Sashe 217
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Da sallama bakinsa ya shiga dakin sanda take gaban sif tana fidda kayansu tana shiryawa cikin akwati,yaran na kwance cikin gadonsu suna bacci hankalinsu kwance,cukin tsafta da qamshi,a qunshe suke cikin kayan baby masu taushi pink,yanayin muryarshi kawai taji ta saki abinda take ta waiwayo tana dubanshi,duk sanda taji muryarshi haka tasan ranshi a bace yake koda yayi yu qurin boye mata,bai dubeta ba har ya isa gaban gadon yaran ya bude dan net din dake matsayin qofa ya zura kanshi,kissing kowannesu yayi yana lumshe idanunshi,qamshinsu da kyan da suka yi suna ratsashi,kaso hamsin cikin dari na bacin ranshi take ya kwaranye,sai da ya gama duddubasu sannan ya sake rufesu,ya waiwayo suka hada idanu da sumayya,kusan tare suka sakarwa juna murmushi,qare mata kallo yake yana takowa inda take tsaye,rigar jikinta ta kamata ta fidda surarta qarara,ga na shanunta fa suka cika sun zauna das jikinta har wani qyalli suke,hankalinshu bai kwanta ba sai da yasanyata cikin jikinsa ya dora hannayenshi saman qirjinta yana yawo da shi yana lumshe ido
"Me kike a tsaye...ke da na gaya miki bacci nakeso kiyi?" A tausashe tace
"Na gaji noor,kuma gobe zamu wuce kaga dole na hada mana kayan da zamuyi amfani da su ko?" Kai ya kada
"noo,kada mi wahalar da kanki,babu wani abu da zaku dauka a nan,akwai komai can an tanada" mamaki ya kasheta,kada dai ya gaya mata ya sake wata siyayyar ne bayan wadda yayi a nan,bakinta ta bude da niyyar magana,saidai ba bata dama ba ya hade bakin nasu waje daya ya soma aika mata da saqo.
Da qyar ta qwaci kanta gajin yana yunqurin wuce makadi da rawa tana maida numfashi,da baya ta soma ja ya dinga binta idanunsa kafe a nata yana dariya
"Me na tsorata haka babe?"Kai ta langabe
"jego fa nake noor...ni wallahi na yafewa anty su'ad kai ka manta yadda mukayi da kai jiya?"
"Don kin yafe kata kuma sai ki haramtamin romancing dinki?,baki isa ba wallahi,wannan tamkar rai da numfashi ne kinga babu mai rabawa ko?"
"Haba noor ka tausaya min mana" ta fada kaman zatayi kuka sanda ya cimmata,kamata yayi sosai yana duban qwayar idanunta
"Toni cewa nayi zanyi wani abu?,kawai dai a barni na dinga hutawa,kuma Allah idan kika yarda kika wani zauna zaman me ake cewa zaki gani shayi ruwa ne,ko an miki tayi kice kawai ni zaki biyo,sati daya kawai zamuyi mu dawo,if not kuwa wallahi takanas zan baro dubai na taho nigeria suburbudarki in koma abina" sosai kalmar ta bata dariya har tana toshe bakinta,yayin da shima ya saki qaramar dariyar yana rage zafi,motsin farkawar usaina ya sanyashi sakinta
"Kina da zabi kan sunayen yaran nan?" Kai ta kada tana kallonshi
"Bani da zani,duk abinda ka yanke dai dai ne" murmushi ya saki,ko yaushe tana maida shi yana jin kansa tamkar wani sarki,komai yayi da rayuwarta bata da zabi dai dai ne,hakan ke qara mata qima a idanunshi
"Amatullah da amatur rahman" idanunta ta juya tana murmushi,sunayen sun mata,sunaye ne masu kyau da ma'ana,bai bi iyayi ko dadin suna a baki ba
"Allah ya musu albakarka,ya sanya ma'anar sunayen ta bisu"
"Amin ya rahman ya rahim"shi yaje ya daukota ya kawo mata ita,har yau bai taba ganin tana shayar da su ba quru quru,hakan ya sanya yau ya titsiyeta,ganin ta tsaya nuqu nuqu ya sanyashi zura hannunshi da kanshi ya dauko mata ya sa mata a baki sannan ya sake daidaita mata riqonta yadda isaka ba zata shiga bakin yarinyar ba sanda take shan nono,dubansu yake cikin shauqi qauna soyayya da burgewa,har sai da tayi kaman zata tsole masa ido tace
"Kada ka cinye mu mana ha'an?" Qawataccen murmushi ya saki,ya jawota jikina yana cewa
"Da zai yiwu hadiyekun zanyi na huta wallahi baki daya,saboda bansan ya zan fassara miki yadda nake jinku cikin zuciyata ba" lumshe idanu tayi,kalamansa na ratsata,tana godewa Allah tare da qarawa kanta qwarin gwiwar yadda zata ci gaba da yi masa biyayya don ta mallaki zuciyarsa fiye da yadda ta mallaka a yanzu,saboda sau da yawa kyautatawa itace ke mai da d'a ya zama bawa,to itakam kyautatawar da take masa ta sanyashi ya zama tamkar bawa a gareta.
****** ****** *******
Cikin cikakkiyar kama da kamala take sanye cikin atamfa riga da zani da wadataccen mayafi,haka almustapha ke sanye da wani yadi irin na sarakai da aka yiwa aikin gidan sarauta,takalmi zuwa hular kanshi duka irin na gidan sarauta ne,sunyi kyau sosai,zallar farinciki qauna da girmamawa juna ta bayyana a tsakaninsu,su'ad ma na sanye da doguwar riga ta gown,saidai a sake take bata kama wani sashe na jikinta ba,almustapha ke dauke da hassana ita kuma na dauke da usaina,karon farko data fara daukar yaran,wanda ganin idanun almustapha yasa ta daukesu,tana son tayi wani abu da zai barta zuwa gida,saidai tana ji kaman tayi jifa da yarinyar,kamar wadda ke dauke da garwashin wuta haka take jinta,tun daga harabar gidan ya isa ya sanar maka akwai baqi a gidan,hakan kuwa yake,anty farida da yaranta,huda da yaranta,oga amira,anty ni'imah wadda ta taho da hibba da hibban sun bar biyu a gida legos tare da mamarsu sai ana ya gobe suna zasu iso.
Ashe baki daya suna daga gefe suna jiran qarasowarsu ciki,take kowa yayi tsaye bakin motar fuskarshi qunshe da murmushi,ba don shakkar ya man din ma da suke ba da babu shakka tuni sun ruge bakin motar suna rigengeniyar daukarsu,amma duk da tsare gidanshi hakan bai hana amira saurin amshe usaina dake hannun su'ad ba,tunu ta sakar mata dama neman mai dauka take,a rayuwarta kusan zata iya irga sau nawa ta dauki jariri,ko da can ita ba mai son yara bace,balle ma ina ta gansu,anty maamaa ita ta karbi hassana,take waje ya kacame da murna,hayaniyarau ta soma tashi,suna mata sannu tare da nuna tsantsar farinciki da kyautar da Allah ya yiwa ahalin nasu na 'yan biyu,wanda wannan ne karon farkonda suka samesu,hakan ya sanya shi janye sumayya zuwa sashen ummi wadda alkunya ta sanyata bata fito ba tun basu saka shi ciwon kai ba.
Nauyi da kunya suka hanata hada ido da ummi,itakam wannan karon ummin yakice ku yar tayi,don sai data rungume sumayya cikin jikinta tana mata sannu sannan ta zaunar da ita saman kujera bayan tasa an kashe ac da fankar dake falon,a nan kowa ya shigo hira sabuwa murna da hada hada ta tashi,gefanta ya zagaya ya rada mata
"Kada ki bari su wahalarmin da daughters,kema ban yarda kiyi hayaniya can ba" a kunyace ta gyada kai,suka hada ido da wasu daga cikin wadanda ke wajen,sai ya tsare gida ya fice abinsa zuwa bangarensu wanda can su'ad ta nufa dama.
A ranar nafeesa dake garin tazo qaraso gidan,suna tare har anty dije,sai ga abida ma wadda dama su tun jiya ita da hamza suka yo gaba,tana son duba mamarta da aka kwantara asibiti duk da ta warware ma,bata samu kanta ba sai da suka tafi,sanda ta sake wanka ta kuma ci abincin,yaran ma tuni anty maamaa ta wankesu ta shiryasu tsaf zasu wajen baba su gaisa,ta dan kama kumatunsu taba cewa
"Saura kuje ku qwace mana miki kuma,kubar ganinku haka farare nunar rana" dariya amira dake zaune wajen tayi
"Haba maamaa kema kinsan saidai kuyi haquri keda ummi,gwamnatinku ta rushe rumumus" ta fada itama cikin raha wanda ya sanyasu darawa.
Ita amira da anty maamaa suka fito suka nufi sashen baban,hanya suka ci karo da almustaphan tare da su'ad,wanda da alama can zasun,hakan ya sanya maamaa miqawa su'ad ummulkhair tace
"Sai ku qarasa kawai ko na shigo daga baya daman zai kawo mishi kununshi" kamar ba zata karba ba har suka so fahimtar haka,saidai tasa hannu ta karba sheqeqe,kau da kanta sumayya tayi kaman bata gani ba,yayin da amira bakinta ya fara rawa tana son yin magana sumayya ta danneta,ashe hakan ya taba ran almustapha
"Kula mana" ya fada a kausashe,dolenta ta gyara riqon suka ci gaba da takawa,saidai amira bata yadda ba tana biye da su'ad a baya har suka isa.
"Me kike a tsaye...ke da na gaya miki bacci nakeso kiyi?" A tausashe tace
"Na gaji noor,kuma gobe zamu wuce kaga dole na hada mana kayan da zamuyi amfani da su ko?" Kai ya kada
"noo,kada mi wahalar da kanki,babu wani abu da zaku dauka a nan,akwai komai can an tanada" mamaki ya kasheta,kada dai ya gaya mata ya sake wata siyayyar ne bayan wadda yayi a nan,bakinta ta bude da niyyar magana,saidai ba bata dama ba ya hade bakin nasu waje daya ya soma aika mata da saqo.
Da qyar ta qwaci kanta gajin yana yunqurin wuce makadi da rawa tana maida numfashi,da baya ta soma ja ya dinga binta idanunsa kafe a nata yana dariya
"Me na tsorata haka babe?"Kai ta langabe
"jego fa nake noor...ni wallahi na yafewa anty su'ad kai ka manta yadda mukayi da kai jiya?"
"Don kin yafe kata kuma sai ki haramtamin romancing dinki?,baki isa ba wallahi,wannan tamkar rai da numfashi ne kinga babu mai rabawa ko?"
"Haba noor ka tausaya min mana" ta fada kaman zatayi kuka sanda ya cimmata,kamata yayi sosai yana duban qwayar idanunta
"Toni cewa nayi zanyi wani abu?,kawai dai a barni na dinga hutawa,kuma Allah idan kika yarda kika wani zauna zaman me ake cewa zaki gani shayi ruwa ne,ko an miki tayi kice kawai ni zaki biyo,sati daya kawai zamuyi mu dawo,if not kuwa wallahi takanas zan baro dubai na taho nigeria suburbudarki in koma abina" sosai kalmar ta bata dariya har tana toshe bakinta,yayin da shima ya saki qaramar dariyar yana rage zafi,motsin farkawar usaina ya sanyashi sakinta
"Kina da zabi kan sunayen yaran nan?" Kai ta kada tana kallonshi
"Bani da zani,duk abinda ka yanke dai dai ne" murmushi ya saki,ko yaushe tana maida shi yana jin kansa tamkar wani sarki,komai yayi da rayuwarta bata da zabi dai dai ne,hakan ke qara mata qima a idanunshi
"Amatullah da amatur rahman" idanunta ta juya tana murmushi,sunayen sun mata,sunaye ne masu kyau da ma'ana,bai bi iyayi ko dadin suna a baki ba
"Allah ya musu albakarka,ya sanya ma'anar sunayen ta bisu"
"Amin ya rahman ya rahim"shi yaje ya daukota ya kawo mata ita,har yau bai taba ganin tana shayar da su ba quru quru,hakan ya sanya yau ya titsiyeta,ganin ta tsaya nuqu nuqu ya sanyashi zura hannunshi da kanshi ya dauko mata ya sa mata a baki sannan ya sake daidaita mata riqonta yadda isaka ba zata shiga bakin yarinyar ba sanda take shan nono,dubansu yake cikin shauqi qauna soyayya da burgewa,har sai da tayi kaman zata tsole masa ido tace
"Kada ka cinye mu mana ha'an?" Qawataccen murmushi ya saki,ya jawota jikina yana cewa
"Da zai yiwu hadiyekun zanyi na huta wallahi baki daya,saboda bansan ya zan fassara miki yadda nake jinku cikin zuciyata ba" lumshe idanu tayi,kalamansa na ratsata,tana godewa Allah tare da qarawa kanta qwarin gwiwar yadda zata ci gaba da yi masa biyayya don ta mallaki zuciyarsa fiye da yadda ta mallaka a yanzu,saboda sau da yawa kyautatawa itace ke mai da d'a ya zama bawa,to itakam kyautatawar da take masa ta sanyashi ya zama tamkar bawa a gareta.
****** ****** *******
Cikin cikakkiyar kama da kamala take sanye cikin atamfa riga da zani da wadataccen mayafi,haka almustapha ke sanye da wani yadi irin na sarakai da aka yiwa aikin gidan sarauta,takalmi zuwa hular kanshi duka irin na gidan sarauta ne,sunyi kyau sosai,zallar farinciki qauna da girmamawa juna ta bayyana a tsakaninsu,su'ad ma na sanye da doguwar riga ta gown,saidai a sake take bata kama wani sashe na jikinta ba,almustapha ke dauke da hassana ita kuma na dauke da usaina,karon farko data fara daukar yaran,wanda ganin idanun almustapha yasa ta daukesu,tana son tayi wani abu da zai barta zuwa gida,saidai tana ji kaman tayi jifa da yarinyar,kamar wadda ke dauke da garwashin wuta haka take jinta,tun daga harabar gidan ya isa ya sanar maka akwai baqi a gidan,hakan kuwa yake,anty farida da yaranta,huda da yaranta,oga amira,anty ni'imah wadda ta taho da hibba da hibban sun bar biyu a gida legos tare da mamarsu sai ana ya gobe suna zasu iso.
Ashe baki daya suna daga gefe suna jiran qarasowarsu ciki,take kowa yayi tsaye bakin motar fuskarshi qunshe da murmushi,ba don shakkar ya man din ma da suke ba da babu shakka tuni sun ruge bakin motar suna rigengeniyar daukarsu,amma duk da tsare gidanshi hakan bai hana amira saurin amshe usaina dake hannun su'ad ba,tunu ta sakar mata dama neman mai dauka take,a rayuwarta kusan zata iya irga sau nawa ta dauki jariri,ko da can ita ba mai son yara bace,balle ma ina ta gansu,anty maamaa ita ta karbi hassana,take waje ya kacame da murna,hayaniyarau ta soma tashi,suna mata sannu tare da nuna tsantsar farinciki da kyautar da Allah ya yiwa ahalin nasu na 'yan biyu,wanda wannan ne karon farkonda suka samesu,hakan ya sanya shi janye sumayya zuwa sashen ummi wadda alkunya ta sanyata bata fito ba tun basu saka shi ciwon kai ba.
Nauyi da kunya suka hanata hada ido da ummi,itakam wannan karon ummin yakice ku yar tayi,don sai data rungume sumayya cikin jikinta tana mata sannu sannan ta zaunar da ita saman kujera bayan tasa an kashe ac da fankar dake falon,a nan kowa ya shigo hira sabuwa murna da hada hada ta tashi,gefanta ya zagaya ya rada mata
"Kada ki bari su wahalarmin da daughters,kema ban yarda kiyi hayaniya can ba" a kunyace ta gyada kai,suka hada ido da wasu daga cikin wadanda ke wajen,sai ya tsare gida ya fice abinsa zuwa bangarensu wanda can su'ad ta nufa dama.
A ranar nafeesa dake garin tazo qaraso gidan,suna tare har anty dije,sai ga abida ma wadda dama su tun jiya ita da hamza suka yo gaba,tana son duba mamarta da aka kwantara asibiti duk da ta warware ma,bata samu kanta ba sai da suka tafi,sanda ta sake wanka ta kuma ci abincin,yaran ma tuni anty maamaa ta wankesu ta shiryasu tsaf zasu wajen baba su gaisa,ta dan kama kumatunsu taba cewa
"Saura kuje ku qwace mana miki kuma,kubar ganinku haka farare nunar rana" dariya amira dake zaune wajen tayi
"Haba maamaa kema kinsan saidai kuyi haquri keda ummi,gwamnatinku ta rushe rumumus" ta fada itama cikin raha wanda ya sanyasu darawa.
Ita amira da anty maamaa suka fito suka nufi sashen baban,hanya suka ci karo da almustaphan tare da su'ad,wanda da alama can zasun,hakan ya sanya maamaa miqawa su'ad ummulkhair tace
"Sai ku qarasa kawai ko na shigo daga baya daman zai kawo mishi kununshi" kamar ba zata karba ba har suka so fahimtar haka,saidai tasa hannu ta karba sheqeqe,kau da kanta sumayya tayi kaman bata gani ba,yayin da amira bakinta ya fara rawa tana son yin magana sumayya ta danneta,ashe hakan ya taba ran almustapha
"Kula mana" ya fada a kausashe,dolenta ta gyara riqon suka ci gaba da takawa,saidai amira bata yadda ba tana biye da su'ad a baya har suka isa.