Sashe 223
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tana tsaye gaban sink kuwa tana wanke wanken,taji shigowarshi amma sai ta kasa waiwayowa,a hankali ya qarasa bayanta,ya sanya hannayenshi ya kamo qugunta ya manna da nashi,sannan ya hade bayanta da qirjinsa ya dora habarshi saman kafadarta,nannauyar ajiyar zuciya ta saki saboda wani saqo na musamman da jikinsa ya aikata mata
"Wani abu kake so" ta furta qasa qasa
"Ke nake so maman 'yan biyu?,wai baki da labarin nayi kewarki ne?" Sai ta ajjye kwanukan alamar tabar wanke wanken,abinda ahi bai sani ba kunyar shi take ji sosai ta rasa dalili
"Um um ci gaba da wanke wankenki,zamuyi hirar a haka....bani labarin bayan rabuwa baby....nikam nayi rayuwa ne kawai,gani nan tamkar mutum mutumin,ina rayuwa ne tsahon wata biyar ba tare da nasan nau'in dandanonta ba,amma alhamdulillah,tunda alwashin da naci na cikashi" ajiyar zuciya ta saki tana dauraye wani kwano
"Bansan ya zan misalta maka ba noor,rayuwa babu kai ashe tamkar gangar jikin da babu ruhi ce,kullum sai nayi kukan rashinka,raba dare nake ina kokawa da tunaninka,sai inji kaman ka tafi kenan,kaman ba zaka dawo ba kaman yadda anty su'ad ta tafi...." Sai ta saki kwanukan ta juyo tana kallonshi,sannan ta lafe a qirjinsa kaman mai tsoron wani abu
"Don Allah noor.....kada ka sake tafiya ka barmu haka,ni da yara duka muna buqatarka" dagota yayi suna duban juna kafin ya sakar mata qayataccen murmushi mai kwantar da rai
"Ba zata sake faruwa ba my summyyy,ni dinma ina tsananin buqatarku cikin rayuwata....,bari in nuna miki kadan wani dan yanki daga cikin yadda nayi kewarku" bai saurari komai ba ha dagata baki daya tana dariya da roqon ya sauketa zata taka amma ya qiya,yace baiso tayi komai wannan karon shi zai sarrafata yadda yaga dama,zai kuma dauke duk wani aiki daya zama nata ya hada da nashi duka yayi.
Tun da suka haura saman sai kukan amatur rahman ne ya sauko da shi,bako kunya ya daukesu duka ya kaima ummi,baga ce komai ba ta karbesu ya sanya qafa ya fito abinsa ya koma sashen nasu,ranan kuwa can suka kwana,bai karbosu ba itama ummin bata aiko musu da su ba,da yake yaran sun riga da sun saba,ba kuma su fiye shan nono ba,hakan duka bai masa ba,ji yake gidan yayi kadan ya dauki soyayyarsu,da safe ko karuawa basuyi ba ya sata ta shirya suka fice zuwa gidanshin nan,wanda anan kadai yake gani zasu baje kolinsu,ya kuwa baje kolin sin ranshi,ya yiwa soyayyarsa cikin zuciyarta service ta sake dawowa sabuwa fil,ya kuma sake dasa mata yadda zata soshin,irin soyayyar mai zafi mai tsayawa a rai,wanda bata barin zuciya ta huta bare gangar jiki,yayi qara'i iya son ranshi ita kuna ta durqusa ta tallafi dukkan nau'in abinda yazo mata da shi,na hadda ta haddace,na karba ta karbeshi yadda ya kamata.
Kwana daya da wunu taji bai zancan su koma gida,dukan kararta da alkunyarta taci tura,yaranta na cikin ranta abinka da uwa,tana zaune tana miqa masa kayanshi da dai dai yana shiryawa tace
"Allah yasa su amatu zaka dauko min"kai ya girgiza
"Wa?a'ah,ai kisaka rai kin yayesu kawai,tunda ummi ta gayamin babu abinda basu ci....ke infact ma zaki soma rainon ciki ne" gira ta dan ya mutsa a shagwabe
"Wake da cikin,ni?,ni ban gaya maka ba" bai kulata ba har sai da ya gama fesa turarenshi sannan ya fincikota jikinsa ba tare data tsammaci hakan ba,haka ne ya sanyata fadawa jikin nashi gaba daya
"Ke kike da ciki,tsakamin kwanakin dawowata ni na tabbatar da cewa nayi ajiya,kuma ni na gaya miki,kema kuma zaki ga alama nan da four to five weeks....am telling you" dariya tayi kawai tana maida abun wasa,dariyar shima yayi sannan yace
"Zamu ga wanda dariyarsa zata kasance ta nasara"
"Allah ya nuna mana" ta fada cikin basar da zancan,wasa wasa sai ga 'yan biyu shiru har sati guda,suma kuma suna gidan basu komai ba,randa suka cika sati biyu saiga ummi da yaran,cikin girmamawa da kunya ta tarbeta,ummun tace ga 'yan yaye ta dawo da su sunzo kuma ganin gida da Allah ya sanya alkhairi,mamaki ya cikata,wato almustapha yace musu sun dawo nan ne sannan ta yaye yaran,kusan awar ummin biyu sannan ta musu sallama ta tafi ta sanar musu anty maamaa da baba suna nan zuwa.
Abun kaman wasa saiga zancan almustapha ya tabbata,da kanta tayi gwaji da PT strip,kuka ta saki cike da tsoro da fargaba,tayi firgai firgai da ita tana jiran dawowar almustapha,ina zata iya da twince wata bakwai ga wani sabon cikin,sanda ya dawo takw gaya masa dariya ya dinga kwasa abinshi hankalinsa kwance
"Sanda nake gaya miki kin dauka da wasa nake?" Takaici ya cikata,wato shi ko a jikinsa ma,sai abinci da ya jawo yanaci yana baiwa su amatullah sunata darunau abinsu,sai ta fashe da kuka ta miqe ta shige daki,cikin mamaki ya bita da kallo din bai zaci haka ba,sai yaji wani abu na susar ranshi,mamaki bai cikashi ba har ya gama bawa yaran abincin,kafin ya kammala abinda zaiyi sun bingire da bacci,hakan ya sanya ya kwashesu suka shiga dakin,tana takure waje daya tana jan hanci da alama taci kukanta sosai,sanyasu yayi cikin gadonsu dake gefe daya,ya tofesu da addu'o'i sannan ya nufeta,ya jima yana kalllnta kafin yayi qas da murya
"Me ya saki kuka sumayya?!" Tun kafin ta bashi amsa wasu sabbin qwallar suka biyo kuncinta
"Yanzu don Allah ya dace ace na sake samun wani cikin?" Kai ya kada
"Eh ya dace mana,tunda har Allah ya baki yasan cewa ya dace ne" sai ta barke da kuka tana fadin ni wallahi bana so,tun yana lallashinta sai ya fahimci da gaske take,ya tunzura sosai,maganganun data dinga yi suka qona ranshi matuqa,kanshi ya dinga lallasa bai tsitstsinka mata mari ba,sai kawai ya miqe ya dauki kayanshi ya fice a dakin,ranar farko da suka taba raba makwanci kenan tun randa ta zama ita kadai.
Wasa wasa sai qaramin abu ya soma zama babba,dan abu qalilan saita sanya kuka,ta daina kulashi sam,iyakarta da shi gaisuwa sai ko girko,shima sai ya daina ci kota dafa din,yadda ta dafa haka zata zo ta dauke,hakan na bala'in qona mata rai,sam bata jin dadin zaman gidan,amma gani taje itace da gaskiya ita ya kamata a bawa haquri ai,bini bini kuka,ko su amatu ke fada ko rigima yanzu zata sanya kuka,wani lokaci yazo ya kwashe abinsa ta qaracu hamcininta ita kadaj,wani lokaci su kwana ma wajensa,tana can ta kasa bacci saboda rashinsh amma ba zata nuna ko ta sauko ba,abinda ya bata masa fiye sa zato,a hankali ta soma rama,ga laulayi tana fama da shi,cikin haka Allah ya kawo halima abujan sunzo wani seminar ita da abdur rahman ta leqo ta wunan musu,baki kawai halima ga sake tana duban sumayya,yo aiko ita ba zata tafka wannan shirmen ba,shi yasa data shigo tana yabon gida sai uhmm kawai take cewa,abin ma haushi ua bata ta kasa ce mata komai ba harta tafi,dadin abun ma su 'yan biyu babu abinda sukayi,sai girma da suka dada da qiba kaman ana jansu,ashe mama ra zayyanewa komai,ranan raga tashinnhankalin da bata taba gani ba,jin muryar maman ta sauya ya daga hankalinya,ta mata fada kaman ta cinyeta,ta kuma tabbatar mata matuqar bata sauya ba to kaman a kunnen malam,ta kuma sani gamonau bazai mata kyau ba,a rannan ta zauna ta yuwa kanta bita daya bayan daya,istigfari ta dinga yi sanda ta dawo hayyacinta,ta tuna girman zunubin data dauka a wannan tsakanin abinda ta yiwa almustaphan,a ranan ta duk abinda ta danja baya da yi duka ta miqe tayi,tayiwa 'yan biyu kwalliyarsu duk da dama bata fasa ba,amma ta yau din ta musamman ce,ta barau falo cikin kekunansu ta shiga nata wankan,tunda ya shigo ya fahimci sauyi a falon,bai ce komai ba ya kwashe yaransa daketa bangala masa dariya da daga masa hannu kowa na son ya soma daukarta,dariya ta saki ya kwashesu baki daya ta haura sama da su,sannan ya kwashi kekunansun ya kai dakinsa,koda ta fito taga bata gansu ba tasan ya shigo kenan,duk sai taji ba dadi,tabbas bata kyauta ba,ada bai shiga ko fita sai da saninta,amma yanzu duka ta bata wadan nan lamuran,sai data gama shiryawa tsaf cikin wasu sabbanin qananun kaya data taba siya a dubai,bata taba amfani da su ba sai ranar,tayi masifar kyau kai kace sumayyar nan ce 'yar sha takwas,kaman bata haifi yara har uku ba,ta koma saman dining ta kwashe abincin ta jera kan wani kwando mai kyau ta haura saman da su.
"Wani abu kake so" ta furta qasa qasa
"Ke nake so maman 'yan biyu?,wai baki da labarin nayi kewarki ne?" Sai ta ajjye kwanukan alamar tabar wanke wanken,abinda ahi bai sani ba kunyar shi take ji sosai ta rasa dalili
"Um um ci gaba da wanke wankenki,zamuyi hirar a haka....bani labarin bayan rabuwa baby....nikam nayi rayuwa ne kawai,gani nan tamkar mutum mutumin,ina rayuwa ne tsahon wata biyar ba tare da nasan nau'in dandanonta ba,amma alhamdulillah,tunda alwashin da naci na cikashi" ajiyar zuciya ta saki tana dauraye wani kwano
"Bansan ya zan misalta maka ba noor,rayuwa babu kai ashe tamkar gangar jikin da babu ruhi ce,kullum sai nayi kukan rashinka,raba dare nake ina kokawa da tunaninka,sai inji kaman ka tafi kenan,kaman ba zaka dawo ba kaman yadda anty su'ad ta tafi...." Sai ta saki kwanukan ta juyo tana kallonshi,sannan ta lafe a qirjinsa kaman mai tsoron wani abu
"Don Allah noor.....kada ka sake tafiya ka barmu haka,ni da yara duka muna buqatarka" dagota yayi suna duban juna kafin ya sakar mata qayataccen murmushi mai kwantar da rai
"Ba zata sake faruwa ba my summyyy,ni dinma ina tsananin buqatarku cikin rayuwata....,bari in nuna miki kadan wani dan yanki daga cikin yadda nayi kewarku" bai saurari komai ba ha dagata baki daya tana dariya da roqon ya sauketa zata taka amma ya qiya,yace baiso tayi komai wannan karon shi zai sarrafata yadda yaga dama,zai kuma dauke duk wani aiki daya zama nata ya hada da nashi duka yayi.
Tun da suka haura saman sai kukan amatur rahman ne ya sauko da shi,bako kunya ya daukesu duka ya kaima ummi,baga ce komai ba ta karbesu ya sanya qafa ya fito abinsa ya koma sashen nasu,ranan kuwa can suka kwana,bai karbosu ba itama ummin bata aiko musu da su ba,da yake yaran sun riga da sun saba,ba kuma su fiye shan nono ba,hakan duka bai masa ba,ji yake gidan yayi kadan ya dauki soyayyarsu,da safe ko karuawa basuyi ba ya sata ta shirya suka fice zuwa gidanshin nan,wanda anan kadai yake gani zasu baje kolinsu,ya kuwa baje kolin sin ranshi,ya yiwa soyayyarsa cikin zuciyarta service ta sake dawowa sabuwa fil,ya kuma sake dasa mata yadda zata soshin,irin soyayyar mai zafi mai tsayawa a rai,wanda bata barin zuciya ta huta bare gangar jiki,yayi qara'i iya son ranshi ita kuna ta durqusa ta tallafi dukkan nau'in abinda yazo mata da shi,na hadda ta haddace,na karba ta karbeshi yadda ya kamata.
Kwana daya da wunu taji bai zancan su koma gida,dukan kararta da alkunyarta taci tura,yaranta na cikin ranta abinka da uwa,tana zaune tana miqa masa kayanshi da dai dai yana shiryawa tace
"Allah yasa su amatu zaka dauko min"kai ya girgiza
"Wa?a'ah,ai kisaka rai kin yayesu kawai,tunda ummi ta gayamin babu abinda basu ci....ke infact ma zaki soma rainon ciki ne" gira ta dan ya mutsa a shagwabe
"Wake da cikin,ni?,ni ban gaya maka ba" bai kulata ba har sai da ya gama fesa turarenshi sannan ya fincikota jikinsa ba tare data tsammaci hakan ba,haka ne ya sanyata fadawa jikin nashi gaba daya
"Ke kike da ciki,tsakamin kwanakin dawowata ni na tabbatar da cewa nayi ajiya,kuma ni na gaya miki,kema kuma zaki ga alama nan da four to five weeks....am telling you" dariya tayi kawai tana maida abun wasa,dariyar shima yayi sannan yace
"Zamu ga wanda dariyarsa zata kasance ta nasara"
"Allah ya nuna mana" ta fada cikin basar da zancan,wasa wasa sai ga 'yan biyu shiru har sati guda,suma kuma suna gidan basu komai ba,randa suka cika sati biyu saiga ummi da yaran,cikin girmamawa da kunya ta tarbeta,ummun tace ga 'yan yaye ta dawo da su sunzo kuma ganin gida da Allah ya sanya alkhairi,mamaki ya cikata,wato almustapha yace musu sun dawo nan ne sannan ta yaye yaran,kusan awar ummin biyu sannan ta musu sallama ta tafi ta sanar musu anty maamaa da baba suna nan zuwa.
Abun kaman wasa saiga zancan almustapha ya tabbata,da kanta tayi gwaji da PT strip,kuka ta saki cike da tsoro da fargaba,tayi firgai firgai da ita tana jiran dawowar almustapha,ina zata iya da twince wata bakwai ga wani sabon cikin,sanda ya dawo takw gaya masa dariya ya dinga kwasa abinshi hankalinsa kwance
"Sanda nake gaya miki kin dauka da wasa nake?" Takaici ya cikata,wato shi ko a jikinsa ma,sai abinci da ya jawo yanaci yana baiwa su amatullah sunata darunau abinsu,sai ta fashe da kuka ta miqe ta shige daki,cikin mamaki ya bita da kallo din bai zaci haka ba,sai yaji wani abu na susar ranshi,mamaki bai cikashi ba har ya gama bawa yaran abincin,kafin ya kammala abinda zaiyi sun bingire da bacci,hakan ya sanya ya kwashesu suka shiga dakin,tana takure waje daya tana jan hanci da alama taci kukanta sosai,sanyasu yayi cikin gadonsu dake gefe daya,ya tofesu da addu'o'i sannan ya nufeta,ya jima yana kalllnta kafin yayi qas da murya
"Me ya saki kuka sumayya?!" Tun kafin ta bashi amsa wasu sabbin qwallar suka biyo kuncinta
"Yanzu don Allah ya dace ace na sake samun wani cikin?" Kai ya kada
"Eh ya dace mana,tunda har Allah ya baki yasan cewa ya dace ne" sai ta barke da kuka tana fadin ni wallahi bana so,tun yana lallashinta sai ya fahimci da gaske take,ya tunzura sosai,maganganun data dinga yi suka qona ranshi matuqa,kanshi ya dinga lallasa bai tsitstsinka mata mari ba,sai kawai ya miqe ya dauki kayanshi ya fice a dakin,ranar farko da suka taba raba makwanci kenan tun randa ta zama ita kadai.
Wasa wasa sai qaramin abu ya soma zama babba,dan abu qalilan saita sanya kuka,ta daina kulashi sam,iyakarta da shi gaisuwa sai ko girko,shima sai ya daina ci kota dafa din,yadda ta dafa haka zata zo ta dauke,hakan na bala'in qona mata rai,sam bata jin dadin zaman gidan,amma gani taje itace da gaskiya ita ya kamata a bawa haquri ai,bini bini kuka,ko su amatu ke fada ko rigima yanzu zata sanya kuka,wani lokaci yazo ya kwashe abinsa ta qaracu hamcininta ita kadaj,wani lokaci su kwana ma wajensa,tana can ta kasa bacci saboda rashinsh amma ba zata nuna ko ta sauko ba,abinda ya bata masa fiye sa zato,a hankali ta soma rama,ga laulayi tana fama da shi,cikin haka Allah ya kawo halima abujan sunzo wani seminar ita da abdur rahman ta leqo ta wunan musu,baki kawai halima ga sake tana duban sumayya,yo aiko ita ba zata tafka wannan shirmen ba,shi yasa data shigo tana yabon gida sai uhmm kawai take cewa,abin ma haushi ua bata ta kasa ce mata komai ba harta tafi,dadin abun ma su 'yan biyu babu abinda sukayi,sai girma da suka dada da qiba kaman ana jansu,ashe mama ra zayyanewa komai,ranan raga tashinnhankalin da bata taba gani ba,jin muryar maman ta sauya ya daga hankalinya,ta mata fada kaman ta cinyeta,ta kuma tabbatar mata matuqar bata sauya ba to kaman a kunnen malam,ta kuma sani gamonau bazai mata kyau ba,a rannan ta zauna ta yuwa kanta bita daya bayan daya,istigfari ta dinga yi sanda ta dawo hayyacinta,ta tuna girman zunubin data dauka a wannan tsakanin abinda ta yiwa almustaphan,a ranan ta duk abinda ta danja baya da yi duka ta miqe tayi,tayiwa 'yan biyu kwalliyarsu duk da dama bata fasa ba,amma ta yau din ta musamman ce,ta barau falo cikin kekunansu ta shiga nata wankan,tunda ya shigo ya fahimci sauyi a falon,bai ce komai ba ya kwashe yaransa daketa bangala masa dariya da daga masa hannu kowa na son ya soma daukarta,dariya ta saki ya kwashesu baki daya ta haura sama da su,sannan ya kwashi kekunansun ya kai dakinsa,koda ta fito taga bata gansu ba tasan ya shigo kenan,duk sai taji ba dadi,tabbas bata kyauta ba,ada bai shiga ko fita sai da saninta,amma yanzu duka ta bata wadan nan lamuran,sai data gama shiryawa tsaf cikin wasu sabbanin qananun kaya data taba siya a dubai,bata taba amfani da su ba sai ranar,tayi masifar kyau kai kace sumayyar nan ce 'yar sha takwas,kaman bata haifi yara har uku ba,ta koma saman dining ta kwashe abincin ta jera kan wani kwando mai kyau ta haura saman da su.