Sashe 79
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tunda suka shigo falon gabanta ke mugun faduwa,sosai ta dinga qoqarin baiwa kanta qwarin gwiwa saboda haka sai ta sadda kanta qasa har suka qaraso cikin falon suna sallama,dattijon ne ya amsa da wasu daga cikin mazauna falon,idonsa na kan antyn da sumayya har suka qaraso,gefe ta samu ta zauna daga qasan carfet din,da sauri baabaa yace
"A'ah,tashi ki koma saman kujera mana" murmushi tayi kanta na qasa,ta soma gaidashi tare da yi masa sannu da zuwa,fuska sake tamkar ya santa ya amsa mata,anty ta dubeshi
"Nasan baka santa ba" sake dubanta yayi yana gyada kai
"Gaskiya kam,koda na santa to ta kwanta min,kinsan shekarun sun fara turawa sai a hankali" sauran dake zaune sukayi danyi dariya banda mutum daya da tun shigowarsu ya dauke kansa ya maida hankalinsa kacokam kan wayarsa yana tura saqonni,hakanan ransa yake a bace.
"Itace wadda ka dinga bamu labari ka kwashi girki na kwana ashirin ka dinga zabga santi" baki daya dariya suka kuma saki wanda hakan ya dan ja hankalinsa,har ya sanyashi daga kai ya mata kallo daya tak ya sake maidawa kan wayarsa yaci gaba da abinda yake
"Masha Allah,Allah yayi albarka,naji dadin abinci kam qwarai da gaske,Allah yayi albarka"
"Amin baabaa,na gode" ta fada cikin jin dadi bisa dabi'arta ta son na gaba da ita wanda take saka ran addu'arsa zata iya binsa ya sa mata albarka,hannu ya miqawa husna wadda ke hannun sumayya,ta kuwa lafe a jikinta tamkar ta santa,qememe taqi zuwa,sai ya zura hannunshi cikin aljihun rigarsa ya zaro alewa,kasancewarsa mai yawan kyauta,musamman a irin wannan lokaci da jikokinsa ke kasancewa a gidan tare da shi,hakan ya sanya baya rabo da alewa da sabbin kudi,miqa mata yayi take kuwa ta tafi gurin nasa,hannu yasa ya dagata yana dariya jama'ar falon na tayashi,tsaki ya ja qasa qasa yana miqewa,shikam bai san me yasa abun dariya bai yiwa su mu'azzam wuya ba,shi baki daya ma baiga abun dariya ba,yarinyar ma tunda ta shigo baki daya ma yaji ransa ya baci,musamman katse musu hanzarin da tayi kan muhimmin batun da suke tattaunawa,tun dazun dama yake addu'ar kada wani ya shigo saboda baison abinda zai katse masa bayanin da ya daukowa baban,ya san mutum ne shi mai mutunta baqo,kome yakeyi yana iya katsewa ya saurari baqonsa,sarai baaban ya ganshi amma sai ya qyaleshi,yasan halin kayansa sarai,da idanu ya rakashi har ya fice,ganin ya fita ya sanya sauran miqewa
"Baabaa kada fa ya tafi ya barmu"
"Jeku,don tsaf zai iya aikatawa,musamman da kun zo da tsarin da baiyi masa ba"dariya suka yi sannan sukayi sallama da baban suka fice,tattambayarta baabaa yayi kan wasu abubuwan tana amsa masa,har alokacin kanta na duqe,ta miqe bayan wasu mintuna ta masa sallama,sai anty ta ajjiye masa kwanon tana masa bayani,qwarai da gaske yaji dadi,domin shi mutum ne da baya raina alkhairi komai qanqantarsa,koda yafi qarfin abu ka bashi shi yana ganin girmansa abun agunsa,dakatar da ita yayi yana fadin
"bari na baki zamzam da bagaruwa ko"
"To" ta fada tana murmushi,antyn yama kwatance cikin dakinsa,cikin sakanni ta shiga ta fito da wata jarka
"Ba ita ba,zamzam din da nayi dawafi da shi" mamaki antyn tayi,don irin wannan zam zam din ba kowa yake bawa shi ba,dashi yaje dawafi da addu'o'i,yakam zama magani cikin ikon Allah ga duk wanda ke jin lalura ya bashi yayi amfani da shi,duk da kasancewarsa tantagaryar dan boko amma akwai ilimin addini mai yawa tattare da shi,jarka ce guda tayi tsawon ta faro qarami ya zuba mata,sannan ya cika mata leda da bagaruwa da dabino,godiya tama baban sosai ta kuma ji dadin kyautar tasa,tare suka fito da antyn
"Anty zan koma"
"Haba daga shigowarki,kodai tsoron kike ji kamar yadda mahmoud ya fada,naga ko mutuniyar taki amira baki gani na,bayan ita tunda muka dawo take maganarki,na tabbata baqi ke suka hanata fitowa da tuni kin ganta,sannan baki shiga kin gaida ummee ba" sam bata so antyn ta debo mata wannan bayanin ba,amma sai ta sadda kai tace
"To,bari na shiga"
"Yauwa,ki gaida ummam khalipan don Allah idan kin koma,nasan itama baqi ke suka hanata leqowa,dukkanmu irin wannan lokacin sai haquri baqi muke ba dauke qafa"
"To zataji" ta furta sanda antyn ke yunqurin amsar husna,nan ma qi tayi,dariya antyn ta dinga
"Shikenan kuje da ita kin samu qanwa,idan tayi kuka ko laila kaya bada ta kawota"
"To anty" tafada tana dariya tare da yin gaba.
Baki daya falon ya sauya ba kamar waccan karon data shigo shi ba,da alama gyaran azumin ne,komai ya canza a falon,saidai tun kafin ka kai ga qarasowa cikin falon zaka jiyo muryarta,tana tsaye tsakiyar falon hannunta riqe a qugu tana zuba masifa,bisa alamu da 'yanmatan dake zaune a falon take,sun kusa su hudu harda amira dake gefe tana shan ice cream hankalinta kwance kamar ma bata falon
"To bani cike da iskanci,ran kowa sai ya baci wallahi,bazan dauki raini ba,kuma wanda ya fasa karbo greeting cards na 'yammata yana kawowa bai cika ba mu zuba ni da ku,aikin banza kawai" tana gamawa ta juya a fusace tana taku kan tsireren takalminta mai igiya,kowa sanye da suturar al'ada banda ita,wando ne a jikinta irin straight leg din nan,sai riga one shoulder a jikinta,gefe sumayyan ta janye tana dubanta,dariya taji 'yammatan suka saki bayan fitar tata banda amira fake ci gaba da abinda take,daya daga cikinsu tace
"Duk wayon amarya wallahi sai an sha manta"sai a lokacin sumayyan ta maimaita sallamarta,amira ce ta amsa cikin fara'a ta miqe
"amiran umman khalipha kinsan kina raina,sannu ga guri zauna" tana mata nuni da wata kujera dake can gefe babu kowa,qarasawa tayi tana zaman amira ta sake cewa
"Ina kika tsinto wannan uwar qyuyar,daina kallona kina wani saukar da kai ban daukanki zanyi ba nima" ta fada tana dan daga murya da zaro ido da alamu tana jin haushin irin qyuyar husnar,murmushi sumayya ta saki tana dafe kan husna wadda ta kwantar da kanta aqirjinta
"Dole fa ta miki qyuya,kina mata irin haka"
"Allah bata da kirki" gaisawa sukayi ta mata sannu da zuwa sannan ta tambayi ummin
"Ummi na sama,bari na miki kiranta"
"To" ta amsa,satar kallonta 'yammatan suka ci gaba da yi itakam hankalinta na kan husna tana mata wasa a haka amira ta dawo ta tadda su,ba dadewa ummin ta sauko,abinda sumayya ta dan lura da shi shine,ummen irin mutanen nan ne da basu son hayaniya da yawan surutu.
A mutunce ta gaidata ta amsa mata fuska a sake itama tana son daukar husna,saidai itama husnar ta watsa mata qasa a idanu kamar sauran,tilas ta barta sumayya na mamakin qyuyar yarinyar,bata wani jima ba tayi musu sallama ta fice sabida yadda 'yammatan ke kallonta.
Anty dije ma tayi mamakin ganinta da husnar,goyata tayi bayan ta bata abinci,ba jimawa kuwa tayi bacci a bayan nata,gab da magariba sukaji sallama a falon,sumayyan ce ta fito goye da husnar tana amsawa,magidanciya ce wadda zata doshi shekara talatin da hudu,fuska a sake sumayya tayi mata sannu da zuwa,leqa bayan sumayyab tayi tana riqe baki cikin fara'a
"Wai lallai raino yayi dadi,ashe kam da gaske tana nan din,ni ina can hankalina na kanki uwar qyuya ashe ke kin haye bayan mutane kina bacci abinki" dariya sumayya ta danyi sai alokacin ta fuskanci mamarta ce,yunqurin saukota tayi tana fadin bari ta bata ita
"A'ah,barta mana idan ba'a matsa miki ba,haba sai kace bare,da nan da gidan baabaa ai duka daya ne,kawai dai idan ta tashine nasam zata taba miki darunta,sai azo a dauketa"
"To" ta amsa tana gyara goyon
"Ina anty dije" ta ambaceta da sunan da suke kiranta a kano sabanin yadda taji mutan gidan na kiranta da umman khalipha
"Yanzun nan ta shiga wanka"
"Sarkin kwalliya wa miji,idan ta fito kice ina gaidata" ta fada da sigar zolaya,bisa alamu sun saba sosai.
Bata farka ba sai bayan magariba sumayyan ma na shirin tada isha'i,daukota tayi daga kan gadon ta cire mata pampers tare da zuba abinci ta bata,sai da taga ta qoshi sannan ta sabata a kafada ta zura hijabin sallarta wanda ke kusan sharar qasa tace khalipha yazo ya rakata.
Tarwai gidan da haske kamar kowanne lokaci,saidai yau akwai yawaitar mutane a harabar gidan,sashen anty maamaa ta shiga tacu sa'a ko ta tadda maman husnar,amsarta tayi tana yiwa sumayyan sannu tare da godiya.
"A'ah,tashi ki koma saman kujera mana" murmushi tayi kanta na qasa,ta soma gaidashi tare da yi masa sannu da zuwa,fuska sake tamkar ya santa ya amsa mata,anty ta dubeshi
"Nasan baka santa ba" sake dubanta yayi yana gyada kai
"Gaskiya kam,koda na santa to ta kwanta min,kinsan shekarun sun fara turawa sai a hankali" sauran dake zaune sukayi danyi dariya banda mutum daya da tun shigowarsu ya dauke kansa ya maida hankalinsa kacokam kan wayarsa yana tura saqonni,hakanan ransa yake a bace.
"Itace wadda ka dinga bamu labari ka kwashi girki na kwana ashirin ka dinga zabga santi" baki daya dariya suka kuma saki wanda hakan ya dan ja hankalinsa,har ya sanyashi daga kai ya mata kallo daya tak ya sake maidawa kan wayarsa yaci gaba da abinda yake
"Masha Allah,Allah yayi albarka,naji dadin abinci kam qwarai da gaske,Allah yayi albarka"
"Amin baabaa,na gode" ta fada cikin jin dadi bisa dabi'arta ta son na gaba da ita wanda take saka ran addu'arsa zata iya binsa ya sa mata albarka,hannu ya miqawa husna wadda ke hannun sumayya,ta kuwa lafe a jikinta tamkar ta santa,qememe taqi zuwa,sai ya zura hannunshi cikin aljihun rigarsa ya zaro alewa,kasancewarsa mai yawan kyauta,musamman a irin wannan lokaci da jikokinsa ke kasancewa a gidan tare da shi,hakan ya sanya baya rabo da alewa da sabbin kudi,miqa mata yayi take kuwa ta tafi gurin nasa,hannu yasa ya dagata yana dariya jama'ar falon na tayashi,tsaki ya ja qasa qasa yana miqewa,shikam bai san me yasa abun dariya bai yiwa su mu'azzam wuya ba,shi baki daya ma baiga abun dariya ba,yarinyar ma tunda ta shigo baki daya ma yaji ransa ya baci,musamman katse musu hanzarin da tayi kan muhimmin batun da suke tattaunawa,tun dazun dama yake addu'ar kada wani ya shigo saboda baison abinda zai katse masa bayanin da ya daukowa baban,ya san mutum ne shi mai mutunta baqo,kome yakeyi yana iya katsewa ya saurari baqonsa,sarai baaban ya ganshi amma sai ya qyaleshi,yasan halin kayansa sarai,da idanu ya rakashi har ya fice,ganin ya fita ya sanya sauran miqewa
"Baabaa kada fa ya tafi ya barmu"
"Jeku,don tsaf zai iya aikatawa,musamman da kun zo da tsarin da baiyi masa ba"dariya suka yi sannan sukayi sallama da baban suka fice,tattambayarta baabaa yayi kan wasu abubuwan tana amsa masa,har alokacin kanta na duqe,ta miqe bayan wasu mintuna ta masa sallama,sai anty ta ajjiye masa kwanon tana masa bayani,qwarai da gaske yaji dadi,domin shi mutum ne da baya raina alkhairi komai qanqantarsa,koda yafi qarfin abu ka bashi shi yana ganin girmansa abun agunsa,dakatar da ita yayi yana fadin
"bari na baki zamzam da bagaruwa ko"
"To" ta fada tana murmushi,antyn yama kwatance cikin dakinsa,cikin sakanni ta shiga ta fito da wata jarka
"Ba ita ba,zamzam din da nayi dawafi da shi" mamaki antyn tayi,don irin wannan zam zam din ba kowa yake bawa shi ba,dashi yaje dawafi da addu'o'i,yakam zama magani cikin ikon Allah ga duk wanda ke jin lalura ya bashi yayi amfani da shi,duk da kasancewarsa tantagaryar dan boko amma akwai ilimin addini mai yawa tattare da shi,jarka ce guda tayi tsawon ta faro qarami ya zuba mata,sannan ya cika mata leda da bagaruwa da dabino,godiya tama baban sosai ta kuma ji dadin kyautar tasa,tare suka fito da antyn
"Anty zan koma"
"Haba daga shigowarki,kodai tsoron kike ji kamar yadda mahmoud ya fada,naga ko mutuniyar taki amira baki gani na,bayan ita tunda muka dawo take maganarki,na tabbata baqi ke suka hanata fitowa da tuni kin ganta,sannan baki shiga kin gaida ummee ba" sam bata so antyn ta debo mata wannan bayanin ba,amma sai ta sadda kai tace
"To,bari na shiga"
"Yauwa,ki gaida ummam khalipan don Allah idan kin koma,nasan itama baqi ke suka hanata leqowa,dukkanmu irin wannan lokacin sai haquri baqi muke ba dauke qafa"
"To zataji" ta furta sanda antyn ke yunqurin amsar husna,nan ma qi tayi,dariya antyn ta dinga
"Shikenan kuje da ita kin samu qanwa,idan tayi kuka ko laila kaya bada ta kawota"
"To anty" tafada tana dariya tare da yin gaba.
Baki daya falon ya sauya ba kamar waccan karon data shigo shi ba,da alama gyaran azumin ne,komai ya canza a falon,saidai tun kafin ka kai ga qarasowa cikin falon zaka jiyo muryarta,tana tsaye tsakiyar falon hannunta riqe a qugu tana zuba masifa,bisa alamu da 'yanmatan dake zaune a falon take,sun kusa su hudu harda amira dake gefe tana shan ice cream hankalinta kwance kamar ma bata falon
"To bani cike da iskanci,ran kowa sai ya baci wallahi,bazan dauki raini ba,kuma wanda ya fasa karbo greeting cards na 'yammata yana kawowa bai cika ba mu zuba ni da ku,aikin banza kawai" tana gamawa ta juya a fusace tana taku kan tsireren takalminta mai igiya,kowa sanye da suturar al'ada banda ita,wando ne a jikinta irin straight leg din nan,sai riga one shoulder a jikinta,gefe sumayyan ta janye tana dubanta,dariya taji 'yammatan suka saki bayan fitar tata banda amira fake ci gaba da abinda take,daya daga cikinsu tace
"Duk wayon amarya wallahi sai an sha manta"sai a lokacin sumayyan ta maimaita sallamarta,amira ce ta amsa cikin fara'a ta miqe
"amiran umman khalipha kinsan kina raina,sannu ga guri zauna" tana mata nuni da wata kujera dake can gefe babu kowa,qarasawa tayi tana zaman amira ta sake cewa
"Ina kika tsinto wannan uwar qyuyar,daina kallona kina wani saukar da kai ban daukanki zanyi ba nima" ta fada tana dan daga murya da zaro ido da alamu tana jin haushin irin qyuyar husnar,murmushi sumayya ta saki tana dafe kan husna wadda ta kwantar da kanta aqirjinta
"Dole fa ta miki qyuya,kina mata irin haka"
"Allah bata da kirki" gaisawa sukayi ta mata sannu da zuwa sannan ta tambayi ummin
"Ummi na sama,bari na miki kiranta"
"To" ta amsa,satar kallonta 'yammatan suka ci gaba da yi itakam hankalinta na kan husna tana mata wasa a haka amira ta dawo ta tadda su,ba dadewa ummin ta sauko,abinda sumayya ta dan lura da shi shine,ummen irin mutanen nan ne da basu son hayaniya da yawan surutu.
A mutunce ta gaidata ta amsa mata fuska a sake itama tana son daukar husna,saidai itama husnar ta watsa mata qasa a idanu kamar sauran,tilas ta barta sumayya na mamakin qyuyar yarinyar,bata wani jima ba tayi musu sallama ta fice sabida yadda 'yammatan ke kallonta.
Anty dije ma tayi mamakin ganinta da husnar,goyata tayi bayan ta bata abinci,ba jimawa kuwa tayi bacci a bayan nata,gab da magariba sukaji sallama a falon,sumayyan ce ta fito goye da husnar tana amsawa,magidanciya ce wadda zata doshi shekara talatin da hudu,fuska a sake sumayya tayi mata sannu da zuwa,leqa bayan sumayyab tayi tana riqe baki cikin fara'a
"Wai lallai raino yayi dadi,ashe kam da gaske tana nan din,ni ina can hankalina na kanki uwar qyuya ashe ke kin haye bayan mutane kina bacci abinki" dariya sumayya ta danyi sai alokacin ta fuskanci mamarta ce,yunqurin saukota tayi tana fadin bari ta bata ita
"A'ah,barta mana idan ba'a matsa miki ba,haba sai kace bare,da nan da gidan baabaa ai duka daya ne,kawai dai idan ta tashine nasam zata taba miki darunta,sai azo a dauketa"
"To" ta amsa tana gyara goyon
"Ina anty dije" ta ambaceta da sunan da suke kiranta a kano sabanin yadda taji mutan gidan na kiranta da umman khalipha
"Yanzun nan ta shiga wanka"
"Sarkin kwalliya wa miji,idan ta fito kice ina gaidata" ta fada da sigar zolaya,bisa alamu sun saba sosai.
Bata farka ba sai bayan magariba sumayyan ma na shirin tada isha'i,daukota tayi daga kan gadon ta cire mata pampers tare da zuba abinci ta bata,sai da taga ta qoshi sannan ta sabata a kafada ta zura hijabin sallarta wanda ke kusan sharar qasa tace khalipha yazo ya rakata.
Tarwai gidan da haske kamar kowanne lokaci,saidai yau akwai yawaitar mutane a harabar gidan,sashen anty maamaa ta shiga tacu sa'a ko ta tadda maman husnar,amsarta tayi tana yiwa sumayyan sannu tare da godiya.