Sashe 113
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kusan ranar haka ta wuni,da daddare ta dauki kayan sawarta kala uku ta gudu gidan anty dije,a can ta barje kukan ta son ranta,saboda a can babu dama saboda idon mutane,itama antyn batasan tana nan ba,sai wayar mai gadinsu ta ara ta gayamata don kada su nemeta,washe gari aka sha yini sosai,duk abin nan da ake sumayyan na gidan anty dijen,haka ta wuni kwanciya don mai gidan baya nan,ita kuma antyn a can gidansu ta kwana,sai gobe zata dawo idan an kai amarya,halima itama sai next week za'a kaita,kafin nan an kammala yi mata tata siyayyar.
******* ****** ********
Zaune take a uwar dakan anty dije wadda jiya bayan kai amarya ta dawo gida,tana ta faman shirya kayansu cikin trolly abinta,sumayya na zaune daga bayanta,sanye take da doguwar riga 'yar kanti mai qaramin hannu,kanta ba dankwali sai gashinta mai baqi da santsi data hade cikin ribbom,jingine take da kujerar dake dakin qafafunta amiqe,hannunta riqe da cup din tea wanda tun dazun aka hado mata shi har yana gab da hucewa bata yi masa kyakkyawan shaa ba,idanuwan nan a kode tamkar danyen nama kamar yadda fuskarta take a kode alamun ko yaushe cikin kuka take,sam anty dije taqi bata fuskan kawo wani qorafi ko wata magana kan auren,tunda dai an riga an daura ta riga data zama matar almustapha,abu guda ne kawai yanzu a gaban anty dijen yadda zata shirya diyar tata fes ta iya shiga kowanne bigire na rayuwa,abinda ke sake karya zuciyar sumayya yadda taga ita antyn ma murnarta take,hannunta tasa ta shafa gashinta hadi da lumshe ido tana kiran sunan Allah qasa qasa,ita kadai tasan meke yawo cikin kwanyarta,kamar ta cire qwaqwalwar ta huta haka take ji,waiwayowa antyn tayi tana cewa
"To zaki bimu abujan ne ko kuwa sai munzo daukar amarya?" Mai neman kuka ne aka jefeshi da kashin awaki,aisai kawai ta saki kukan ta sosai ta dire cup din tea din,baki anty dije ta kama dariya na subuce mata
"La'ilah,ku jimin yarinya,wai ita bilhaqqi da gaskiya bata son almustapha,mutumin da ake so ko kallon arziqi ya yiwa wasu,to wallahi saidai kiyita kukanki kada ki fasa bazan lallasheki ba,tunda kinqi jin lallashi ballantana shawara,da kinsam tun usilu ba zaki iya biyayya wa su malam ba ai da kin gaya musu tun sanda suka tasamma hada auren,sai yanzu saboda yankan baya zaki tasani gaba da kuka me zan miki,haka zakije ki yi gaban su'ad din,tabdi wallahi da kuwa kin jawa kanki,idan kin gama kukan kya tashi kiyi abinda ya dace,don tun jiya malam ke tambayarki bai gqnki ba zai damqa miki sadakinki" anty dijen ta juya tana ci gaba da aikace aikacenta har sanda laila ta shigo da wayar sumayyan hannunta tana fadin
"Anty amira ce a layi" ta miqawa sumayyan,harara ta danqara mata hakan ne ya sanya anty dije karbar wayar ta kara a kunnenta bayan ta sanyata a handsfree tana fadin
"Ai amira kema ta shafeki ba zata amsa wayarki ba,ke da jin muryarta sai bayan wani lokaci"dariya ta qyalqyale da ita
" don Allah anty matsa kusa da ita nayi kata waqar ta zama ta zama,nima haka ta yimin,ranki ya dade amaryar yayanmu ayi mana haquri,amma dai ya musty ne ya riga ya zama mijin sai haquri,anty barta ko bata yi magana ba yanzun zata yi idan muka zo sayan baki"dariya suka sanya baki daya,hakan ya sake qular da zuciyar sumayya,sai ta miqe ta fice tana kuka muraran kamar wata qaramar yarinyar,binta anty dije tayi da kallo tana dariya,har yau da sauran quruciya sosai tattare da sumayyan,gata nan a zahiri ta bayyana.
Tunda aka daura auren ranar juma'a baabaan bai bar kano ba har zuwa yau litinin,misalin qarfe takwas na dare bayan ya gama cin abincin dare ya dauki wayarsa ya soma lalubar musty man.
Dawowarshi kenan daga asibiti,yau a gajiye yake saboda mutum uku ya yiwa c.s,kayan jikinsa kawai ya cire ya rataye suit dinshi a inda yake rataye kayan da za'a wanke masa,ya zaluqo daya daga cikin towel daga ma'ajiyar towel ya daura sannan ya shiga wanka,kwanciyarsa yayi luf cikin ruwan wankan mai azabar dumi da qamshi,duminsa na ratsa kowacce gaba ta jikinsa,idanunsa na alumshe sai ka rantse da Allah bacci yake saidai idanunshi biyu,tunani ne kala kala kan kwanyarsa yake yawo,ya soma gajiya da zaman wannan hotel din wanda kusan a ciki yake rayuwa,duk da yana da gida mallakinsa cikin qasar,saidai hakanan yafi sha'awar zamam hotel din yana ganin kamar ya fi masa sauqi,idan gidan ne dole sai ya nemi ma'aikata da zasu zauna cikin gidan su kula masa da tsaftarsa da komai da komai wanda shi ba kasafai yake son ma'aikata haka barkatai ba,musamman a qasar da ba taka ba,tun yana cikin bayin ya dinga jin rurin wayarshi,data katse wani kiran ke shigowa,sai ya saki tsaki ya sake gyara kwanciyarsa ba tare da koya bude idanunshi ba bare yayi haramar fitowa,ga tsammaninshi su'ad ce don kimanin sati guda rabon da ya nemeta,ta kirashi dazu zai shiga thiather ya dakatar da ita,saboda abu na farko data fara da shi shine mitan ya watsar da ita sabida ta koma zata qarasa karatunta,shikam a yanzun yana ganin matsalarta ce,shi ya gama da wannan issue din,sabgogin dake gabansa ma kawai sun shasa masa kai,sai da ya kammala wankansa a nutse sannan ya fito ya daura towel dinsa a qugu wanda hakan ya fito da dukkan suffa da zatinsa na cikakken namijin da ya amsa sunanshi,ya qarasa wani sashi daban ya daura alwala ya fito.
Zai gifta wayar kenan ta sake ruri,ya waiwaya kadan ya dubeta sai yaga sunan abbu na yawo saman screen din,sunan da ya sanyawa baabaa prof kenan,da hanzari ya fasa abinda yake ya isa ga inda wayar take ya daga cikin girmamawa tamkar yana gabanshi cikinnn nutsuwa da sanyin murya
"Barka da warhaka" ya fadi
"Barka kadai,ina ka shiga ne haka tun dazun ina kira ko kana asibiti ko company?"
"A'a wanka nake" ya fada a taqaice,don a tsarinsa bai fiya doguwar magana ba,kadan ce mai ma'ana
"To madalla"
"Lafiya kuke baabaa ya kowa da kowa?"
"Kowa lafiya qalau yake almustapha"
"Masha Allah"
"Ammm,almustapha kawai tsarin zuwanka gida ne nan kusa?" Dan jim yayi kafin ya amsa
"A'ah,saidai ko idan kana son ganina ne?" Yana mamakin yadda yake da kaifin qwaqwalwa da cimma abun tun kafin ka kammala bayaninka,sau tari suna fara magana da baabaan yake gane mai yake da buqata tun bai qarasa ba
"Tabbas,ina buqatar ganinka,wani muhimmin batu ne ya taso ma rayuwarka nake so mu gana a kai,yaushe kake da chance din zuwa?" Duk da maganan ta dan sanyashi a duhu amma bai da niyyar tambaya
"Yaushe kake son gani na?"
"Eh to,ko kamar nan da sati biyu haka"
"Sati biyu masu zuwa ina zuwa da yardar Allah"
"To masha Allah,Allah yayi maka albarka,sai kazo"
"Amin,na gode" a hankali ya ajjiye wayar yana binta da kallo,zuciyarsa na son sawwara masa muhimmin batun da baabaa yace ya taso wa rayuwarshi,duk iya hasashensa bai canka ba,hakan ya sanya ya dage kafadunsa biyu na rashin damuwa ya nufi inda ya ajjye kayan shafarshi a tsare kamar wata mace,komai nashi mai aji da tsada irin wanda maza ke amfani da shi,yana shiryawa yana tunanin yadda tafiyan zata kasance,dama yana son zuwa daya daga cikin asibitocinsa dake kano kwana biyu bai leqa yaga maike faruwa ba shu da gidan marayunsa,duk da yana da wakili dake gano duk abinda ke tafiya kuma a kai duk abinda ake da buqata wuraren,amma bai saki komai ba balle kowa yayi mishi yadda yaga dama,mutum ne shi mai doka da qa'ida baison kuma a saba masa ko a taka mishi kamar yadda bai taka dokar kowa.
Yana shiryawa yana kiran lambobin da ya saba kiran idan yana buqatar abinci,duk da sun san kusan cimarsa ta dare,ba wani abu mai nauyi yake ciki ba,a ladabce suka amsa buqatarsa ya kashe wayar,wanda kamar jira ake ya kashe wancan kiran wani kiran ya shigo,su'ad ce da layinta na america,yana kallon kiran yayi banza da shi har sai daya gaji ya katse,haka ta dinga kira har ta hada masa wajen miscal biyar,wanda tuni ya maida wayar silent don baison hayaniya,daga qarshe saqon tex ya shigo yasan kuma daga ita ne,baibi ta kai ba ya share ya tada shafa'i da wuturi,da wuri yake son kwanciya yau ya huta sosai saboda gobe yana da meeting da ma'aikatan companynsa na saqar abaya.
To masu karatu yanzu fa kusan aka soma ko?,saidai gobe kumin uziri idan ina da sabga idan kun samu to ba lallai ya kai na yau ba,idan kuma kunji shuru sai uziri,kasancewar duk sanda kuka ji shiru daga wajen marubuci uziri ne ke kama shi irin uzirin dake kama kowanne dan adam,babban nauyi marubuci keji cikin kansa da qirjinsa idan ya soma rubutawa jama'a labari,baya jinsa fayau sakayau har sai randa ya kammala,Allah ya bar zumunci.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:51] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
7⃣5⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*ALLAH S W T YANA CEWA*
*ALLAH BAYA JINKIRTAWA WATA RAI IDAN AJALINTA YAZO*
______________________________________
Wannan karo anty dije daga ita sai yaranta suka koma abuja cike da kewa,kowa cikinsu sai yaji babu dadi,kasancewar sumayyan ta riga ta shiga jikinsu.
******* ****** ********
Zaune take a uwar dakan anty dije wadda jiya bayan kai amarya ta dawo gida,tana ta faman shirya kayansu cikin trolly abinta,sumayya na zaune daga bayanta,sanye take da doguwar riga 'yar kanti mai qaramin hannu,kanta ba dankwali sai gashinta mai baqi da santsi data hade cikin ribbom,jingine take da kujerar dake dakin qafafunta amiqe,hannunta riqe da cup din tea wanda tun dazun aka hado mata shi har yana gab da hucewa bata yi masa kyakkyawan shaa ba,idanuwan nan a kode tamkar danyen nama kamar yadda fuskarta take a kode alamun ko yaushe cikin kuka take,sam anty dije taqi bata fuskan kawo wani qorafi ko wata magana kan auren,tunda dai an riga an daura ta riga data zama matar almustapha,abu guda ne kawai yanzu a gaban anty dijen yadda zata shirya diyar tata fes ta iya shiga kowanne bigire na rayuwa,abinda ke sake karya zuciyar sumayya yadda taga ita antyn ma murnarta take,hannunta tasa ta shafa gashinta hadi da lumshe ido tana kiran sunan Allah qasa qasa,ita kadai tasan meke yawo cikin kwanyarta,kamar ta cire qwaqwalwar ta huta haka take ji,waiwayowa antyn tayi tana cewa
"To zaki bimu abujan ne ko kuwa sai munzo daukar amarya?" Mai neman kuka ne aka jefeshi da kashin awaki,aisai kawai ta saki kukan ta sosai ta dire cup din tea din,baki anty dije ta kama dariya na subuce mata
"La'ilah,ku jimin yarinya,wai ita bilhaqqi da gaskiya bata son almustapha,mutumin da ake so ko kallon arziqi ya yiwa wasu,to wallahi saidai kiyita kukanki kada ki fasa bazan lallasheki ba,tunda kinqi jin lallashi ballantana shawara,da kinsam tun usilu ba zaki iya biyayya wa su malam ba ai da kin gaya musu tun sanda suka tasamma hada auren,sai yanzu saboda yankan baya zaki tasani gaba da kuka me zan miki,haka zakije ki yi gaban su'ad din,tabdi wallahi da kuwa kin jawa kanki,idan kin gama kukan kya tashi kiyi abinda ya dace,don tun jiya malam ke tambayarki bai gqnki ba zai damqa miki sadakinki" anty dijen ta juya tana ci gaba da aikace aikacenta har sanda laila ta shigo da wayar sumayyan hannunta tana fadin
"Anty amira ce a layi" ta miqawa sumayyan,harara ta danqara mata hakan ne ya sanya anty dije karbar wayar ta kara a kunnenta bayan ta sanyata a handsfree tana fadin
"Ai amira kema ta shafeki ba zata amsa wayarki ba,ke da jin muryarta sai bayan wani lokaci"dariya ta qyalqyale da ita
" don Allah anty matsa kusa da ita nayi kata waqar ta zama ta zama,nima haka ta yimin,ranki ya dade amaryar yayanmu ayi mana haquri,amma dai ya musty ne ya riga ya zama mijin sai haquri,anty barta ko bata yi magana ba yanzun zata yi idan muka zo sayan baki"dariya suka sanya baki daya,hakan ya sake qular da zuciyar sumayya,sai ta miqe ta fice tana kuka muraran kamar wata qaramar yarinyar,binta anty dije tayi da kallo tana dariya,har yau da sauran quruciya sosai tattare da sumayyan,gata nan a zahiri ta bayyana.
Tunda aka daura auren ranar juma'a baabaan bai bar kano ba har zuwa yau litinin,misalin qarfe takwas na dare bayan ya gama cin abincin dare ya dauki wayarsa ya soma lalubar musty man.
Dawowarshi kenan daga asibiti,yau a gajiye yake saboda mutum uku ya yiwa c.s,kayan jikinsa kawai ya cire ya rataye suit dinshi a inda yake rataye kayan da za'a wanke masa,ya zaluqo daya daga cikin towel daga ma'ajiyar towel ya daura sannan ya shiga wanka,kwanciyarsa yayi luf cikin ruwan wankan mai azabar dumi da qamshi,duminsa na ratsa kowacce gaba ta jikinsa,idanunsa na alumshe sai ka rantse da Allah bacci yake saidai idanunshi biyu,tunani ne kala kala kan kwanyarsa yake yawo,ya soma gajiya da zaman wannan hotel din wanda kusan a ciki yake rayuwa,duk da yana da gida mallakinsa cikin qasar,saidai hakanan yafi sha'awar zamam hotel din yana ganin kamar ya fi masa sauqi,idan gidan ne dole sai ya nemi ma'aikata da zasu zauna cikin gidan su kula masa da tsaftarsa da komai da komai wanda shi ba kasafai yake son ma'aikata haka barkatai ba,musamman a qasar da ba taka ba,tun yana cikin bayin ya dinga jin rurin wayarshi,data katse wani kiran ke shigowa,sai ya saki tsaki ya sake gyara kwanciyarsa ba tare da koya bude idanunshi ba bare yayi haramar fitowa,ga tsammaninshi su'ad ce don kimanin sati guda rabon da ya nemeta,ta kirashi dazu zai shiga thiather ya dakatar da ita,saboda abu na farko data fara da shi shine mitan ya watsar da ita sabida ta koma zata qarasa karatunta,shikam a yanzun yana ganin matsalarta ce,shi ya gama da wannan issue din,sabgogin dake gabansa ma kawai sun shasa masa kai,sai da ya kammala wankansa a nutse sannan ya fito ya daura towel dinsa a qugu wanda hakan ya fito da dukkan suffa da zatinsa na cikakken namijin da ya amsa sunanshi,ya qarasa wani sashi daban ya daura alwala ya fito.
Zai gifta wayar kenan ta sake ruri,ya waiwaya kadan ya dubeta sai yaga sunan abbu na yawo saman screen din,sunan da ya sanyawa baabaa prof kenan,da hanzari ya fasa abinda yake ya isa ga inda wayar take ya daga cikin girmamawa tamkar yana gabanshi cikinnn nutsuwa da sanyin murya
"Barka da warhaka" ya fadi
"Barka kadai,ina ka shiga ne haka tun dazun ina kira ko kana asibiti ko company?"
"A'a wanka nake" ya fada a taqaice,don a tsarinsa bai fiya doguwar magana ba,kadan ce mai ma'ana
"To madalla"
"Lafiya kuke baabaa ya kowa da kowa?"
"Kowa lafiya qalau yake almustapha"
"Masha Allah"
"Ammm,almustapha kawai tsarin zuwanka gida ne nan kusa?" Dan jim yayi kafin ya amsa
"A'ah,saidai ko idan kana son ganina ne?" Yana mamakin yadda yake da kaifin qwaqwalwa da cimma abun tun kafin ka kammala bayaninka,sau tari suna fara magana da baabaan yake gane mai yake da buqata tun bai qarasa ba
"Tabbas,ina buqatar ganinka,wani muhimmin batu ne ya taso ma rayuwarka nake so mu gana a kai,yaushe kake da chance din zuwa?" Duk da maganan ta dan sanyashi a duhu amma bai da niyyar tambaya
"Yaushe kake son gani na?"
"Eh to,ko kamar nan da sati biyu haka"
"Sati biyu masu zuwa ina zuwa da yardar Allah"
"To masha Allah,Allah yayi maka albarka,sai kazo"
"Amin,na gode" a hankali ya ajjiye wayar yana binta da kallo,zuciyarsa na son sawwara masa muhimmin batun da baabaa yace ya taso wa rayuwarshi,duk iya hasashensa bai canka ba,hakan ya sanya ya dage kafadunsa biyu na rashin damuwa ya nufi inda ya ajjye kayan shafarshi a tsare kamar wata mace,komai nashi mai aji da tsada irin wanda maza ke amfani da shi,yana shiryawa yana tunanin yadda tafiyan zata kasance,dama yana son zuwa daya daga cikin asibitocinsa dake kano kwana biyu bai leqa yaga maike faruwa ba shu da gidan marayunsa,duk da yana da wakili dake gano duk abinda ke tafiya kuma a kai duk abinda ake da buqata wuraren,amma bai saki komai ba balle kowa yayi mishi yadda yaga dama,mutum ne shi mai doka da qa'ida baison kuma a saba masa ko a taka mishi kamar yadda bai taka dokar kowa.
Yana shiryawa yana kiran lambobin da ya saba kiran idan yana buqatar abinci,duk da sun san kusan cimarsa ta dare,ba wani abu mai nauyi yake ciki ba,a ladabce suka amsa buqatarsa ya kashe wayar,wanda kamar jira ake ya kashe wancan kiran wani kiran ya shigo,su'ad ce da layinta na america,yana kallon kiran yayi banza da shi har sai daya gaji ya katse,haka ta dinga kira har ta hada masa wajen miscal biyar,wanda tuni ya maida wayar silent don baison hayaniya,daga qarshe saqon tex ya shigo yasan kuma daga ita ne,baibi ta kai ba ya share ya tada shafa'i da wuturi,da wuri yake son kwanciya yau ya huta sosai saboda gobe yana da meeting da ma'aikatan companynsa na saqar abaya.
To masu karatu yanzu fa kusan aka soma ko?,saidai gobe kumin uziri idan ina da sabga idan kun samu to ba lallai ya kai na yau ba,idan kuma kunji shuru sai uziri,kasancewar duk sanda kuka ji shiru daga wajen marubuci uziri ne ke kama shi irin uzirin dake kama kowanne dan adam,babban nauyi marubuci keji cikin kansa da qirjinsa idan ya soma rubutawa jama'a labari,baya jinsa fayau sakayau har sai randa ya kammala,Allah ya bar zumunci.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:51] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
7⃣5⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*ALLAH S W T YANA CEWA*
*ALLAH BAYA JINKIRTAWA WATA RAI IDAN AJALINTA YAZO*
______________________________________
Wannan karo anty dije daga ita sai yaranta suka koma abuja cike da kewa,kowa cikinsu sai yaji babu dadi,kasancewar sumayyan ta riga ta shiga jikinsu.