← Book details Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 164 OF 226

Sashe 164

Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

      Wayarshi ce ta fara tsuwwa,ga zatonshi ma umme ce zata ce ya hadata da sumayya,saboda haka bai ko dubaba ya daga yana karawa akunnensa,ya maqaleta a kafadarshi yana ci gaba da shafarshi,muryar su'ad ce cikin bacin rai da kwantar da murya cikin harashen nasara
"Ashe da gaske ne abinda akefadi idan namiji yayi aure wulaqantaki yake?,yanzu a haka kakeso na yarda na karbi kishiyar da ka yimin mu zauna tare?"shiru yayi tamkar bai kam layin har sai data kira sunanshi,kawai sai ta saki kuka harda sheshsheqa,cikin harshen hausa da son dawo da qauna cikin zuciyar wanda kuke magana tace
"almustapha kasan duk duniya babu wani abu da nake qauna sama da kai don me zaka yimin haka?"
"Look su'ad,wannan baki daya matsalarki ce ni ban da case da duka zantukanki,i think na gaya miki dukkan wani rules nawa ko?,so pls idan zaki iya bi bismillah,if not ki qyaleni na huta hakanan"
"Ni kake wulaqantawa haka maan?"cikin fushi yace
"if u dont like how things are,take control,decide how u ar going to change it,kada ki sake nema na daga yau,take me as iam,or leave me as iam"katse layin yayi ya jefa wayar gefanshi,cikin bacin rai yaci gaba da shiryawa sauri sauri,sumayya kam tunda taji ya ambaci su'ad ta miqe ta shige toilet,dama wanka take sonyi wanda yau bata samu tayi da wuri ba tun na safe da tayin.

         Cire wayar su'ad tayi daga kunnenta sanda ta fahimci ya katse kiran nata,duk da ba yau ne farau ba idan tazo masa da shirme amma wannan yayi matuqar baqanta mata,gani take kawai saboda ya sake aure ne ya sake qaro wulaqanci fiye da wanda ta sanshi da shi,hawaye na bin idanuwanta ta dubi mamanta,sannan ta dubi qanwar maman nata anty kubra dake zaune tana kallonta wadda ke zaune ita mijinta a south africa,ta zo ne american wajen yayarta ta tadda wannan cakwakiyar
"Ba sai kince komai ba naji komai,ai wallahi laifinki ne khaulat,ta yaya har zaki bari su'ad tayi wasa da damarta,kunfi kowa sanin samun damar auren irin su mustaphan sai wanda Allah ya zaba nan gidan duniya,tun tuni kallonku kawai nake,yarinya tana gantalinya da sunan karatu,karatun uwar me?,me zata ci da karatun?,me take nema da shi?,dame mijinta ya rageta?,bata taba tambayarsa abu komai yawansa yace mata babu ko bazai bayar ba saidai ma ya ninka mata,kuna zaton miji irin mustapha wanda Allah ya yuwa baiwar kyau da kudi zai zauna bai sake aureba bayan yana da mace irin su'ad?,to ta godewa Allah ma daba neman mata yake ba ya kwaso wata cutar ya laqaba mata,kinga idan zaki zubar da wannan gantalallen karatun naki kije ki kwashu makaman qwatar mijinki kije ku buga ke da ita mai rabo ka dauka to,ta taki qatuwar sa'ar samun auren elmustapha bayan gwagwarmayar da aka sha,duk da tasan cewa ba sonta yake ba amma tausayi da qaunar da take masa ya sanya ya amincewa aurenta" ta fada tana maida numfashin takaici
"To kuma kubra me ya kawo tonon silili haka?,abinda ya wuce ai ya riga ya wuce ko?,kawai shawara muke da buqata"
"Ki tattarata ta koma gidanta,ko a kango yace ta zauna ba nijeria ba ta zauba,bare ma meye marabar gidan nata da nan din?don kawai tana cikin family house,kowa ya sani qaryarka kace gidan mutum kamar almustapha an rasa jin dadi da walwala da dukka wata qawar duniya,idan zata koma taje kowa ta qwaci mijinta to,idan kuma zama zatayi bismillah saikici gaba da dorata akeken bera ki kuma share mata wajen zama,kinsan dai ko auren ta kaso wallahi duk yadda takejin kan nan nata a sama ba zata samu wanda ya koda kama qafar doctor mustapha ba"
"Ya isa kubra don Allah,ke dole sai kin zagi mutum zakiji dadi" waiwayawa haj khaulat tayi ta dubi su'ad dake zaune hawaye shabe shabe,har cikin qirjinta taje jin kishin mustapha,tamkar ta dauki ran wadda ta aure mata shi haka take ji,kullum kwanan duniya ji taje kamar ta yanki ticket ta koma masa,don tun kafin a kai ko ina ta soma raina kanta,ta tabbatar rabuwa da mustapha kamar yadda tayi iqirari ba mi yiwuwa bane a rayuwarta,ko sakinta yayi tana jin ba zata iya qara aure ba har ta mutu,don gani take nan duniya babu kamar yashi
"Zaki shirya ki koma wajen mijinki,daga yau so nake kada ki saurara kada ki daga qafa,duk inda ya sanya qafa ki bishi,sai kin tabbatar kin mamaye rayuwarshi,sannan cijin gidan bance ki saurarawa uban kowa ba,fin baki dayansu munafukai ne,suna da masaniyar qara auren nasa su suka hada,ki taka uban kowa koda kuwa hajiya zuwairiyya ce uwarsa kinji na gaya miki,ki fara shiri,naji labarin biki ya tasi a gidan,zaki isa ranar daurin aure don kiga idon uban kowa,uban kowa yaga naki idon ihee"kai su'ad ta gyada cike da gamsuwa da samun qwarin gwiwa,itadai kubra na gefe tana kallonsu tana tabe baki,ta tabbatar zamansu bazai taba daidaita da mustaoha ba matuqar tace zata taba iyayensa,kai ta dauke tana qissima yadda dramer zata kwashe.

        Minti talatin cif ta fiti daga bandakin,ba kowa cikin dakin alamar ya fita,hakan ya sanya cikin nutsuwa ta fara shiryawa bayan ta kulle qofar,sai data gama komai tsaf sannan ta bude ledar daya bata ta zari rigar ta wareta,sosai rigar tayi mata bata taba ganin irin desing dinta ba,bisa dukkan alamu sabuwar design ne dako kasuwa bata kai ga fita ba,sai taji tana sha'awar sanyawa,saboda haka kai tsaye ta zirata ta daidaita ta ajikinta,cif cif tayi mata har fadin tamkar an gwadata,ta fidsa shape din qirjinta sosai zuwa faffadan qugunta,qila hakan baya rasa nasaba da tsahonsu da ya kusa zuwa daya da abida,saidai abidan ta fita jiki,don sake qawata rigar a jikinta sai ta bude inda take ajiyar dankunnayenta,ta sanya dankunne da 'yar sarqar hannu wadda ta dace da kalar dutsen da aka qawata rigar da shi,yafa mayafin kawai tayi bayan ta daure gashinta,sai ta fito tamkar wata balariyar qasar,murmushi ta saki sanda ta kalli kanta a madubi,ba shakka tayi amsheta rigar,wayar dake gefanta ta jawo ta dauki hoto guda biyu,zata qara sai ta tuna ta almustapha ce,ajjiyeta tayi inda ta dauka ta wuce zuwa saman kujera kuma gadonta ta koma ta zauna ta janyo littafin wajen anty dije taci gaba da karantawa karo na biyu tunda ta bata shi.

       A quntace yake takowa zuwa qofar dakin nasu cikin tafiyarshi ta qasaita,ranshi har yanzu a matuqar bace yake,hannunshi ya sanya ya murda handle din da niyyar turawa ya shiga sai yaji qofar a rufe tanke,ranshi ya dan baci,ya soma knocking a zafafe,littafin ta ajjiye cikin fargabar yadda ake qwamqwasa qofar,ta isa bakin qofar cikin siririyar muryarta tana fadin
"Ana zuwa" ta janyo qofar baya,idanunshi suka fada kanta ba tare da ya shirya ba,kallo ya shiga qare mata tun daga yatsun qafarta zuwa kanta,ya dawo ya dire a qirjinta,boyayyar ajiyar zuciya ya saki,bai taba tsammanin rigar da suke fitarwa ta kai kyawun haka ba duk da yasan yadda suke zuba fasaha wajen saqata ba sai yau,dalili kuwa bai taba tsayawa ya qare mata kallo jikin wata ba sai yau din,koda ya kawowa su'ad bai taba gani ta saka ba,hasalima saidai ta bayar ko tayi kyautar neman suna,ita dole ace mijinta ke da MM VAIL AND ABAYA INTERNATIONAL COMPANY,amma bata taba rabata a jikinta ba,a cewarta tayi mata nauyi ko zata bata mata tsarin shigarta duk kuwa da yadda abayar ta kai ga kyau da tsada,sosai shigar abaya ta sake burgeshi duk da dama can yana sonta,da sauri ya hade fuska sanda suka hada idanu ta kama shi yana kallonta,baya taja a hankali cikin tsoron irin kallon da yake kata,takowa ya soma yi zuwa ciki murya a dake yana fadin
"Idan da wani ne kuma kr bugawarfa,kawai saiki bude ba tare da kin tambayi waye ba?"
"Ai nasan kai kadaine zai shigo"
"Ba tabbas,hotel ne dont do this again"
"In sha Allah" ta fada kai tsaye kuma cikin sanyi,sai amsar tata tayi masa dadi,a hankali sai ya dinga lalubar bacin ran nashi yana rasawa har zuwa sanda ya dubeta sanda take nannade saman kujera tana ci gaba da duba littafin
"Ki shirya kayanki,nan da gata zaki je naijeria" a ba zata maganar tazo mata,sai ta dago kai tana ware fararen  idanuwanta a kansa tana bude baki cikin tsananin farinciki har batasan sanda tace
"Da gaske?,da gaske kake don Allah"
"Ni abokin wasanki ne" ya fada yana mai fatan ta janye fararen idanuwanta daka kanshi,wani feelings akanta ke son kamashi,idanuwa ya lumshe sanda ta girgiza kai alamun a'a ta janye idanuwan nata daga kanshi,saidai murmushin dake saman fuskarta yaqu boyuwa,sake bude idanuwan nashi yayi a hankali ya azasu kanta,wanda ita bata ma sani ba ta tattara hankalinta ga littafin duk da ba karantawa take ba,zai iya cewa bai taba ganinta cikin farinciki haka ba,sai ya sake maida su ya rufe again,baya son abinda yake ji a kanta yaci gaba da tasiri a kanshi,don matuqar yaci gaba da tasirin to zai jagoranceshi ya aikata koma mene,tun wancan daren zuwa yanzu bai taba samun sukuni ba duk sanda tunanin moment na daren ya fado masa,sai yaji kamar ana mintsini ko tsikarinshi,baiso ya karya alqawarin da ya daukarwa kanshi a kanta,hakan ya sanya tilas ya kwanta duk da baijin bacci,da qyar ya samu bacci ya daukeshi.

*******   ********    ********

      Baki daya ta kasa sukuni tunda ya shaida mata tafiyar,ji take kamar tayi tsuntsuwa ta ganta a gida,har ya fura lura da irin dokin da takeyi,ana ya jibi zata tafi kuwa ta kwashe kusan duk wani abu nata mai muhimmanci tayi parkinga nasa waje guda.

       Ana ya gobe kuwa zata tafi har ya kwanta tana ta zirga zirgan hada komai nata,ya jima kwance cikin bargo yana kallonta cikin kayan bacci,wanda ita har ga Allah ta tsammatar masa bacci,mamakin irin zumudin da take kawai yakeyi,sai tayita sakin murmushi ita kadai.
Chapter 164 · 0% Book details