Sashe 46
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Abinda bata sani ba malam din na sane da komai,bata san da hakan ba sai ranar da aka kai kudin auren abubakar da saka rana wanda baki daya aka tsaida watanni biyu,washegarin ranar malam din yayi kiranta falonsa,bayan ya kammala duka abubuwan da yake ya dubeta
"Am sumayya,nasan cewa kinsan tsarina da al'ada ta gidan nan,sannan alhamdulillah kin san mutuncin mace dakin mijinta,baki da inda yafi nan daraja,dukkan wani abu da ya faru a baya mu ajjiyeshi gefe haka Allah ya tsarama rayuwarki,cikin KUNDIN QADDARARKI yake,babu wanda ya isa ya goge miki ko ya kautar miki da shi"
"Haka ne malam" ta fada kanta na duqe zuciyarta ba bugawa kamar zata bullo,addu'a take kada Allah yasa malam ya bullo mata da zancan da bata da buqatar jinsa a yanzu
"Sumayya,yaron nan abdur rahman yazo guna ya gabatar min da kansa a matsayin manenin aurenki,to amma kasancewarki bazawara a yanzu addini ya baki damar zabawa kanki mijin aure ya sanya nace sai na tambayeki naji mene ne ra'ayinki,kada ki zalunci kanki a yanzu kina da dama,sannan zaman aure zama ne bana yau ko gobe kawai ba,zama ne na har abada". Wani tashin hankali ne ya rikito mata,abubuwan da suka dinga faruwa da ita zamanin tana auren mukhtar tsaf suka dinga dawo mata,a hankali ta bude bakinta muryarta na rawa
"Kayi haquri malam,abdur rahman dan uwa ne ga mukhtar dan wan babansa ne nasan kasan haka malam" murmushi ya saki
"Sumayya,sumayya kenan,wannan duka ba abun damuwa bane tunda dai aure ya halasta a tsakaninku ba haramun bane" tashin hankali ta fada cikin zuciyarta,'yan uwan mukhtar fa sune dai 'yan uwan abdur rahman,ba'a canzawa tuwo suna
"Malam,ina tsoron sake kasancewa da ahalin su mukhtar...." Sai tayi shiru ta kasa qarasawa,shima shirun yayi yana nazarin maganarta,tabbas sumayya yarinya ce mai matuqar zurfin ciki,a iya zamanta na aure bazai iya fadar ranar data kawo matsalarta ba,saidai idan an fahimta a maganta mata.
"Ke kike da zabi a hannunki ai,ba zan miki auren dole ba"
"Malam,ina so abdur rahman ya janye daga qudurinsa,bana son sake shiga ahalinsu" ta fada zuciyarta na raurawa muryarta na rawa
"Shikenan zancansa ya wuce,sai ki fidda miji ina son hada aurenki da na yayanki abubakar idan ta kama har da su halima baki daya"
"Amma malam ba......."
"Sumayya,bana son qorafi ko wata magana,kinsan ba zaiyiwu kici gaba da zama a gida ba,shekara nawa,shekara daya ana gab da cika ta biyu" shuru tayi don tafi kowa sanin waye malam,amma ina mafita meye mafitarta?,
"Sumayyan luqman fa?" Taji ya jefo mata tambayar wadda ta sanya dago kanta ta dubeshi,murmushi ya kuma yi yana dubanta
"Mamaki kike yadda na sanshi?,ya fara zuwa gunki ba da izini ba ya karya doka ta,hakan ya sanya nayi bincike a kansa,na samu gamsassun bayanai a kansa,mutumin kirki ne bakin gwargwado" sai ya dan ja fasali yana dubanta kafin yaci gaba da cewa.
_yauma dai amin uziri_
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣0⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*innal laha la yugayyiru maa bi qaumin hatta yugayyiru ma bi'an fusihim*
_haqiqa Allah baya canzawa mutane(halin ko yanayin da suke ciki)har sai sun canza da kansu_
______________________________
Ungawa ce mai matuqar kyau da tsari,akwai nauikan mutane daban daban cikinta,saidai akasarin mzauna cikinta din masu hannu da shuni ne da kuma masu rufin asiri ko wadanda suke ma'aikatan gwamnatin tarayya ta basu gida su zauna kamar su anty dije.
Sai da mansur ya fidda kayanta baki daya ya shigar mata cikin gidan ta masa godiya sosai sannan ya ja motarsa ya shige wani katafare kuma hamshaqin gida dake kallon nasu.
Dukka yaran gidan na nan kasancewar ranar qarshen mako ce,laila ita ce babba,sai hafiz mai bi mata,sannan khalifa sai nasir sai auta amina minal,a qalla laila zata yi shekaru goma sha hudu,ita ta fara ganin shigowar sumayya falon,ihu ta sanya wanda ya janyo hankalin 'yan uwanta ta nufi sumayya ta rungumeta,haka sauran suka baibayeta wanda ya janyo musu faduwa a qasa dukansu suna dariya,da qyar ta samu suka dagata suka koma saman kujera sannan ta soma tambayarsu anty dijen don bata ji motsinta ba,dining laila ta nuna wa sumayyan tana cewa
"Kinga yaya sumayya can duka abincinki ne,tun dazu mama ke jiranki baku iso ba har ta gaji ta shiga gidan daddy prof,amma bari naje na kirata" ta fada tana yafa dan yalolon mayafinta tayi waje da sauri,khalifa sumayya tasa ya fara nuna mata toilet ta shiga tayi alwala,tana kammala alwalar anty dije na shigowa
"Sai yanzu?,gaskiya kunyi nauyi a hanya kamar wadanda suka hau motar haya inji hajiya bilki" murmushi sumayya tayi tana duban anty dije wadda ta sake gogewa bisa dukkan alamu zaman garin ya karbeta matuqa,ta kuma zama 'yar gayu ita da yaranta baki daya
"Wallahi anty sai da muka biya kasuwa muka karbo wasu kaya sannan har mun dau hanya wani oga ko yallabai ya maida ku zoo road karbo dinki"
"Eh inaga man ne dinkunan su'ad ce,maza yi sallar kizo kici abinci kafin mu zauna hirar yashe gamo" ta fada tana sanya su laila dauke akwatunta zuwa wani daki da aka tanada saboda baqi irinta.
Sai da taci ta qoshi sannan suka baje a falon ana hiran yaushe gamo,kusan haka suka qarar da wunin ranar,ko da malamar lesson din yaran ma tazo guduwa sukayi suka qi zuwa sai tafiya tayi,da dare ma yayi da qyar suka tafi dakinsu don cewa sukayi tare da sumayyan zasu kwana,saida anty dije ta korasu saboda tana son suyi zance,sosai suka sake kuwa don mai gidan ta baya nan sun tafi semina lagos,sosai anty dije ta sake kwantar mata da hankali tare da bata shawarwari ta rufe da fadi cikin sigar tsokana
"Duk da nasan sumayyan tawa zuwa yanzu ta fara girma,hankali ya fara zuwa mata" itama dariya tayi,sai wajen sha daya da rabi sannan ta fita ta barta,to nan din ma lukman bai barta ba da hira sai data ce tana jin bacci sannan yace
"Ki kula min da kanki to na baki amanar kanki my dear kinji"ajiyar zuciya ta saki sannan ta amsa masa ta katse kiran,taso kiran halina taji ya abdallah yake,amma ganin dare yayi nisa ya sanyata ta haqura ta barwa gobe,duk sai taji tana kewar yaron nata.
****** ****** ******
Kwanakin da tayi a garin kwanaki ke da suka yi mata dadi sosai,kullum yaran na nanuqe da ita suna hira,sauqin abun sun gama jarabawa hutu kawai suke jira,wani lokaci da yammaci anty dije kan debe su da motar mai gidan da ya barta a gida ta kaisu park su dan sha iska suyi ciye ciye su dawo,hakan na yiwa sumayya dadi,lallai ko yaya ka motsa daga wani gu zuwa wani gu zaka samu sauyi zuciyarka zata yi dadi.
Duk wani abu da ya kamata a yiwa amarya anty dije da kanta ta yiwa sumayya,cikin kwana goma ta hadata tsaf.
Ana ya gobe zasu koma kanon laila na kwance kan cinyar sumayya sumayyan na tsefe mata kitsonta zasu wankin gashi da yamma anty dije ta fito ta dubesu
"zan dan shiga gidan daddy prof zamuyi sallama da su,Allah baiyi da ni za'a yi sunan nan ba"sumayya ta daga kai ta dubi anty dije
" au haihuwa akayi halan?"
"Sai yau zaki tambaya kenan,kwana na nawa ina leqa su amma baki taba karar ki shiga ku gaisa da mutanen ba,direban gidan ya dauko ki daga kano fa,surukar gidan ce ta haihu" murmushi sumayya tayi
"To ai ban sansu bane anty"
"Ni ai na sansu kuma gashi na gaya miki,mutanen akwai tsabar mutunci da karrama mutum,duk yadda Allah ya musu tsabar arziqi amma basu raina na qasansu,mai gidan bakiga yadda ya dauki abban khalifa ba kamar dan cikinsa,su khalifa kuwa ya maidasu tamkar jikokinsa" jinjina kai sumayya keyi sannan tace
"Allah ya saka musu da alkhairi,kice ina musu barka"
"Zasuji tunda ba zaki din ba" inji anty dije ta fice tana mita sumayya ta bita da dariya.
Basu jima da kammala tsifar ba anty dijen ta dawo hannunya dauke da baqar leda,ta cillar kan cinyar sumayya
"Da baki iya zuwa gaida mutane ba gashinan haj bilkisu tace na kawo miki kiyi fitar biki,ta yaba da zabin leshin ki wai kin iya zabar kala,ashe tare kuka shiga shagon da mansur din". Baki ta saki sanda ta fiddo leshin taga daya daga cikin wadanda suka siya dinne
"Anty kinsan kuwa nawa ne farashinsa duk guda daya?". Dariya anty dijen tayi
"Hmmmmm,bakisan mutan gidan bane sumayya,kinga ku tashi ku shirya ku wuce wankin kan nan kada dare yayi muku hanya"ta furta tana miqewa ta nufi kitchen.
****** ******* *******
Sanda suka isa kwanaki biyu sukayi saura a daura aure don babu wani event da sumayyan ta tsara yi,yaya abubakar ne kawai zaiyi walima bayan an gama daura aure.
Kusa awa guda kenan da shigowarta gidan amma bata ga wulgawar abdallah ba,tun tana kawaici bata tambaya ba har sai data magantu
"wai nikam ina abdallah ne?" Maimakon maman ta amsa mata sai tace da ita
"Kije malam nason magana da ke" hakanan taji jikinta bai bata ba,ta miqe ta zura hijabinta ta fice.
"Am sumayya,nasan cewa kinsan tsarina da al'ada ta gidan nan,sannan alhamdulillah kin san mutuncin mace dakin mijinta,baki da inda yafi nan daraja,dukkan wani abu da ya faru a baya mu ajjiyeshi gefe haka Allah ya tsarama rayuwarki,cikin KUNDIN QADDARARKI yake,babu wanda ya isa ya goge miki ko ya kautar miki da shi"
"Haka ne malam" ta fada kanta na duqe zuciyarta ba bugawa kamar zata bullo,addu'a take kada Allah yasa malam ya bullo mata da zancan da bata da buqatar jinsa a yanzu
"Sumayya,yaron nan abdur rahman yazo guna ya gabatar min da kansa a matsayin manenin aurenki,to amma kasancewarki bazawara a yanzu addini ya baki damar zabawa kanki mijin aure ya sanya nace sai na tambayeki naji mene ne ra'ayinki,kada ki zalunci kanki a yanzu kina da dama,sannan zaman aure zama ne bana yau ko gobe kawai ba,zama ne na har abada". Wani tashin hankali ne ya rikito mata,abubuwan da suka dinga faruwa da ita zamanin tana auren mukhtar tsaf suka dinga dawo mata,a hankali ta bude bakinta muryarta na rawa
"Kayi haquri malam,abdur rahman dan uwa ne ga mukhtar dan wan babansa ne nasan kasan haka malam" murmushi ya saki
"Sumayya,sumayya kenan,wannan duka ba abun damuwa bane tunda dai aure ya halasta a tsakaninku ba haramun bane" tashin hankali ta fada cikin zuciyarta,'yan uwan mukhtar fa sune dai 'yan uwan abdur rahman,ba'a canzawa tuwo suna
"Malam,ina tsoron sake kasancewa da ahalin su mukhtar...." Sai tayi shiru ta kasa qarasawa,shima shirun yayi yana nazarin maganarta,tabbas sumayya yarinya ce mai matuqar zurfin ciki,a iya zamanta na aure bazai iya fadar ranar data kawo matsalarta ba,saidai idan an fahimta a maganta mata.
"Ke kike da zabi a hannunki ai,ba zan miki auren dole ba"
"Malam,ina so abdur rahman ya janye daga qudurinsa,bana son sake shiga ahalinsu" ta fada zuciyarta na raurawa muryarta na rawa
"Shikenan zancansa ya wuce,sai ki fidda miji ina son hada aurenki da na yayanki abubakar idan ta kama har da su halima baki daya"
"Amma malam ba......."
"Sumayya,bana son qorafi ko wata magana,kinsan ba zaiyiwu kici gaba da zama a gida ba,shekara nawa,shekara daya ana gab da cika ta biyu" shuru tayi don tafi kowa sanin waye malam,amma ina mafita meye mafitarta?,
"Sumayyan luqman fa?" Taji ya jefo mata tambayar wadda ta sanya dago kanta ta dubeshi,murmushi ya kuma yi yana dubanta
"Mamaki kike yadda na sanshi?,ya fara zuwa gunki ba da izini ba ya karya doka ta,hakan ya sanya nayi bincike a kansa,na samu gamsassun bayanai a kansa,mutumin kirki ne bakin gwargwado" sai ya dan ja fasali yana dubanta kafin yaci gaba da cewa.
_yauma dai amin uziri_
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
4⃣0⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*innal laha la yugayyiru maa bi qaumin hatta yugayyiru ma bi'an fusihim*
_haqiqa Allah baya canzawa mutane(halin ko yanayin da suke ciki)har sai sun canza da kansu_
______________________________
Ungawa ce mai matuqar kyau da tsari,akwai nauikan mutane daban daban cikinta,saidai akasarin mzauna cikinta din masu hannu da shuni ne da kuma masu rufin asiri ko wadanda suke ma'aikatan gwamnatin tarayya ta basu gida su zauna kamar su anty dije.
Sai da mansur ya fidda kayanta baki daya ya shigar mata cikin gidan ta masa godiya sosai sannan ya ja motarsa ya shige wani katafare kuma hamshaqin gida dake kallon nasu.
Dukka yaran gidan na nan kasancewar ranar qarshen mako ce,laila ita ce babba,sai hafiz mai bi mata,sannan khalifa sai nasir sai auta amina minal,a qalla laila zata yi shekaru goma sha hudu,ita ta fara ganin shigowar sumayya falon,ihu ta sanya wanda ya janyo hankalin 'yan uwanta ta nufi sumayya ta rungumeta,haka sauran suka baibayeta wanda ya janyo musu faduwa a qasa dukansu suna dariya,da qyar ta samu suka dagata suka koma saman kujera sannan ta soma tambayarsu anty dijen don bata ji motsinta ba,dining laila ta nuna wa sumayyan tana cewa
"Kinga yaya sumayya can duka abincinki ne,tun dazu mama ke jiranki baku iso ba har ta gaji ta shiga gidan daddy prof,amma bari naje na kirata" ta fada tana yafa dan yalolon mayafinta tayi waje da sauri,khalifa sumayya tasa ya fara nuna mata toilet ta shiga tayi alwala,tana kammala alwalar anty dije na shigowa
"Sai yanzu?,gaskiya kunyi nauyi a hanya kamar wadanda suka hau motar haya inji hajiya bilki" murmushi sumayya tayi tana duban anty dije wadda ta sake gogewa bisa dukkan alamu zaman garin ya karbeta matuqa,ta kuma zama 'yar gayu ita da yaranta baki daya
"Wallahi anty sai da muka biya kasuwa muka karbo wasu kaya sannan har mun dau hanya wani oga ko yallabai ya maida ku zoo road karbo dinki"
"Eh inaga man ne dinkunan su'ad ce,maza yi sallar kizo kici abinci kafin mu zauna hirar yashe gamo" ta fada tana sanya su laila dauke akwatunta zuwa wani daki da aka tanada saboda baqi irinta.
Sai da taci ta qoshi sannan suka baje a falon ana hiran yaushe gamo,kusan haka suka qarar da wunin ranar,ko da malamar lesson din yaran ma tazo guduwa sukayi suka qi zuwa sai tafiya tayi,da dare ma yayi da qyar suka tafi dakinsu don cewa sukayi tare da sumayyan zasu kwana,saida anty dije ta korasu saboda tana son suyi zance,sosai suka sake kuwa don mai gidan ta baya nan sun tafi semina lagos,sosai anty dije ta sake kwantar mata da hankali tare da bata shawarwari ta rufe da fadi cikin sigar tsokana
"Duk da nasan sumayyan tawa zuwa yanzu ta fara girma,hankali ya fara zuwa mata" itama dariya tayi,sai wajen sha daya da rabi sannan ta fita ta barta,to nan din ma lukman bai barta ba da hira sai data ce tana jin bacci sannan yace
"Ki kula min da kanki to na baki amanar kanki my dear kinji"ajiyar zuciya ta saki sannan ta amsa masa ta katse kiran,taso kiran halina taji ya abdallah yake,amma ganin dare yayi nisa ya sanyata ta haqura ta barwa gobe,duk sai taji tana kewar yaron nata.
****** ****** ******
Kwanakin da tayi a garin kwanaki ke da suka yi mata dadi sosai,kullum yaran na nanuqe da ita suna hira,sauqin abun sun gama jarabawa hutu kawai suke jira,wani lokaci da yammaci anty dije kan debe su da motar mai gidan da ya barta a gida ta kaisu park su dan sha iska suyi ciye ciye su dawo,hakan na yiwa sumayya dadi,lallai ko yaya ka motsa daga wani gu zuwa wani gu zaka samu sauyi zuciyarka zata yi dadi.
Duk wani abu da ya kamata a yiwa amarya anty dije da kanta ta yiwa sumayya,cikin kwana goma ta hadata tsaf.
Ana ya gobe zasu koma kanon laila na kwance kan cinyar sumayya sumayyan na tsefe mata kitsonta zasu wankin gashi da yamma anty dije ta fito ta dubesu
"zan dan shiga gidan daddy prof zamuyi sallama da su,Allah baiyi da ni za'a yi sunan nan ba"sumayya ta daga kai ta dubi anty dije
" au haihuwa akayi halan?"
"Sai yau zaki tambaya kenan,kwana na nawa ina leqa su amma baki taba karar ki shiga ku gaisa da mutanen ba,direban gidan ya dauko ki daga kano fa,surukar gidan ce ta haihu" murmushi sumayya tayi
"To ai ban sansu bane anty"
"Ni ai na sansu kuma gashi na gaya miki,mutanen akwai tsabar mutunci da karrama mutum,duk yadda Allah ya musu tsabar arziqi amma basu raina na qasansu,mai gidan bakiga yadda ya dauki abban khalifa ba kamar dan cikinsa,su khalifa kuwa ya maidasu tamkar jikokinsa" jinjina kai sumayya keyi sannan tace
"Allah ya saka musu da alkhairi,kice ina musu barka"
"Zasuji tunda ba zaki din ba" inji anty dije ta fice tana mita sumayya ta bita da dariya.
Basu jima da kammala tsifar ba anty dijen ta dawo hannunya dauke da baqar leda,ta cillar kan cinyar sumayya
"Da baki iya zuwa gaida mutane ba gashinan haj bilkisu tace na kawo miki kiyi fitar biki,ta yaba da zabin leshin ki wai kin iya zabar kala,ashe tare kuka shiga shagon da mansur din". Baki ta saki sanda ta fiddo leshin taga daya daga cikin wadanda suka siya dinne
"Anty kinsan kuwa nawa ne farashinsa duk guda daya?". Dariya anty dijen tayi
"Hmmmmm,bakisan mutan gidan bane sumayya,kinga ku tashi ku shirya ku wuce wankin kan nan kada dare yayi muku hanya"ta furta tana miqewa ta nufi kitchen.
****** ******* *******
Sanda suka isa kwanaki biyu sukayi saura a daura aure don babu wani event da sumayyan ta tsara yi,yaya abubakar ne kawai zaiyi walima bayan an gama daura aure.
Kusa awa guda kenan da shigowarta gidan amma bata ga wulgawar abdallah ba,tun tana kawaici bata tambaya ba har sai data magantu
"wai nikam ina abdallah ne?" Maimakon maman ta amsa mata sai tace da ita
"Kije malam nason magana da ke" hakanan taji jikinta bai bata ba,ta miqe ta zura hijabinta ta fice.