskanci bata son mutane" ta fada tana murmushi
"Ke kuma gaki da shegen kwashe kwashe ko,ki bata guri parrot tukunna,ki gayawa anty zan dawo anjima,yanzun yaa man ya aikeni ne" ya fada yana juyawa zai fice,ganin haka yasa amira daga murya
"Don Allah ya mahmoud ka siyo min na tuba" ta fada a shagwabe tana kama kunnuwanta guda biyun,harara ya watsa mata yayi ficewarsa,sai ta narke fuska kamar zata yi kuka har ya bace a falon kafin ta maida kanta wajen sumayya.
Murmushi tayi mata sannan tace
"Ga waje zauna,amma sai kin dan jira antyn don tana wajen dan tsohon mijinta,kinsan ba'a kiranta idan ya shigo sai mutum ya jirata" ta fada cikin salon tsokana tana dariya,itama sumayyan sai ta saki murmushi,kusan haka halayyar anty dije take,take mukhtar ya fado mata,a hankali sai murmushin nata ya soma gushewa damuwa ta fara bijiro mata,take ta fada kogin tunani tana tuna wasu lokuta masu dadi daga cikin rayuwar da sukayi tare da shi.