Sashe 185
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har suka zauna cin abinci alamun bacin ran basu sakeshi ba,hakan ya matuqar taba ranra itama,yana zaune saman dining ya hade hannayenshi waje guda yana dubanta,qoqari yake ya saita kanshi don kada ya shiga haqqinta ko ya sanyata damuwa kamar yadda yaga kuzarinta ya soma raguwa,baki daya warmers din ta bude wanda take qamshi ya cika wajen,sai ta koma kujerar dake daura da shi ta zauna,idonta cikin nashi tana sakar masa murmushi,a hankali ta sanya hannunta saman hancinsa ta ja madaidaicin hancinsa da ya zauna das bisa fuskarshi ya qawata kyawunsa
"Me zaka iya ci ciki mu gani?,kai din cikakken bahaushe ne?ni duka ma fa nakeso ka cinye" ta qarashe maganar taba dage masa girarta,murmushi ya subuce masa lokaci guda,ya raba hannyenshi yana rarraba ido tsakanin kwanukan,abincin da ya jima baici ba kenan,kusan ya manta ma da ita a jerin abinciccika,ya maida kallonshi kanta
"Kina son miji lukuti me qiba kenan" qayataccen murmushi ta saki masa
"Idan na cinye wannan abincin duka yau anan gun zan kwana,bazan iya kai kaina daki ba" dariyar data riqe ce ta subuce mata,ganin yadda ya soma kwatanta yana shafa sumar kanshi
"Dariya kike?,ke zakiji a jikinki,don ba lallai ki iya daukan lukuti ba idan na qara qiba" kunyar maganar ta bata,sai ta soma gunqurin zuba masa abincin yana binta da kallo,komai nata burgeshi yake sake yi duk kwanan duniya,dabi'u da al'adun masu burgewa da kuma mabanbanta kullum yake sake gani wajenta,wasu ya manta da su tana tuna masa su daya bayan daya,wasu yana sane da su saidai baisan inda zaya gansu ba yau gasu cikin gidanshi a gabanshi,spoon ya amsa da niyyar fara ci,sau ta langabe kai tana dubanshu,yau wani irin abu take ji yana fusgarta zuwa gareshi
"I promise to feed you when we r together"
"Thanks" ya fada murmushin na fita a fuskarshi
"No" ta fada tana girgiza kai,ya gane mai take nufi,zuwa yanzu ya fara fahimtarta,tafi qaunar ya sanya mata albarka fiye da godiya,hakan baya rasa nasaba da muhimmancin albarkar wajenta fiye da godiyar,shima hancinta ya ja
"U r smart,barakallu fiki"
"Wa laka" itama ta maida masa,ta debi abinci ta kai bakinshi da cokali,sai yasa hannunshi ya amshe cokalin ya ajjiye
"Da hannunki nakeso ki bani" ba musu ta sanya hannun,ta miqa bakinsa yayi bismillah sannan ya soma amsa,kasa cewa komai yayi sai jinjina kai da yake a fakaice,wasa wasa sai gashi yaci leda hudu,ya dubeta suka hada idanu sai suka qyalqyale da dariya baki dayansu
"U r the best cooker apart from my mom da na sani" yabon yayi mata dadi qwarai,sai ta jangi jug na tana tsiyaya masa lemon da tunda ta fara zubashi ya zuba masa idanu,ta cika glasa cup ta kai bakinsa,ya kurba,sai ya cire yana duban cup din tare da hadiya na bkinshi
"Kunun aya?" Kai ta gyada masa,dariya ta subuce masa,yayi qas da murya
"Kinsan barnar da yake min ko?,halan kin shirya gyarota" ido ta zaro don har ga Allah batasan komai a kai ba,matsowa ya sake yi dab da ita,cikin kunnuwanta ya gaya mata komai,kunya ta sanyata sunne kai,sai yayi relax jikin kujera yana dubanta murmushi na fita a fuskarshi
"Can you remember our first night?,the day i start......." Sai ya kasa qarasawa yana dariya
"Hamza......shi ya hadani da shi,ashe gata yayimin,ya zama silar shigata wata sabuwar duniya mai qunshe da ababan mamaki da jin dadi masu tarin yawa,sai ta dire cup din tana dariya idanunta a qasa,riqe hannun nata yayi caraf yana fadin
"Saikin qarasa bani ai,kin dandana min zuma a baki kuma ki janye,u r at my side ai,nasan ba matsala ko?" Haka ta dinga zuba masa yana shanyewa,ya masa dadi qwarai da gaske,cup biyu yasha qwarara sannan ya haqura jin yadda ya qoshi,ya jima baiji qoshi a jikinsa irin hakan ba.
Darene data kaishi wata duniya da bata taba kaishi ba,duk wani hanya data sani da wadda ya koya mata wadda ke tafi da mutum sai data masa,abinda ya sake sukurkutashi kenan,ya kuma sanyashi tafiya mai nisan gaske cikin kogin sonta.
Suna idar da sallahr asuba ta dauke wayoyinshi baki daya ta kashe,taci alwashin maida shi mutum mai cikakken lokacin kansa,tayi alqawarin rage masa jibgin sabgogi da hidindimu da yake wuni yi,walau yana kano abuja america ko dubai,babu hutu cikin lokutansa baki daya,tamkar kuwa ta sani yau qarfe goma na safiyar zaiyi taro da dukka ma'aikatan asibitinsa dake abuja,sannan sunyi da hamza zasu je yaga gonakin da suka siya domin fara noman auduga,wanda hakan zai sake habaka kamfaninsu,tare da rage musu kudaden da suke kashewa wajen sayen zare da auduga wajen wasu kamfanoni na waje,hakan kuma zai kuma samar da ayyuka ga matasan qasarmu.
Tana gaban mudubi tana qarasa daurin dankwalinta goma na safe sanda almustapha ke kwance saman gado yana bacci nannade cikin bargo,cikin cikakkiyar nutsuwa da kwanciyar hankali,knocking aka fara da qarfi tamkar an samu bangon dakin,barin abinda take yi tayi tana tunanin waye?,sai ta dauki turarukanta ta fesa sannan ta nufi qofar ta bude a hankali,su'ad ce a wani birkice,babu wannan kwalliyar kwata kwata tattare da ita,neman hanya take kawai zata sanya kanta cikin dakin,lura da haka ya sanya sumayya rage fadin qofar ta hanyar karo qofar ta riqeta a hannu,sauran wajen da yayi ragowa kuma ta tsaya tana dubanta
"Anty su'ad lafiya kuwa?"kallo ta watsa mata mai siffar harara
"bake nake nema ba matsa kiban waje" murmushi ta saki cikin kwanciyar hankali da nutsuwa
"Kin manta kin shardanta cewa kowa dan girkinsa ba ruwan miji da 'yar uwata?,ke kika fadi hakan,amma kasancewar nasan akwai haqqinki rataye bisa wuyanshi bazan hanashi ganinki ba,amma banda yanzun don Allah,don bacci yake,yana buqatar isashshen hutu,amma idan ya tashi na gaya masa"
"Ke baki isa ki hanani ganinsa ba wallahi" ta fada a zafafe,sai kawai sumayya taja baya ta kuma maida murfin qofar ta rufe.
Baqinciki ya hanata aikata komai,sai kawai ta juya ta sauka tana laluben wayarta ta nemi almustaphan kawai,saidai kash ta buga rashin sa'a tunda sumayya ta jima da kashesu,batayi tsammanin ya farka fa,saidai tana waiwayowa suka hada ido da shi,yana zaune daram yana kallonta,hannunsa ya bude mata fuskarshi a dan tsuke cike da miskilanci,a nutse ta iso gareshi ta fada jikinsa a tausashe ya maida hannu ya rufe
"Hausa girl" ya rada mata a kunneta,shigar atamfa tana mata kyau tana kuma burgeshi,dalili da ya sanya take yawanyi itama kenan
"Meyw dalilin kashemin wayoyi,sannan aka qi tashina?,kina son na soma halin da ba nawa ba karya alqawari?" Ya fada har yanzu tana jikinsa,kai ta girgiza
"You need some rest"
"I know,kuma nima bansan fitan,ya kamata ace idan nazo qasata ina hutawa sa iyalaina kadai basai wani sabgar ya shigo cikin wadan nan lokutan ba,sai yanzu na gane muhimmancin hakan.....amma duk da haka zanje meeting da ma'aikata a asibiti,so ki shirya,zaki min rakiya?"kai ta gyada masa,sosai taji dadi,ko banza zata miqe qafa,tunda tazo banda gidan anty dije bata je ko ina ba
"Ok,shirya min ruwan wanka"
"Jiranka ma yake" ta furta itama cikin salon rada,sai ya matseta cikin jikinsa
"Kina son hanamu fitan ma kenan baki daya ko?" Da sauri ta girgiza kai tana dariya,don tasan me tayi masa
"Dagani to" ya fada yana dubanta,ta janye jikinta a hankali sannan ya miqe ya shige toilet din.
Tare suke saukowa baki dayansu,cikin shigar cikakkiyar bahaushiya take,plain zani da riga fitted,tayi daurinta das biasa kanta,lullubinta har saman ka,yayin da ya kasance shi kuma cikin yadin kufta da aka yiwa aiki irin na gidan sarauta,cikin kayan da ya bayar ayi masa tun daga randa ya fahimcu ire iren shigar na burgeshi,
"Wait" ya fadi yana nufar wajen su'ad,gefan kujera ta samu ta zauna tana tsumayinsa.
Fitowarta daga wanka kenan daure da towel,tana ta qamshin shower gel dinta mai matuqar tsada da take amfani da shi duk din saboda tattalin fatarta,ranta a quntace yayi sallama,ciki ciki ta amsa shima don tasan yadda suke qarewa da shi idan bata amsa ba,abu na farko data fara shine qorafin taje wajensa sumayyan ta mata rashin kunya,ta kira wayoyinshi kuma a kashe,bai ko tanka mata ba ya duba ciwukan nata
"Suna zafi har yanzu?"kai ta girgiza tana tabe baki,ya qarasa bakin mudubinta ya ajjiye mata kudi
"baka ce komai ba na maka magana but ka share" ita batasan bacin ran mutum bane?,a nutse hannayensa cikin aljihunsa ya dawo inda take tsaye
"Bakisan abinda kika aikata jiya ba dai dai bane?"kafada ta daga
"to sai me,kishinka nake kuma dole na nuna"idanunshi ya zuba mata wanda ya sanyata rusunar dole ta janye nata idanun,cikin bacin rai yace
"Wannan ba kishi bane hauka ne,kin dauki aqidar da ba taki ba kin yafawa kanki?,daga ranki ya baci saiki hau yanka kanki koki yanka wasu?,zubar jini wannan baki daukeshi a bakin komai ba?,zan miki warning na qarshe,kinyi na farko kinyi na biyu,kada ki yarda ki sake na uku,if not zan dauki mataki a kanki,take note" ya fadi yana juyawa ya fice a dakin,tabbas ba qaramin illa baqin al'adu ke mana ba da yaranmu,sai yaji baki daya zaman wata qasar bashi da fa'ida karon farko a rayuwarshi,ya tabbatar sanda suna zuwa islamiyya a america da su'ad bata yaye kanta ta daina zuwa ba wasu halayen nata ba zasu ta'azzara har haka ba.
Wajen ummee suka fara biya,cikin farinciki ta tarbesu suka gaidata,farinciki fal ranta,yau almustapha ne ya kusa dosar sati biyu a abuja bai nemi komawa inda ya fito ba,wanda ta tabbatar da da ne da tuni ya koma din,a qalla ma yayi kwanaki uku kacal,sallama suka yi mata ta rakasu da addu'a suka fice,suka gaida anty mama sannan suka wuce,don baba ranar baya nan,sun fita shi da su mahmoud angwaye.
"Me zaka iya ci ciki mu gani?,kai din cikakken bahaushe ne?ni duka ma fa nakeso ka cinye" ta qarashe maganar taba dage masa girarta,murmushi ya subuce masa lokaci guda,ya raba hannyenshi yana rarraba ido tsakanin kwanukan,abincin da ya jima baici ba kenan,kusan ya manta ma da ita a jerin abinciccika,ya maida kallonshi kanta
"Kina son miji lukuti me qiba kenan" qayataccen murmushi ta saki masa
"Idan na cinye wannan abincin duka yau anan gun zan kwana,bazan iya kai kaina daki ba" dariyar data riqe ce ta subuce mata,ganin yadda ya soma kwatanta yana shafa sumar kanshi
"Dariya kike?,ke zakiji a jikinki,don ba lallai ki iya daukan lukuti ba idan na qara qiba" kunyar maganar ta bata,sai ta soma gunqurin zuba masa abincin yana binta da kallo,komai nata burgeshi yake sake yi duk kwanan duniya,dabi'u da al'adun masu burgewa da kuma mabanbanta kullum yake sake gani wajenta,wasu ya manta da su tana tuna masa su daya bayan daya,wasu yana sane da su saidai baisan inda zaya gansu ba yau gasu cikin gidanshi a gabanshi,spoon ya amsa da niyyar fara ci,sau ta langabe kai tana dubanshu,yau wani irin abu take ji yana fusgarta zuwa gareshi
"I promise to feed you when we r together"
"Thanks" ya fada murmushin na fita a fuskarshi
"No" ta fada tana girgiza kai,ya gane mai take nufi,zuwa yanzu ya fara fahimtarta,tafi qaunar ya sanya mata albarka fiye da godiya,hakan baya rasa nasaba da muhimmancin albarkar wajenta fiye da godiyar,shima hancinta ya ja
"U r smart,barakallu fiki"
"Wa laka" itama ta maida masa,ta debi abinci ta kai bakinshi da cokali,sai yasa hannunshi ya amshe cokalin ya ajjiye
"Da hannunki nakeso ki bani" ba musu ta sanya hannun,ta miqa bakinsa yayi bismillah sannan ya soma amsa,kasa cewa komai yayi sai jinjina kai da yake a fakaice,wasa wasa sai gashi yaci leda hudu,ya dubeta suka hada idanu sai suka qyalqyale da dariya baki dayansu
"U r the best cooker apart from my mom da na sani" yabon yayi mata dadi qwarai,sai ta jangi jug na tana tsiyaya masa lemon da tunda ta fara zubashi ya zuba masa idanu,ta cika glasa cup ta kai bakinsa,ya kurba,sai ya cire yana duban cup din tare da hadiya na bkinshi
"Kunun aya?" Kai ta gyada masa,dariya ta subuce masa,yayi qas da murya
"Kinsan barnar da yake min ko?,halan kin shirya gyarota" ido ta zaro don har ga Allah batasan komai a kai ba,matsowa ya sake yi dab da ita,cikin kunnuwanta ya gaya mata komai,kunya ta sanyata sunne kai,sai yayi relax jikin kujera yana dubanta murmushi na fita a fuskarshi
"Can you remember our first night?,the day i start......." Sai ya kasa qarasawa yana dariya
"Hamza......shi ya hadani da shi,ashe gata yayimin,ya zama silar shigata wata sabuwar duniya mai qunshe da ababan mamaki da jin dadi masu tarin yawa,sai ta dire cup din tana dariya idanunta a qasa,riqe hannun nata yayi caraf yana fadin
"Saikin qarasa bani ai,kin dandana min zuma a baki kuma ki janye,u r at my side ai,nasan ba matsala ko?" Haka ta dinga zuba masa yana shanyewa,ya masa dadi qwarai da gaske,cup biyu yasha qwarara sannan ya haqura jin yadda ya qoshi,ya jima baiji qoshi a jikinsa irin hakan ba.
Darene data kaishi wata duniya da bata taba kaishi ba,duk wani hanya data sani da wadda ya koya mata wadda ke tafi da mutum sai data masa,abinda ya sake sukurkutashi kenan,ya kuma sanyashi tafiya mai nisan gaske cikin kogin sonta.
Suna idar da sallahr asuba ta dauke wayoyinshi baki daya ta kashe,taci alwashin maida shi mutum mai cikakken lokacin kansa,tayi alqawarin rage masa jibgin sabgogi da hidindimu da yake wuni yi,walau yana kano abuja america ko dubai,babu hutu cikin lokutansa baki daya,tamkar kuwa ta sani yau qarfe goma na safiyar zaiyi taro da dukka ma'aikatan asibitinsa dake abuja,sannan sunyi da hamza zasu je yaga gonakin da suka siya domin fara noman auduga,wanda hakan zai sake habaka kamfaninsu,tare da rage musu kudaden da suke kashewa wajen sayen zare da auduga wajen wasu kamfanoni na waje,hakan kuma zai kuma samar da ayyuka ga matasan qasarmu.
Tana gaban mudubi tana qarasa daurin dankwalinta goma na safe sanda almustapha ke kwance saman gado yana bacci nannade cikin bargo,cikin cikakkiyar nutsuwa da kwanciyar hankali,knocking aka fara da qarfi tamkar an samu bangon dakin,barin abinda take yi tayi tana tunanin waye?,sai ta dauki turarukanta ta fesa sannan ta nufi qofar ta bude a hankali,su'ad ce a wani birkice,babu wannan kwalliyar kwata kwata tattare da ita,neman hanya take kawai zata sanya kanta cikin dakin,lura da haka ya sanya sumayya rage fadin qofar ta hanyar karo qofar ta riqeta a hannu,sauran wajen da yayi ragowa kuma ta tsaya tana dubanta
"Anty su'ad lafiya kuwa?"kallo ta watsa mata mai siffar harara
"bake nake nema ba matsa kiban waje" murmushi ta saki cikin kwanciyar hankali da nutsuwa
"Kin manta kin shardanta cewa kowa dan girkinsa ba ruwan miji da 'yar uwata?,ke kika fadi hakan,amma kasancewar nasan akwai haqqinki rataye bisa wuyanshi bazan hanashi ganinki ba,amma banda yanzun don Allah,don bacci yake,yana buqatar isashshen hutu,amma idan ya tashi na gaya masa"
"Ke baki isa ki hanani ganinsa ba wallahi" ta fada a zafafe,sai kawai sumayya taja baya ta kuma maida murfin qofar ta rufe.
Baqinciki ya hanata aikata komai,sai kawai ta juya ta sauka tana laluben wayarta ta nemi almustaphan kawai,saidai kash ta buga rashin sa'a tunda sumayya ta jima da kashesu,batayi tsammanin ya farka fa,saidai tana waiwayowa suka hada ido da shi,yana zaune daram yana kallonta,hannunsa ya bude mata fuskarshi a dan tsuke cike da miskilanci,a nutse ta iso gareshi ta fada jikinsa a tausashe ya maida hannu ya rufe
"Hausa girl" ya rada mata a kunneta,shigar atamfa tana mata kyau tana kuma burgeshi,dalili da ya sanya take yawanyi itama kenan
"Meyw dalilin kashemin wayoyi,sannan aka qi tashina?,kina son na soma halin da ba nawa ba karya alqawari?" Ya fada har yanzu tana jikinsa,kai ta girgiza
"You need some rest"
"I know,kuma nima bansan fitan,ya kamata ace idan nazo qasata ina hutawa sa iyalaina kadai basai wani sabgar ya shigo cikin wadan nan lokutan ba,sai yanzu na gane muhimmancin hakan.....amma duk da haka zanje meeting da ma'aikata a asibiti,so ki shirya,zaki min rakiya?"kai ta gyada masa,sosai taji dadi,ko banza zata miqe qafa,tunda tazo banda gidan anty dije bata je ko ina ba
"Ok,shirya min ruwan wanka"
"Jiranka ma yake" ta furta itama cikin salon rada,sai ya matseta cikin jikinsa
"Kina son hanamu fitan ma kenan baki daya ko?" Da sauri ta girgiza kai tana dariya,don tasan me tayi masa
"Dagani to" ya fada yana dubanta,ta janye jikinta a hankali sannan ya miqe ya shige toilet din.
Tare suke saukowa baki dayansu,cikin shigar cikakkiyar bahaushiya take,plain zani da riga fitted,tayi daurinta das biasa kanta,lullubinta har saman ka,yayin da ya kasance shi kuma cikin yadin kufta da aka yiwa aiki irin na gidan sarauta,cikin kayan da ya bayar ayi masa tun daga randa ya fahimcu ire iren shigar na burgeshi,
"Wait" ya fadi yana nufar wajen su'ad,gefan kujera ta samu ta zauna tana tsumayinsa.
Fitowarta daga wanka kenan daure da towel,tana ta qamshin shower gel dinta mai matuqar tsada da take amfani da shi duk din saboda tattalin fatarta,ranta a quntace yayi sallama,ciki ciki ta amsa shima don tasan yadda suke qarewa da shi idan bata amsa ba,abu na farko data fara shine qorafin taje wajensa sumayyan ta mata rashin kunya,ta kira wayoyinshi kuma a kashe,bai ko tanka mata ba ya duba ciwukan nata
"Suna zafi har yanzu?"kai ta girgiza tana tabe baki,ya qarasa bakin mudubinta ya ajjiye mata kudi
"baka ce komai ba na maka magana but ka share" ita batasan bacin ran mutum bane?,a nutse hannayensa cikin aljihunsa ya dawo inda take tsaye
"Bakisan abinda kika aikata jiya ba dai dai bane?"kafada ta daga
"to sai me,kishinka nake kuma dole na nuna"idanunshi ya zuba mata wanda ya sanyata rusunar dole ta janye nata idanun,cikin bacin rai yace
"Wannan ba kishi bane hauka ne,kin dauki aqidar da ba taki ba kin yafawa kanki?,daga ranki ya baci saiki hau yanka kanki koki yanka wasu?,zubar jini wannan baki daukeshi a bakin komai ba?,zan miki warning na qarshe,kinyi na farko kinyi na biyu,kada ki yarda ki sake na uku,if not zan dauki mataki a kanki,take note" ya fadi yana juyawa ya fice a dakin,tabbas ba qaramin illa baqin al'adu ke mana ba da yaranmu,sai yaji baki daya zaman wata qasar bashi da fa'ida karon farko a rayuwarshi,ya tabbatar sanda suna zuwa islamiyya a america da su'ad bata yaye kanta ta daina zuwa ba wasu halayen nata ba zasu ta'azzara har haka ba.
Wajen ummee suka fara biya,cikin farinciki ta tarbesu suka gaidata,farinciki fal ranta,yau almustapha ne ya kusa dosar sati biyu a abuja bai nemi komawa inda ya fito ba,wanda ta tabbatar da da ne da tuni ya koma din,a qalla ma yayi kwanaki uku kacal,sallama suka yi mata ta rakasu da addu'a suka fice,suka gaida anty mama sannan suka wuce,don baba ranar baya nan,sun fita shi da su mahmoud angwaye.