Sashe 211
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin mota shiru sumayyan tayi,tana tunanin yadda rayuwa take sauyawa bawa a duk sanda Allah yaso,haqiqa rayuwa abar tsoro ce ga dukkan mai tunani,wannan kadai ya isa bawa ishara yasan cewa babu wani abu dake dawwama nan duniya banda ikon Allah,walau dadi ko wuya,komai na wuceea ne tamkar a mafarki,gefw daya tunanin su'ad ya fado mata
"Babyyyyy...." Almustapha ya kira sunanta wanda hakan shi ya sanyata dago kanta ta dubeshi,sai ta dora hannunta saman nashi hannun dake kan giyar motar
"Tunanin me kike yi?" Kai ta kada
"My...meke damun su'ad?" Kai ya kada yana duban titi
"Nima ban sani ba"
"Amma ya kamata ka binciki damuwarta kaji ko?", kusan shekaran jiya abinda yayi kenan,ya tsirata da tambaya,bata da amsa daga bisani ma kuka ta sanya mata tana gaya masa so taje ta gansu daga shi sai ita,duj da akwai wannan cikin zuciyarta amma babban abinda yafi damunta shine ta yaya zata dauki ciki itama kaman sumayyan?,ta samu soyayya tattali da kulawa irin tata?,duk da babu abinda ya rageta da shi
"bansan me take so na mata ba cikin duniya,ban rageta da komai ba,ba abinda ban bata ba babu kuma abinda bana mata,ko yaushe qoqarin tanqwara zuciyata nake don ma saba da halayyarta amma ko da yashe sabon hali take qirqiromin,bana son na aikata mata wani abu da ba dai dai ha ko don mutuncin mahaifinta,ina girmamashi,ina ganin qimarshi....amma ko yaushe kamar ina tunzura ta haka na......" Shiru yayi ba tare daya qarasa ba,ko da can shi bai tattauna matsalar wata cikinsu da wata,ya sani cewa inda hakan me yiwuwa ne sumayya abokiyar shawararshi ce,halayenta sunyi dari bisa darin da ya tabbatar zata iya bashi shawara da mafita kan koma mene ne,shiru itama tayi,ta tabbatat da cewa ya kai maqura shi yasa har yau yake furta wadan nan kalaman,hannunshi take matsawa a tausashe har sai da taji ya saki ajiyar zuciya sannan a hankali ta furta
"Am sorry....Allah ya shiga lamuranmu"
"Amin" ya furta yana jin dadin lafazinta.
Maganar noman audugar da ya sanya ake masa a qasar kano jigawa da zaria ta taso,hakan ya sanya ya shirya zuwa nigeria cikin satin,cikin ikon Allah sai kuma ga haihuwar halima,wadda ta sauka lafiya ta samu namiji,daman can yana da niyyar tafiyar da su don haka ra'ayinshi yake,saboda haka yace su shirya,zasu sauka kano da sumayya,zai barta nan su wuve jigawa da zaria da su'ad tunda ita sumayyan tafiyar zata iya yi mata wahala,hakan itama yayi mata,ko banza tasan zatayi hidimar sunanta hankali kwance,kishin dake damun su'ad cikin zuciyarta tace sam ita ba zata je ba,me zata je yi wani zaria da jigawa?,ta rasa wajen zuwa sai nan?,ranshi ya baci,shima kuma ya motsa qwanjinsa ya nuna mata mazantaka yace sai taje,hakanan ba yadda ta iya ta haqura zata bishin,itakam sumayya ko a jikinta,shiri ta soma yi sosai tana siyan tsaraba,duk da ya hanata fitan tana daga gida take siyayyar ake kawo mata.
Ana gobe su nuwaira zasu tafi suka kawo mata ziyara,tana daki kwance aka shaida mata tana da baqi,ta miqe cikin farinciki ta tar besu har zuwa falonta,duk da nauyin data yi bata zauna ba sai data tana dar musu komai,zata dora abinci rumaisa tace a'a sam,itama tana fama da kanta ne,suma kuma a qoshe suke snack din kawai ya isa,bata rabo da kayan snacks zuwa su dambun nama saboda almustapha,wani lokaci su kadai yake ci a matsayin abinci,hakan ya sanya take yinsu ta saka su a freezer sanda zaici sai ta dauko idan na soyawa ne ta soya masa,idan na gasawa ne ta gasa masa.
Hira suke wadda kusan rabinsu da nuwaira suke yinta,jifa jifa rumaisa ke saka musu baki
"Ina maman naku karima ne?" Murmushi nuwaira tayi
"Daddy ya saketa ta koma garinsu,yanzu kullum bakiga yadda take masa naci ya maidata ba wai ta tuba hajiya tace sam bata dawowa wa,yanzu ma wai ta kusa aure a can" kai sumayya ke jinjinawa,abinda ya faru shine,baki daya rayuwan yaran da mai gidan komawa tayi wajen hajiya,sai kariman ta koma tamkar wata saniyar ware a cikinsu,suna sashen hajiya suna walwalarsu tana vangarenta ita kadai kamar mayya,duk wani qoqari na dawo da yaran rayuwarta da mai gidan amma abu yaci tura,a hankali karima ta soma fita daga kansa,a lokacinne ita kuma ta soma gane kurenta,tayi laqwas ta soma biyayyar qarfi sa yaji saboda ta fuskanci ba wata mafita gareta,saidai ina tunu ta gama fita akan lukman din baki daya,bare hajiya wadda tayi shiru ne kawai saboda darajar yaran da kariman ke da su,uwa uba kuma tayi alqawarin ba zata sake saka dan nata ya saki wata cikin matanshi ba har abada,don taga ishara,Allah ya kawo qarshen zaman nasu,hajiya ta wayi gari lukman ya saki karima har saki biyu,qememe yace bazai maidata ba,don ya kamata da kanshi tana zuba wani abu cikin abincin hajiyan,wanda magani ne qarshe aka bata matuqar baiyi aiki ya dawo mata da rayuwar gidanta yadda take ba daa to malamin nata ya gaya mata tayi haquri kawai,sai gashi bata zuba a sa'a ba ya zama silar tsinkewar igiyar aurenta.
Bayan mutuwar auren da wasu watanni hajiya ta soma sha'awar dawowar rumaisa mahaifiyar nuwaira gidan,wadda ita daya ce ta haihu da lukman,macen kuma data fi duka saurab matan da ya taba aura tsantsar haquri da biyayya,faduwa tazo daidai da zama,don shi dinma rumaisan ke kai kawo cikin ranshi,tunda ya tabbatar da ceea ya rasa sumayya,wadda kabatin aurenta a abuja ya gigitashi fiye da zato,ya soma binciken wanda ta aura,sanda yaci karo da labarin cewa doctor muhammad almustapha mukhtar gombe ne tilas ya aro haquri ya yafawa kanshi,saboda ya kwana da sanin babban goro ne sai magogin qarfe,hakanan bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane,bayan sun rabu da karima sun hadu da rumaisan kusan sau uku a gurare daban daban,saidai ko dubanshi bata yiba bare ya samu fuskar tunkararta,soyayyar da sukayi bata zaci zai rabu da ita haka da wuri ba ba laifin tsaye ba na zaune,ya karbi umarni kawai daga mahaifiyarsa,da qyar aka shawo kanya harda hajiyan wajen lallashi sannan ta yarda aka maida aurensu,wanda dawowarta ya sake dawo da walwalar gidan kaman zamanin da sumayya kenan,duk da hakan basu manta da ita ba kullum kwanan duniya su da hajiya sai sunyi zancanta,wanda har rumaisa ta saba da ji,takan zauba ta tayasu wani lokaci,ko daya rumaisa bata bari abinda karima ta yiwa diyarta yayi tasiri a ranta ba har ta rama kan yaranta guda hudu data bari,ta hadasu ta rungume kamar ita ta haifesu,sannan taci gana da dorawa kan tarbiyyar da sumayya ta azasu wanda hakan yayi mata dadi sosai.
Wannan shi ake kira da QADDARA saiga rumaisa ta zama ita din dai itace matar lukman,dawowarra ba dadewa harkokin lukman suka bude sosai,wanda hakan bai rasa nasaba da yadda ya maida kai wajen kyautatawa hajiyarshi ita kuma taci gaba da binsa da addu'a,cikin qanqanin lokaci ya sake habaka,ya sauya gida da abubuwa masi dama cikin rayuwarshi data yaranshi,basu dade da komawa sabom gida ba rumaisa ta samu juna biyu,wanda yanzu haka siyayyar haihuwa tazo yi sanda yayarta dake kasuwanci zata zo dubai lukman ya masu visa ita da nuwaira suka taho,wanda yace girma yake bi,zuwa na gaba kuma mai biwa nuwaira da ita za'a babbar yarinyar kariman.
Basu wuce awa biyu ba suka yi sallama zasu wuce,suka rabu kowannensu na tsokanar dan uwansa kan sai sunzo suna,ta musu alaqawarin indai tazo kano matuqar mai gidan ya barta zata shigo ta gaida hajiya,amma su isar mata da gaisuwar tata wajen hajiyan kafin ta iso da su basma baki dayansu,a haka suka rabu.
Kwana hudu tsakani suma suka tashi zuwa kano,saukar yamma sukayi saboda haka kai tsaye suka wuce gidan baba wanda nan suke sauka dama,ba haka sumayya taso ba,so tayi ya barta ya sauka gida amma ya hade gabas da yamma ya qiya,saboda yau ne zata amshi kwananta,farincikinsa shine sama da nata saboda haka itama ta danne tata buqatar ta haqura.
Yana bakin gado yana shafa mai ta fito itama daga wanka,daure da towel amma ya dage mata saboda tsinin cikinta,kallonta yake cikin shauqi yana lumshe idanu,saboda yadda ta masa wani kyau,fatarta kana kallanta kasan ta samu hutu,ruwan wanka yayi dai dai kan fatarta,miqews tsaye yayi ya isa bayanta inda take tsaye gaban madubi tana tsane jikinta,ya kama qugunta ya manna a jikinsa,sai ta lafe tana dubanshi ta jikin mudubi fuskarta wasai
"Wannan cikin naki kaman ya wuce watanninsa fa.....na qagu ya fito zuwa yanzu ya soma hanani aiwatar da wasu abubuwa yadda ya kamata,baki daya kin zama wata lazy,perfomance dinki ya ragu babe" kanta ta langabar saman kafadarshi a shagwabe
"Duk rawar gaban hantsin da kake sha abinka noor?" Habarta ya kama ya riqe
"Yanzun idan nace ina son mu shiga babbar headquater nayi rawar gaban hantsin za'a barni?" A gajiye take tabbas,amma ta sani so yake ya qureta don ya samu abun tsokana,hakan ya sanya ta dan janye jikinta ta waiwayo tana dubanshi
"An gaya ma raguwa ce ni?" Gira ya dage dariya na cinsa ya daga kafadarsa
"Wa yasani?"
"Bari in nuna maka" ta fada tana nufar saman gado,sosai dariya ke cinsa,shikenan ya gama mata wayo,baisan yaushe sumayyar zatayi wayo ba,duk da yana maraba da irin wannan rashin wayon nata,gunta ya isa yana qunshe dariyarsa,yayin da ya lullubeta cikin qirjinsa,yana aika mata da zafafan saqonminsa cikin zafi zafi masu dumama duniyar ma'aurata wadda ke qunshe da tsantsar soyayya qauna da kuma shauqi.
Ranar baki daya ba inda ya fita,da qyar ta lallabashi ya rakata kitchen ta musu abinci mai sauqi suka dawo daki.
"Babyyyyy...." Almustapha ya kira sunanta wanda hakan shi ya sanyata dago kanta ta dubeshi,sai ta dora hannunta saman nashi hannun dake kan giyar motar
"Tunanin me kike yi?" Kai ta kada
"My...meke damun su'ad?" Kai ya kada yana duban titi
"Nima ban sani ba"
"Amma ya kamata ka binciki damuwarta kaji ko?", kusan shekaran jiya abinda yayi kenan,ya tsirata da tambaya,bata da amsa daga bisani ma kuka ta sanya mata tana gaya masa so taje ta gansu daga shi sai ita,duj da akwai wannan cikin zuciyarta amma babban abinda yafi damunta shine ta yaya zata dauki ciki itama kaman sumayyan?,ta samu soyayya tattali da kulawa irin tata?,duk da babu abinda ya rageta da shi
"bansan me take so na mata ba cikin duniya,ban rageta da komai ba,ba abinda ban bata ba babu kuma abinda bana mata,ko yaushe qoqarin tanqwara zuciyata nake don ma saba da halayyarta amma ko da yashe sabon hali take qirqiromin,bana son na aikata mata wani abu da ba dai dai ha ko don mutuncin mahaifinta,ina girmamashi,ina ganin qimarshi....amma ko yaushe kamar ina tunzura ta haka na......" Shiru yayi ba tare daya qarasa ba,ko da can shi bai tattauna matsalar wata cikinsu da wata,ya sani cewa inda hakan me yiwuwa ne sumayya abokiyar shawararshi ce,halayenta sunyi dari bisa darin da ya tabbatar zata iya bashi shawara da mafita kan koma mene ne,shiru itama tayi,ta tabbatat da cewa ya kai maqura shi yasa har yau yake furta wadan nan kalaman,hannunshi take matsawa a tausashe har sai da taji ya saki ajiyar zuciya sannan a hankali ta furta
"Am sorry....Allah ya shiga lamuranmu"
"Amin" ya furta yana jin dadin lafazinta.
Maganar noman audugar da ya sanya ake masa a qasar kano jigawa da zaria ta taso,hakan ya sanya ya shirya zuwa nigeria cikin satin,cikin ikon Allah sai kuma ga haihuwar halima,wadda ta sauka lafiya ta samu namiji,daman can yana da niyyar tafiyar da su don haka ra'ayinshi yake,saboda haka yace su shirya,zasu sauka kano da sumayya,zai barta nan su wuve jigawa da zaria da su'ad tunda ita sumayyan tafiyar zata iya yi mata wahala,hakan itama yayi mata,ko banza tasan zatayi hidimar sunanta hankali kwance,kishin dake damun su'ad cikin zuciyarta tace sam ita ba zata je ba,me zata je yi wani zaria da jigawa?,ta rasa wajen zuwa sai nan?,ranshi ya baci,shima kuma ya motsa qwanjinsa ya nuna mata mazantaka yace sai taje,hakanan ba yadda ta iya ta haqura zata bishin,itakam sumayya ko a jikinta,shiri ta soma yi sosai tana siyan tsaraba,duk da ya hanata fitan tana daga gida take siyayyar ake kawo mata.
Ana gobe su nuwaira zasu tafi suka kawo mata ziyara,tana daki kwance aka shaida mata tana da baqi,ta miqe cikin farinciki ta tar besu har zuwa falonta,duk da nauyin data yi bata zauna ba sai data tana dar musu komai,zata dora abinci rumaisa tace a'a sam,itama tana fama da kanta ne,suma kuma a qoshe suke snack din kawai ya isa,bata rabo da kayan snacks zuwa su dambun nama saboda almustapha,wani lokaci su kadai yake ci a matsayin abinci,hakan ya sanya take yinsu ta saka su a freezer sanda zaici sai ta dauko idan na soyawa ne ta soya masa,idan na gasawa ne ta gasa masa.
Hira suke wadda kusan rabinsu da nuwaira suke yinta,jifa jifa rumaisa ke saka musu baki
"Ina maman naku karima ne?" Murmushi nuwaira tayi
"Daddy ya saketa ta koma garinsu,yanzu kullum bakiga yadda take masa naci ya maidata ba wai ta tuba hajiya tace sam bata dawowa wa,yanzu ma wai ta kusa aure a can" kai sumayya ke jinjinawa,abinda ya faru shine,baki daya rayuwan yaran da mai gidan komawa tayi wajen hajiya,sai kariman ta koma tamkar wata saniyar ware a cikinsu,suna sashen hajiya suna walwalarsu tana vangarenta ita kadai kamar mayya,duk wani qoqari na dawo da yaran rayuwarta da mai gidan amma abu yaci tura,a hankali karima ta soma fita daga kansa,a lokacinne ita kuma ta soma gane kurenta,tayi laqwas ta soma biyayyar qarfi sa yaji saboda ta fuskanci ba wata mafita gareta,saidai ina tunu ta gama fita akan lukman din baki daya,bare hajiya wadda tayi shiru ne kawai saboda darajar yaran da kariman ke da su,uwa uba kuma tayi alqawarin ba zata sake saka dan nata ya saki wata cikin matanshi ba har abada,don taga ishara,Allah ya kawo qarshen zaman nasu,hajiya ta wayi gari lukman ya saki karima har saki biyu,qememe yace bazai maidata ba,don ya kamata da kanshi tana zuba wani abu cikin abincin hajiyan,wanda magani ne qarshe aka bata matuqar baiyi aiki ya dawo mata da rayuwar gidanta yadda take ba daa to malamin nata ya gaya mata tayi haquri kawai,sai gashi bata zuba a sa'a ba ya zama silar tsinkewar igiyar aurenta.
Bayan mutuwar auren da wasu watanni hajiya ta soma sha'awar dawowar rumaisa mahaifiyar nuwaira gidan,wadda ita daya ce ta haihu da lukman,macen kuma data fi duka saurab matan da ya taba aura tsantsar haquri da biyayya,faduwa tazo daidai da zama,don shi dinma rumaisan ke kai kawo cikin ranshi,tunda ya tabbatar da ceea ya rasa sumayya,wadda kabatin aurenta a abuja ya gigitashi fiye da zato,ya soma binciken wanda ta aura,sanda yaci karo da labarin cewa doctor muhammad almustapha mukhtar gombe ne tilas ya aro haquri ya yafawa kanshi,saboda ya kwana da sanin babban goro ne sai magogin qarfe,hakanan bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane,bayan sun rabu da karima sun hadu da rumaisan kusan sau uku a gurare daban daban,saidai ko dubanshi bata yiba bare ya samu fuskar tunkararta,soyayyar da sukayi bata zaci zai rabu da ita haka da wuri ba ba laifin tsaye ba na zaune,ya karbi umarni kawai daga mahaifiyarsa,da qyar aka shawo kanya harda hajiyan wajen lallashi sannan ta yarda aka maida aurensu,wanda dawowarta ya sake dawo da walwalar gidan kaman zamanin da sumayya kenan,duk da hakan basu manta da ita ba kullum kwanan duniya su da hajiya sai sunyi zancanta,wanda har rumaisa ta saba da ji,takan zauba ta tayasu wani lokaci,ko daya rumaisa bata bari abinda karima ta yiwa diyarta yayi tasiri a ranta ba har ta rama kan yaranta guda hudu data bari,ta hadasu ta rungume kamar ita ta haifesu,sannan taci gana da dorawa kan tarbiyyar da sumayya ta azasu wanda hakan yayi mata dadi sosai.
Wannan shi ake kira da QADDARA saiga rumaisa ta zama ita din dai itace matar lukman,dawowarra ba dadewa harkokin lukman suka bude sosai,wanda hakan bai rasa nasaba da yadda ya maida kai wajen kyautatawa hajiyarshi ita kuma taci gaba da binsa da addu'a,cikin qanqanin lokaci ya sake habaka,ya sauya gida da abubuwa masi dama cikin rayuwarshi data yaranshi,basu dade da komawa sabom gida ba rumaisa ta samu juna biyu,wanda yanzu haka siyayyar haihuwa tazo yi sanda yayarta dake kasuwanci zata zo dubai lukman ya masu visa ita da nuwaira suka taho,wanda yace girma yake bi,zuwa na gaba kuma mai biwa nuwaira da ita za'a babbar yarinyar kariman.
Basu wuce awa biyu ba suka yi sallama zasu wuce,suka rabu kowannensu na tsokanar dan uwansa kan sai sunzo suna,ta musu alaqawarin indai tazo kano matuqar mai gidan ya barta zata shigo ta gaida hajiya,amma su isar mata da gaisuwar tata wajen hajiyan kafin ta iso da su basma baki dayansu,a haka suka rabu.
Kwana hudu tsakani suma suka tashi zuwa kano,saukar yamma sukayi saboda haka kai tsaye suka wuce gidan baba wanda nan suke sauka dama,ba haka sumayya taso ba,so tayi ya barta ya sauka gida amma ya hade gabas da yamma ya qiya,saboda yau ne zata amshi kwananta,farincikinsa shine sama da nata saboda haka itama ta danne tata buqatar ta haqura.
Yana bakin gado yana shafa mai ta fito itama daga wanka,daure da towel amma ya dage mata saboda tsinin cikinta,kallonta yake cikin shauqi yana lumshe idanu,saboda yadda ta masa wani kyau,fatarta kana kallanta kasan ta samu hutu,ruwan wanka yayi dai dai kan fatarta,miqews tsaye yayi ya isa bayanta inda take tsaye gaban madubi tana tsane jikinta,ya kama qugunta ya manna a jikinsa,sai ta lafe tana dubanshi ta jikin mudubi fuskarta wasai
"Wannan cikin naki kaman ya wuce watanninsa fa.....na qagu ya fito zuwa yanzu ya soma hanani aiwatar da wasu abubuwa yadda ya kamata,baki daya kin zama wata lazy,perfomance dinki ya ragu babe" kanta ta langabar saman kafadarshi a shagwabe
"Duk rawar gaban hantsin da kake sha abinka noor?" Habarta ya kama ya riqe
"Yanzun idan nace ina son mu shiga babbar headquater nayi rawar gaban hantsin za'a barni?" A gajiye take tabbas,amma ta sani so yake ya qureta don ya samu abun tsokana,hakan ya sanya ta dan janye jikinta ta waiwayo tana dubanshi
"An gaya ma raguwa ce ni?" Gira ya dage dariya na cinsa ya daga kafadarsa
"Wa yasani?"
"Bari in nuna maka" ta fada tana nufar saman gado,sosai dariya ke cinsa,shikenan ya gama mata wayo,baisan yaushe sumayyar zatayi wayo ba,duk da yana maraba da irin wannan rashin wayon nata,gunta ya isa yana qunshe dariyarsa,yayin da ya lullubeta cikin qirjinsa,yana aika mata da zafafan saqonminsa cikin zafi zafi masu dumama duniyar ma'aurata wadda ke qunshe da tsantsar soyayya qauna da kuma shauqi.
Ranar baki daya ba inda ya fita,da qyar ta lallabashi ya rakata kitchen ta musu abinci mai sauqi suka dawo daki.