Sashe 156
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har ya kammala shiryawa bata gama ba har sai daya zauna cin abinci sannan ta gama,ta ninke takardar tana murmushi ta daga pillow dinta dake saman kujera ta saka a qasa,yana cin abincin amma a zahirance hankalinsa duka na kanta,baisan me yasa ya damu da abinda takeyi din ba,bayan shi mutum ne da bai damuwa da lamuran da ba nashi ba,sai ta nade qafafunta saman kujeran ra rungume pillow a qirjinta tana satar kallonshi,sau uku suna hada idanu kowa yana basarwa,a na hudun suka kama juna,sai ya gyara zamanshi,cikin yanga kamar wata mace ya soma magana a hankali
"Ina fatan ba damuwa bace ta hanaki bacci kamar yadda kika saba ba?" Kai kawai ta kada masa idanuwanta na duban bezar da aka yiwa filon ado bayan ta dauke idaon nata daga kan abincin da yake ci,tana mamakin ta yadda mutun zai dinga cin wadan nan abunuwan da dare kadai wai sune abincin darensa,banda hutu da kudi da yasa jikinsa da fatarsa murjewa da babu abinda zai hana ya shiga sahun ramammu,saidai babu qashi a jikinsa wanda zai nuna maka ramarsa,amma idan ya samu kulawar data fi haka ba shakka jikinsa sai yafi haka cika,ajjiye spoon din hannunsa yayi
"To me ya hanaki bacci as usual?"motsa bakinta tayi itama a yangance tamkar bata son yin maganar ta maida masa
"nothing"yanayin yadda labbanta da suka sha lips balm suka motsa ya sanyashi tsaida idanuwanshi kansu,sai kuma ya janye yana ci gaba da cin abincin a nutse
"sai haquri,haka nake haka aikina yake"ya sake fada
"ba matsala"ta amsa a taqaice itama,duk da yayi mamakin yadda ta amsa din amma bai nuna ba,zai iya tuna duk sanda su'ad ta kawo masa ziyara ta sameshi cikin aiki haka har ta koma tana mita da qorafi,shi a kan kansa yasan yana hora kanshi da aiki over,saidai yana ganin hakanne ya dace da shi,baiso ya baiwa kansa wata kafa da zaiji wani feeling a jikinsa da zai hanashi sakewa,dubai qasa ce ta cin gashin kai,zaka iya duk harkokin da kaga dama,mata sai kalar wanda ka zaba babu qabilar da babu,mai ko wanne irin kyau kuma,musamman idan kana da abun hannunka har inda kake sana'arka za'a kawo maka tallarsu,kai ko ba'a kawo maka ba su da kansu idan suka samu wargi zasu kawo kansu,musamman idan kayi musu koda ba zaka biya ha zasu iya kasancewa tare da kai,bazai iya tuna adadin mutanen da ya daina hulda da su ta sanadiyyar haka ba,idan kuma yana ganin qimarka ya yanka maka babban warning,(da wannan nakeson jan hankalin matan da mazansu ke tafiye tafiye,ku tsaya tsayin daka ku kula da mazanku,na tabbatar babu kalad matan da basa gani,wadanda sun fimu komai,matuqar akwai fahimtar juna tsakaninki da mai gida kuka zauna yana bakin labarin qasashen da yake zuwa zaki ji irin wadannan labaran,wanda da dama marasa tsoron Allah sun fada harkar neman mata saboda suna ganin suna wata duniyar babu mai ganinsu,ko kuma ke kinyin sakacin da har yaga wata mara kintsin ta burgeshi,wanda tsoron Allah da irin kyautatawar da kike masa shi kadai zai tsallakar da shi,Allah ka tsare ka kiyaye mana musulminmu a duk inda suke).
Kana dubanshi zai yi wuya ka dauka ba bacci yake ba,sakamakon lamo da yayi saman gadon cikin tattausan bargo yana sauraren wani recording na tattaunawar sirri da hamza yayi da qananun ma'aikata yayi recording bada saninsu ba ya turo masa don gano bakin zaren matsalar dake shirin kunno kai a companyn,a tunaninta yayi bacci saboda haka ta miqe ta ajjiye littafin hannunta ta dauki kayan baccinta ta shiga toilet ta sauya
"La haula wala quwwata illa billah...." Ya fada qasa qasa yana jan numfashinsa tare da kulle idanuwansa,ba wani tsiraici bane da rigar baccin saidai yadda ta lafe a fatarta ya fitar da sigarta ya kuma haskata,daga sanda ta fito bai sake fahimtar audion din da yake saurare ba,sai yaci gaba da binta da idanu har ta kai ga yafa mayafin ta kwanta abunta bayan ta gama addu'o'inta,saidai a banza,tamkar bata yafa ba haka yake gani,ya tabbatar bazai sake samun nutsuwa ba matuqar tana a haka,zumbur ya miqe zaune saman gadon,ya miqa hannunshi ya kunna qwan dakin bayan ya rufe jikinsa da bargo,hasken da ya mamaye dakin shi ya farkar da ita
"Nemi hijabin sallarki ki saka,wannan kayan sam basu dace da ke ba" ya fada cikin dakiya yana kau da kai sannan ya gayar filonsa ya maida kansa ya ya kwanta bayan ya kashe wutar dakin,ba musu ta ja hijabin ta zura tana mamakin me maganarshi ke nufi?,ita dai tasan ba aibu a kayanta,asali ma suna da kaurin da yawonta a dakin zata iya,baya ga haka ga mayafi data lullube jikinta da shi,ture tunanin tayi gefe absa dole saboda bacci da yaci qarfinta.
******** ****** *********
Yau kan idanunta aka kawo break din,tana zaune saman kujera lokaci lokaci tana satar kallonshi bayan ta tabbatar ta sanyabtakardarva muhallin da zai fara karo da ita a duk sanda ya buqaci aiki da jakar,hannunta riqe da cuo din tea data hada bata kai ga sha ba,ya fiya ado kamar mace,haka take gulmarsa cikin ranta,tsaf ya kammala shirinsa ya dauki wayoyinshi da jakarsa,da sauri ta isa gabanshi,sai kuna ta rage saurin bayan ta isa dab da shi,cup din ta miqa masa tana kallonshi,shima ita yake kallo,ummee,ummee ce ta fado masa a rai,ita kadai duk duniya har yau ke masa haka,tunawa yayi da wace ita wajen ummee da baba,sai yasa hannun damanshi ya karba sannan ya koma gefan madubi yadan jingina kadan daukar yin hani da shan abu a tsaye daga ma'aiki S A W,a nutse yake kurba yana dubanta kadan kadan inda take zaune tana wasa da yatsun hannunta,baifi rabi ya sha ba ya tako a hankali inda take,wanda bata ji takunshi ba sai qamshinsa gab da ita,ya dire cup din a teburin dake kusa da ita,murya qasa qasa ya furta
"Thanks" ya juya yana niyyar fita
"Ina zan samu layi ina son yin magana da 'yan gida" tsayawa yayi cak,kafin ya daj dawo da baya kadan,ya fidda wayoyinsa dake aljihunsa ya zari daya ya sake dawowa kusa da ita ya ajjiye
"Aro" ya fadi a taqaice kafin ya fice.
Bin wayar tayi da kallo,fara ce qal kamar hannu baya tabata,wayar kanta sai tayi mata kwarjini,saka hannu tayi ta dauka,qamshinsa daya ratsa dukkan wani abu da yake mu'amulanta shi ya kama wayar ita kanta,bata taba ganin waya mai kyau data burgeta haka ba,tasa hannu ta shafa screen din ya bude,kasancewar babu password a kai.
Murmushi tayi ta ajjiye wayar gefe,sai data yi wanka ta karya sannan ta zauna sosai saman kujera ta soma kiran duk wanda zata kira din daya bayan daya ciki kuwa har da ummee wadda ba qaramin murna tayi da jinta ba,ta sake jaddada qorafinta na kullum ta kira almustapha kan ya bata sai yace yana company shin bai hutawa ne shi?.
Tafe yake yana duba wani file da daya daga cikin manyan ma'aikatansu wanda shine mataimakin hamza a sashen da suke kula da irin auduga da zararrukan da suke siya daga wasu kamfanoni,takardun jimillar audugar da suka shigo da su ne yake dubawa,dab da zai shiga elevator sukayi kacibus da hamzan,sai ya miqawa wancan da ake kira ramadan yace anjima ya kawo mishi ya qarasa dubawa,don su kammala lissafin dukkan kudin da suka fita ta wannan fannin.
"Ya dai yau naga kamar kadan so makara baka shigo da wuri ba"
"Jiki da jini ke kawai"
"Gaskiya ne,me kake tunani kan audion daka saurara jiya?"
"Mu qarasa na yi maka bayani", a haka suka qarasa office din.
Kan kujerarsa ya nufa kai tsaye ya zauna yana dora jakarsa saman teburin,yayin da hamza ya fara bude fridge ya dauko ruwa yana sha,qoqarin bude jakar ya fara yi amma mazugin ya cije,ya daga jakar don ganin mai ya hanashi wucewa sai yaga takarda lanqwashe a jiki,cikin mamaki ua ciro takardar ya soma warwareta,rubutu ne a tsare tamkar da injin buga rubutu aka tsara shi,sannu a hankali ya soma bin rubutun yana karantawa,yana karantawa kanshi na shiga duhu,shawarwarine a tsare game da yadda zai warware matsalar kamfanin cikin sauqi,daya bayan daya kowacce kalma dake qunshe cikin takardar mai muhimmanci ce,kanshi bai fita daga duhu ba sai da yazo layin qarshe
"ina fatan alkhairi tare da fatan warwarewar matsalar cikin sauri,saboda ka dawo nutsuwarka,iyalinka na da buqatar zamanka waje daya da kuma samun cikakkiyar nutsuwarka,kulawar ubangiji ta tabbata tattare da kai" sosai kalaman suka dinga ratsashi,sai ya samu kanshi da maimaita kalaman,karon farko a rayuwarshi da ya taba samun wadan nan kalamai masu kyau da tsari daga wajen wata mace dake qarqashin ikonshi,a hankali murmushi ya subuce masa sanda ya kammala karanta sadarar karo na biyar
"Lafiyanka qalau kuwa zaka zauna kana dariya kai kadai,mutumin da murmushin naka ma wataran sai anyi kamar za'a biya kafin a ganshi?"
"Hauka nake" ya bashi amsa kai tsaye cikin gatsali yana gintse fuskarsa tare da miqewa tsaye,takardar ya dunqule zaiyi jifa da ita yana jan tsaki sai kuma ya fasa,ya daga takaddun dake gabanahi ya saka ta a tsakiyarsu,hakanan sai yaji wani sashe na zuciyarsa na bashi qwarin gwiwar gwada amfani da shawarwarin dake qunshe cikin wasiqar,jawo wayar land line yayi dake gabanshi ya fara latsawa,cikin qanqanin lokaci ya bada umarnin tara dukkan ma'aikatan dake cikin kamfanin a babban dakin taro dake kamfanin,freezer ya isa ya ciro ruwan shima yana kurba a hankali,binsa hamza yake kallo kafin yace
"Wai meke faruwa haka musty?"
"Zaka gani" bakinsa yaja yayi shiri,yasan tunda ya fara magana haka a taqaice ba mai sanya shi fadadawa,tilas yayi shiru har sanda aka isar masa da saqon gama haduwar ma'aikatan baki daya sannan ya dubi hamza
"Taso muje,meeting ne na qarshe".
"Ina fatan ba damuwa bace ta hanaki bacci kamar yadda kika saba ba?" Kai kawai ta kada masa idanuwanta na duban bezar da aka yiwa filon ado bayan ta dauke idaon nata daga kan abincin da yake ci,tana mamakin ta yadda mutun zai dinga cin wadan nan abunuwan da dare kadai wai sune abincin darensa,banda hutu da kudi da yasa jikinsa da fatarsa murjewa da babu abinda zai hana ya shiga sahun ramammu,saidai babu qashi a jikinsa wanda zai nuna maka ramarsa,amma idan ya samu kulawar data fi haka ba shakka jikinsa sai yafi haka cika,ajjiye spoon din hannunsa yayi
"To me ya hanaki bacci as usual?"motsa bakinta tayi itama a yangance tamkar bata son yin maganar ta maida masa
"nothing"yanayin yadda labbanta da suka sha lips balm suka motsa ya sanyashi tsaida idanuwanshi kansu,sai kuma ya janye yana ci gaba da cin abincin a nutse
"sai haquri,haka nake haka aikina yake"ya sake fada
"ba matsala"ta amsa a taqaice itama,duk da yayi mamakin yadda ta amsa din amma bai nuna ba,zai iya tuna duk sanda su'ad ta kawo masa ziyara ta sameshi cikin aiki haka har ta koma tana mita da qorafi,shi a kan kansa yasan yana hora kanshi da aiki over,saidai yana ganin hakanne ya dace da shi,baiso ya baiwa kansa wata kafa da zaiji wani feeling a jikinsa da zai hanashi sakewa,dubai qasa ce ta cin gashin kai,zaka iya duk harkokin da kaga dama,mata sai kalar wanda ka zaba babu qabilar da babu,mai ko wanne irin kyau kuma,musamman idan kana da abun hannunka har inda kake sana'arka za'a kawo maka tallarsu,kai ko ba'a kawo maka ba su da kansu idan suka samu wargi zasu kawo kansu,musamman idan kayi musu koda ba zaka biya ha zasu iya kasancewa tare da kai,bazai iya tuna adadin mutanen da ya daina hulda da su ta sanadiyyar haka ba,idan kuma yana ganin qimarka ya yanka maka babban warning,(da wannan nakeson jan hankalin matan da mazansu ke tafiye tafiye,ku tsaya tsayin daka ku kula da mazanku,na tabbatar babu kalad matan da basa gani,wadanda sun fimu komai,matuqar akwai fahimtar juna tsakaninki da mai gida kuka zauna yana bakin labarin qasashen da yake zuwa zaki ji irin wadannan labaran,wanda da dama marasa tsoron Allah sun fada harkar neman mata saboda suna ganin suna wata duniyar babu mai ganinsu,ko kuma ke kinyin sakacin da har yaga wata mara kintsin ta burgeshi,wanda tsoron Allah da irin kyautatawar da kike masa shi kadai zai tsallakar da shi,Allah ka tsare ka kiyaye mana musulminmu a duk inda suke).
Kana dubanshi zai yi wuya ka dauka ba bacci yake ba,sakamakon lamo da yayi saman gadon cikin tattausan bargo yana sauraren wani recording na tattaunawar sirri da hamza yayi da qananun ma'aikata yayi recording bada saninsu ba ya turo masa don gano bakin zaren matsalar dake shirin kunno kai a companyn,a tunaninta yayi bacci saboda haka ta miqe ta ajjiye littafin hannunta ta dauki kayan baccinta ta shiga toilet ta sauya
"La haula wala quwwata illa billah...." Ya fada qasa qasa yana jan numfashinsa tare da kulle idanuwansa,ba wani tsiraici bane da rigar baccin saidai yadda ta lafe a fatarta ya fitar da sigarta ya kuma haskata,daga sanda ta fito bai sake fahimtar audion din da yake saurare ba,sai yaci gaba da binta da idanu har ta kai ga yafa mayafin ta kwanta abunta bayan ta gama addu'o'inta,saidai a banza,tamkar bata yafa ba haka yake gani,ya tabbatar bazai sake samun nutsuwa ba matuqar tana a haka,zumbur ya miqe zaune saman gadon,ya miqa hannunshi ya kunna qwan dakin bayan ya rufe jikinsa da bargo,hasken da ya mamaye dakin shi ya farkar da ita
"Nemi hijabin sallarki ki saka,wannan kayan sam basu dace da ke ba" ya fada cikin dakiya yana kau da kai sannan ya gayar filonsa ya maida kansa ya ya kwanta bayan ya kashe wutar dakin,ba musu ta ja hijabin ta zura tana mamakin me maganarshi ke nufi?,ita dai tasan ba aibu a kayanta,asali ma suna da kaurin da yawonta a dakin zata iya,baya ga haka ga mayafi data lullube jikinta da shi,ture tunanin tayi gefe absa dole saboda bacci da yaci qarfinta.
******** ****** *********
Yau kan idanunta aka kawo break din,tana zaune saman kujera lokaci lokaci tana satar kallonshi bayan ta tabbatar ta sanyabtakardarva muhallin da zai fara karo da ita a duk sanda ya buqaci aiki da jakar,hannunta riqe da cuo din tea data hada bata kai ga sha ba,ya fiya ado kamar mace,haka take gulmarsa cikin ranta,tsaf ya kammala shirinsa ya dauki wayoyinshi da jakarsa,da sauri ta isa gabanshi,sai kuna ta rage saurin bayan ta isa dab da shi,cup din ta miqa masa tana kallonshi,shima ita yake kallo,ummee,ummee ce ta fado masa a rai,ita kadai duk duniya har yau ke masa haka,tunawa yayi da wace ita wajen ummee da baba,sai yasa hannun damanshi ya karba sannan ya koma gefan madubi yadan jingina kadan daukar yin hani da shan abu a tsaye daga ma'aiki S A W,a nutse yake kurba yana dubanta kadan kadan inda take zaune tana wasa da yatsun hannunta,baifi rabi ya sha ba ya tako a hankali inda take,wanda bata ji takunshi ba sai qamshinsa gab da ita,ya dire cup din a teburin dake kusa da ita,murya qasa qasa ya furta
"Thanks" ya juya yana niyyar fita
"Ina zan samu layi ina son yin magana da 'yan gida" tsayawa yayi cak,kafin ya daj dawo da baya kadan,ya fidda wayoyinsa dake aljihunsa ya zari daya ya sake dawowa kusa da ita ya ajjiye
"Aro" ya fadi a taqaice kafin ya fice.
Bin wayar tayi da kallo,fara ce qal kamar hannu baya tabata,wayar kanta sai tayi mata kwarjini,saka hannu tayi ta dauka,qamshinsa daya ratsa dukkan wani abu da yake mu'amulanta shi ya kama wayar ita kanta,bata taba ganin waya mai kyau data burgeta haka ba,tasa hannu ta shafa screen din ya bude,kasancewar babu password a kai.
Murmushi tayi ta ajjiye wayar gefe,sai data yi wanka ta karya sannan ta zauna sosai saman kujera ta soma kiran duk wanda zata kira din daya bayan daya ciki kuwa har da ummee wadda ba qaramin murna tayi da jinta ba,ta sake jaddada qorafinta na kullum ta kira almustapha kan ya bata sai yace yana company shin bai hutawa ne shi?.
Tafe yake yana duba wani file da daya daga cikin manyan ma'aikatansu wanda shine mataimakin hamza a sashen da suke kula da irin auduga da zararrukan da suke siya daga wasu kamfanoni,takardun jimillar audugar da suka shigo da su ne yake dubawa,dab da zai shiga elevator sukayi kacibus da hamzan,sai ya miqawa wancan da ake kira ramadan yace anjima ya kawo mishi ya qarasa dubawa,don su kammala lissafin dukkan kudin da suka fita ta wannan fannin.
"Ya dai yau naga kamar kadan so makara baka shigo da wuri ba"
"Jiki da jini ke kawai"
"Gaskiya ne,me kake tunani kan audion daka saurara jiya?"
"Mu qarasa na yi maka bayani", a haka suka qarasa office din.
Kan kujerarsa ya nufa kai tsaye ya zauna yana dora jakarsa saman teburin,yayin da hamza ya fara bude fridge ya dauko ruwa yana sha,qoqarin bude jakar ya fara yi amma mazugin ya cije,ya daga jakar don ganin mai ya hanashi wucewa sai yaga takarda lanqwashe a jiki,cikin mamaki ua ciro takardar ya soma warwareta,rubutu ne a tsare tamkar da injin buga rubutu aka tsara shi,sannu a hankali ya soma bin rubutun yana karantawa,yana karantawa kanshi na shiga duhu,shawarwarine a tsare game da yadda zai warware matsalar kamfanin cikin sauqi,daya bayan daya kowacce kalma dake qunshe cikin takardar mai muhimmanci ce,kanshi bai fita daga duhu ba sai da yazo layin qarshe
"ina fatan alkhairi tare da fatan warwarewar matsalar cikin sauri,saboda ka dawo nutsuwarka,iyalinka na da buqatar zamanka waje daya da kuma samun cikakkiyar nutsuwarka,kulawar ubangiji ta tabbata tattare da kai" sosai kalaman suka dinga ratsashi,sai ya samu kanshi da maimaita kalaman,karon farko a rayuwarshi da ya taba samun wadan nan kalamai masu kyau da tsari daga wajen wata mace dake qarqashin ikonshi,a hankali murmushi ya subuce masa sanda ya kammala karanta sadarar karo na biyar
"Lafiyanka qalau kuwa zaka zauna kana dariya kai kadai,mutumin da murmushin naka ma wataran sai anyi kamar za'a biya kafin a ganshi?"
"Hauka nake" ya bashi amsa kai tsaye cikin gatsali yana gintse fuskarsa tare da miqewa tsaye,takardar ya dunqule zaiyi jifa da ita yana jan tsaki sai kuma ya fasa,ya daga takaddun dake gabanahi ya saka ta a tsakiyarsu,hakanan sai yaji wani sashe na zuciyarsa na bashi qwarin gwiwar gwada amfani da shawarwarin dake qunshe cikin wasiqar,jawo wayar land line yayi dake gabanshi ya fara latsawa,cikin qanqanin lokaci ya bada umarnin tara dukkan ma'aikatan dake cikin kamfanin a babban dakin taro dake kamfanin,freezer ya isa ya ciro ruwan shima yana kurba a hankali,binsa hamza yake kallo kafin yace
"Wai meke faruwa haka musty?"
"Zaka gani" bakinsa yaja yayi shiri,yasan tunda ya fara magana haka a taqaice ba mai sanya shi fadadawa,tilas yayi shiru har sanda aka isar masa da saqon gama haduwar ma'aikatan baki daya sannan ya dubi hamza
"Taso muje,meeting ne na qarshe".