← Book details Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 120 OF 226

Sashe 120

Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:51] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖

*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)

6⃣8⃣

*Bismillahir rahmanir rahim*

Allah yana cewa
*(RANAR QIYAMA YAYIN DA AKA BAWA DAN ADAM LITTAFIN DUKKAN AYYUKANSA ABINDA YA AIKATA SANDA YANA RAYE ZA'A CE DA DAN ADAM)KA KARANTA LITTAFINKA!!!,YA ISHEKA AKAN KANKA KA YIWA KANKA HISABI*

ya subhanallah,ya rahmanu kada kayi mana hisabi ka yafemu.
____________________________________

TEAM ABDUR RAHMAN YA DA SAURIN KARAYA IRIN HAKA NE,NAGA HAR KUN FARA SAREWA FA,ITA FA MACE ALLURAR CIKIN RUWA CE MAI RABO KA DAUKA,KADA 'YAN ADAWA SUYI MUKU DARIYA FA,TAM.
_____________________________________

Bata sake yunqurin tashi ko motsawa daga wajen ba har zuwa sanda suka iso qasa nijeria,anty dijen na lura da ita,ta kuma kusa ankarewa da dalilin gushewar nutsuwarta,daya daga cikin motocin alfarma dake mallakar mustaphan ita tazo ya kwashe baki daya,kallo daya zaka yi musu ka tabbatar sabuwa ce dal,laila sai bude baki take saboda yadda motar tayi mata dadi,qasa qasa take cewa da sumayya
"Anty sumayya dama kada aje gida don kada mu sauka daga motar nan,dadi wallahi" dariya ta baiwa sumayyan har sautin murmushinta ya fito,hada idanuwa sukayi sanda ya waiwayo yana tsammanin ko wani abun ne ya sake faruwa,da sauri ta kawar da kanta tana gintse dariyar.

Kowa na ficewa daga motan yayin da yake zaune baiko da niyyar motsawa,amma ta danganta hakan da cewa shi za'a shige da shi cikin gida ne tunda su zasu sauka ne su shiga nasu gidan,tsoron ta yadda zata giftashi ya kamata,duka sun fice saura ita daya,a hankali ta durqusa zuciyarta na bugawa har ta isa bakin qofar inda anty dije ke tsaye tana tsumayin fitowarta din cirar maqullin gidan dake jakar sumayyan,daidai sanda ya fara magana cikin izza da nutsuwa yana baiwa driva umarnin su wuce ciki,kadan ya rage ta fadi anty dije ta tallafeta tana dubanta cikin salon tuhuma
"Wai mene haka sumayya lafiyanki kuwa"
"Bab....babu komai,qafata ce ta harde" bata ce komai ba ta karbi maqullin sannab suka jera zuwa cikin gidan
"Ya kamata ki sanyawa ranki nutsuwa,na fuskanci duk sanda mustapha yayi magana saiki rasa sukuni da nutsuwarki,bafa mukhtar babe,bai kuma san mukhtar ba,kada ki sake ki sake aikata irin gangancin da kika aikata" da sauri ta dubi anty dijen,ya akayi ta karancin halin da take ciki,itama bata sani ba,batasan dalilin da yake sanyawa take kasa controlling kanta ba aduk sanda taji muryarshi wadda ke zubi sak data mukhtar dinta,abinda kawai zai banbanta tashi data dan fi ta mukhtar laushi,bata da bakin magana saboda haka bata ce komai ba jikinta a sanyaye suka qarasa cikin gidan.

Washe gari haka ta tashi jiki duk a mace,ba dadi haja take ji cikin ranta,bata so anty dije tayi mata wani duba na daban,ba ita ta dorawa kanta ba tasani daga Allah ne,muhimmancin da mukhtar ke da shi a rayuwarta zaiyi wuya tayi saurin mance duk wani abu da yayi kamanceceniya da tashi rayuwar,ba abunda ta iya tsinanawa daga wanka sai kwanciya,ita kanta anty dijen ta lura,sai itama taji ba dadi,tana tsammanin ko fadan data yi mata ne ya sanyata zama haka?.

Wajen sha biyu ta sameta dakinta tana fitar da kayan da suka dawo da su tana kuma shirya wasu cikin wata jakar daban
"Sumayya,meke damunki?,ko don na miki fada jiya" kamar mai jira sai taji qwalla ta cika mata idanu,kai take girgizawa tana duban anty dijen
"Ba don wani abu yasa na miki magana ba,na fuskanci abinda ke faruwa da ke ne,ina so ki sauya kanki ne" da sauri ta tareta
"Ki daina fadar haka anty,wlh ba haka bane,ke uwa ce a gareni,kina da ikon zartar da duk hukuncin da ya dace da ni,nima bansan me yasa a duk sanda yayi magana nake zamowa haka ba,mukhtar dina nake tunawa anty har yau yaqi barin zuciyata,muryar mukhtar nake ji cikin tasa,sai na dinga jin kamar shine tare da ni" tausayin sumayya ya kamata,ta kama hannuwanta tana duban idanuwanta tana murmushi
"Na fahimceki sumayya,amma shi baisan da haka ba,bana son ya raina min ke ko yayi tunanin wani abu na daban,nafa ji zafin abinda ya miki da fari,ban fadi miki bane saboda yayi ne cikin rashin sani......ki zama jaruma pls,ki dinga tunawa ba shine mukhtar ba....any way,mu ajjiye wannan maganar a gefe,me zakiyi da wadan nan kayan da kike shiryawa a jaka?" Hawayen take gogewa da tafin hannunta itama tana murmushi
"Kano nake so gobe na tafi" idanu ta zaro
"Kano sumayya gobe daga dawowarmu jiya,ko dai wani abun daban aka yi miki?" Marairaice wa tayi
"Don Allah umman khalipha ki daina cewa an min wani abu,kin taba gani uwa ta yiwa 'yarta wani abu ba dai dai ba,kuma diyar ranta ya baci?"
"To idan ba haka ba ai kya bari ko zuwa next week ne atleast ko?,zuwa sannan kin warware gajiyar tafiya kin fidda tsarabar su malam"
"Anty inata kara amma baki gane me nake nufi ba,na qagu any naga abdallah,i missed him alort anty,shima kuma nasan haka ne" kama baki tayi taja dariya
"Iyeeee,lallai yarinya,ga malam ga mama duka su bakiyi missing dinsu ba sai yaronki gaskiya ne" kunya ta kama sumayyan ta kifa kanta saman hannun anty tana dariya qasa qasa,ba zata iya boyewa ba,tabbas tayi missing yaronta
"Shikenan,Allah ya kaimu,amma fa saidai ki bari sai jibi,zamu bude jaka afidda kayan su malam" duk da cewa ba hakan taso ba amma anty dije tafi gaban tayi jayayya da ita haka ta amsa mata da to.

Misalin uku na rana suna zaune suna cin abincin rana amira ta shigo,bisa dukkan alamu daga makaranta take,don ga handout nan a hannunta da key din motarta,wani daj ihun farinciki ta saki tana qarasowa kusa da sumayya,gaisawa sukayi da anty dije tana tsatstsokanar su laila khalipha da minal,baki daya tace sun sauya,lallai garin ya karbesu,sai ta maida dubanta ga sumayya
"Umman khalipha wai wannan amiran umman khalipha ce ko wata kuka samo a can?" Dariya suka saki baki daya kowa ya gane me take nufi,cikin salon zolaya itama sumayyan tace
"Sun baro waccar a can,wannan musanyota sukayi" dukan cinyar sumayyan amira tayi tana fadin
"Kina kallon mudubi kuwa?,wallahi kin bala'in zama wata queen namesake,ni zan fara yiwa alqasim wannan albishir din" harara ta aika mata tana murmushi
"Ban aikeki ba,bismillah sa hannu muci abinci" idanuwanta ta maida kan abincin wanda saura duk da miya suke ci banda ita,fara da man take jin ci don an dade ba'a hadu ba
"Wai wai,an kuwa zanci,shinkafa da wake da manja ne da yaji ko?,ga kuma salad,rabona da abincin nan da dewa,ina son fara da mai da yaji,su kam saidai suyi miya,musamman idan waccan baturiyar tazo,bama tasan fara da mai ba,idan taga wani yana ci har kyabe baki take wai muna cin abinci gaya" ta fada itama tana tabe baki,murmushi anty dije tayi
"Dan gidanku yayarki ce dai,kuma kinsan baki isa ku fadi ba gaban maigidanta" amsa mata ta soma bayan tayi cokali daya
"Me ruwa na da su,shima shi yaga zaya iya,haka kawai mutum bashi da maraba da gauro,kowa yana ci gaba ta fuskan family amma banda shi,haka kawai jiya har na kwanta ya tada ni wai na hada mishi fruit salad baturen kawai ga abinci ba zaya ci ba wai yayi masa nauyi"
"Ke amira,zakici gidanku,ba yayanki bane?" Saki tabe fuska tayi kakar zata saki kuka
"Ni umman khalipha bama wannan bane ya qonan raj,Allah anty su'adah 'yar rainin sense ce,na shiga kai mishi naji suna waya,ta baro america ta biyoshi dubai wai bata tadda shi,yace bai nan yana naija wai gobe zata biyoshi,wannam ai ba matar aure bace matar yawo ce,kuma kowa yw zuba mishi idanu wai matarshi ce haka suka tsara rayuwansu,to wallahi aure zamu masa" baki daya ta basu dariya saboda salon yadda tayi maganar bilhaqqi,har sumayya na qwarewa sai data kurbi ruwa
"To ba sai ki masa ba tunda kece gaba da shi,kijimim tsaurin ido,musty zaki ma aure?,yo ko adam ai bai usa yace zaya yi masa aure ba bare ke" tsaki sumayya ta ja bayan ta samu tarin ya tsaya tana dan dukan cinyar amiran
"Kinga malama,ki dinga maganar da zata amfanemu,juyo muci abinci" waiwayowa tayi tana duban sumayya
"Uhmmmm,wallahi kuwa,don wannan babu ranar sauyawarsu" sai tayi qasa qasa da murya
"Kefa kawai nake jira ki dawo a fara tsara mai yiwuwa,jibi za'a kawo lefe fa,kuma da sati uku zasu zo kwanakin bikin"
"Komai kika tsara dai dai ne,amma ni jibin zan wuce kano" idanu ta zaro tana tsaida cin abincin da take
"Me kika fada namesake,ina ce miki jibi kawo lefe kina cemin jibi zaki tafi kano,a satin nan fa zamu je dubai siyo kayan kitchen,tare da ya musty zamu koma,shigowar nan da nayi passport naki nazo karba za'a buga mana visa" cabdi,wane musty din,mustaphansu?,ta godewa Allah da ya bata idea din tafiya kano,don ko ana yankan jikinta ba zata bisu ba,wannan dan jin kan?,dan wulaqancin dan rainin wayo?
"Kice wani abu mana kinyi shiru,duk kin rusan plan,wallahi idan baki je ba da wannan matar tashi zaya hadanu siyan kayan kitchen,bayan babu abinda tasan amfaninsa a kitchen saidai ta ganshi da ido,sai shegen izza da dagawa,zata siya min kayan shirme ne masu dan banzar tsada tana ganin kudin mijinta ne,kamar an gaya mata shi mai kudi baisan ciwo da zafinsu ba" ajiyar zuciya ta saki
"Banji dadi bane amira,amma zuwa kano ya zame min dole jibi,malam na son ganina" ta hada da qarya,sai anty dije tayi saurin tashi ta doshi kitchen don kada amira ta roqeta ta hana sumayyan zuwa,don qaryan sumayyan ta mata dai dai,koda tana abuja ba zata barta taje ba,don ta fuskanci inuwa daya bata zaunuwa tsakanin sumayyan da shi uban gayyar,bare tafiya ma wata uwa duniya babu muharramin sumayyan ba zata yarda tayi ta ba.
Chapter 120 · 0% Book details