← Book details Sakar Makafi Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 113

Sashe 52

Sakar Makafi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

.......“Hakan shine yafi dacewa”. Shugaban ƙasa ya amsa yana kallon Imran ɗin shima, sai kuma ya cigaba da faɗin, “Domin idan aka bayyana, za su motsa. Idan aka ɓoye… za mu gan su suna motsi. Dole Imran zai koma ɓoyayyen ma'aikaci a wajenka daga shi har Haydar, dan karka manta akwai kaki a jikinsu, kuma suna da ƙarfin iko a waccan bishiyar ma. Dole kuma su cigaba da zama dan inuwarsu zata mana amfani cikin wannan ɓoyayyar tafiyar, ta haka ne zasu banbance ganyen daya bushe akan bishiyar da suke”.
       Cikin gamsuwa da jinjina kai Dada ya miƙa hannu ya ɗauki takardar a karo na farko, bai kalle ta ba. Sai dai kai tsaye ya furta,
       “Yaushe aiki zai fara?”
   “Ba a wannan daren ba. Amma daga yau… ka riga ka fara.”
      Dada ya ɗauki kofin sabon shayinsa da Imran ya sake zuba masa, dan sun shanye coffee ɗin farko tuni, ya kai bakinsa. Sai da yasha ya ajiye sannan ya furta.
      “Idan haka ne, ku shirya kawai.” daga haka ya miƙe. Shugaban ƙasa ya miƙe shima, hakama Imran da ya furta kalmar;
       “Da me?”
  Dada ya kallesa, idanuwansa sun yi sanyi amma murya ta yi kaifi. Kai tsaye ya bashi amsa da.
       “Da komai ma. Domin wannan karon… ba zan tsaya tsaka-tsaki ba. Zan yi aiki kunne a toshe, ido a makance. Ba uba, ba ɗa, ba ƙani, ba aboki, ba mata koda tsautsayi ya gitta”.
         Shugaban ƙasa ya kalleshi na ɗan lokaci yana siririyar dariya, sannan ya ce, “In sha ALLAHU ma baza'a kai ga nan ba ZAKIN IMRAN”. Ya ƙare maganar yana miƙa musu hannu alamar su yi musabaha. Sai da suka ɗan dara a tare, kafin musabahar dake nunin abubuwa masu yawa.
      Ba murmushi. Ba alkawari mai yawa akan ɗagama kowa ƙafa. Sai dai akwai fahimta. Sannan akwai tabbatarwar a waje ƙungiyar duhu na jira. A gida, zuri'a da iyalai na kusa.
A ɓoye munafukai na motsi.....

>>>>>>>%<<<<<<<

      WASHE GARI JUMA'ATU babbar rana. Ranar da kan biɗa ka samu da izinin UBANGIJI mai taskar da bata girgiza balle ƙarewa. Babu wanda yasan lokacin da Dada ya dawo gidan a daren jiya. Wayar gari kawai sukai suka ganshi. Ganin nasa ma su Uncle Ja'afar ne kawai a wajen fita massalaci sallar asubahi. Su Nimrah kuwa har suka kammala shirin makaranta suka fito basu san ma mi gidan yake ciki ba. Sai da suka fito kai tsaye Mammah tace bazasu makaranta ba sun mance abinda suka aikato jiya. Dole su jira sai anji halin da yaron ke ciki gudun abinda zai iya zuwa ya dawo.
        Ko'a jikinsu dan daɗi ma suka ji, tuni suka koma ɗaki suna tsallen murna suka cire uniform. Hankali kwance suka sake hayewa gidajensu suka duƙun ƙune a barguna bayan sun kashe fitilu sun saki labulale da ƙara gudun ac. Babu kuwa wanda ya sake jin labarinsu bare motsin su har sha biyun rana. Koda Mammah ta saka Kulu ta tado mata su suzo suyi breakfast samu tai sun kulle ƙofa ma. Bugun duniya kuma babu ƙo motsinsu sai kawai ta ƙyalesu.
        Kaf mazan gidan yau suna gida. Dama su Ma'aruff basa fita kasuwa juma'a, Bilal da Ammar ne kawai sukaje aiki. Kuma sun taso da wuri saboda tafiya massalaci. Dada kam babu wanda ya gansa a safiyar har yanzu. Yana ɗakinsa. Da yake ya sanar ma Mammah zai yi barci ne sanda ya shiga suka gaisa da asuba, dan shi yama ce ta hana su Nimrah zuwa makaranta shiyyasa bata damu da rashin fitowar tasa ba balle tayi jajensa...
        Sai misalin ƙarfe sha biyu da kwata duk suna falo ana hira sai gashi ya sakko. Ƙamshinsa shi ya fara ratsa hancinansu kafin bayyanarsa. Babu wanda baiyi tasbihi a ransa ba ga UBANGIJIN halittar wannan bawa. Dada ko yaya sutura take idan ya saka tana masa kyau matuƙa, koda ba mai daraja bace. Sai dai fa manyan kaya sukan zama na musamman dake ƙara masa kamala da cikar haiba tamkar uniform ɗin aiki. Dan a shekarun baya Imran yasha tsokanarsa da kalmar (bai taɓa ganin wanda uniform kema ƙyau a jiki irinsa ba). Ko a lokacin baya ce masa komai, wani lokacin ma sai dai ya samu tukuycin harara.
Received at 5:42 PMReactions:      Ƙaramar dariya shugaban ƙasa yayi, dan yanda Imran ɗin yayi dole kai dariya. Shi kansa uban gayyar duk da ya fuske sai da ya murmusa a zuciyarsa.
       Janar ya buɗe drawer jikin center table ɗin ya zaro wata takarda, Imran ya miƙawa yana faɗin, “Ba takardar aiki ba. Umurni ne. Jagorancin sashen tsaro na musamman”. Ya maida idanunsa kan Dada. “Kai kaɗai zaka ba da rahoto kai tsaye gare ni. Kana da damar haɗa ɓoyayyar rundunar aiki, a cikin kowanne jami'an tsaro na ƙasar nan ko farar hula. Sai dai ka sani zan saka ɓoyayyen tsaro a bayanka, dan kai ma tsaron lafiyarka zai koma ƙarƙashin ikona ne daga yau a gida da waje. ALLAH ya bamu fiye da nasarar da muke fata da buƙa”.
        “Amin ya rabbi ranka ya daɗe”. Cewar Imran cike da farin ciki. Dada ma ya ɗan yi murmushi kaɗan. Sai kuma cikin ɗan taɓe lips ya furta.
     “Sir! A ɓoye baiyi ƙarfi ba? Karfa ka manta akwai soji biyu tare da ni.” ya ƙare maganar da kallon Imran...........✍️
Received at 5:42 PM
reacted with 🥰          Shi ya fara gaishe da Mammah kafin su ma duk su gaishe shi. Koda Mammah ta masa maganar abinci ce mata yay sai sun dawo massalaci.
    “Zama da yunwa ko Muhammad? Bafa ka karya ba”.
     Murmurshi yay mata. “Mammah nasha Coffee”.
        “Coffee ba abinci bane ai, yanzu dai ko milk tea a haɗa maka”.
    Bai ce komai ba, dan yasan in ma bai sha ba hankalinta bazai kwanta ba. Kafin Mammah tai magana Biebah ta miƙe kusan lokaci guda da Lailah. Mammah tace Lailah ta koma ta zauna ita dake fama da kanta. Dan yau Shariffa ma gaida Mammah kawai tazo tayi ta koma sashenta alamar ɗan baba nata harama. Dan har asibiti ma Yaya Ja'afar ɗin yaso su wuce taƙi, acewarta a ɗan dai saurara tunda ba wani ciwo take ji mai tsanani ba, kawai dai jikin ne baya mata daɗi. Biebah ce taje tai mata komai a sashenta, su Abees kam sai Lailah ta haɗasu tai musu shirin makaranta dan su sunje.
      Yana kammala sha suka wuce massalaci. Bayan wucewar tasu Mammah da kanta taje ya tada su Nimrah. Da ƙyar suka zo suka buɗe mata ƙofar kuwa. Korasu tai suje suyi wanka, ita kuma ta fice nata ɗakin. Koda suka fito fes da su, duk da ba wasu kaya masu nauyi suka saka ba amma da yake yaran Mammah masha ALLAH sai suka fito darr. Hanoon kawai suka samu a falon tana kallo, ko kallon inda take basuyi ba suka wuce kitchen, dan tsabar neman magana ma hanci Ruky ta rufe, sai kuma ta ɗauki turaren SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. Ta saka bonner. Mi Nimrah zatai inba dariya ba. Harda wani faɗin, “Sai dake Trouble Buddy na”.
       Ruky kam ta fuske kamar bata aikata komai ba. Hanoon ta shaƙa sosai, sai dai batayi magana ba. Haka suka zauna suka fara cin abinci suna hira da dariya data saka Hanoon daina fahimtar Film ɗin ma gaba ɗaya. Fitowar Biebah ya taimaki Hanoon. Dan Biebah data fahimci abinda ke faruwa sai ta ɗauke musu hankali da labarin ƙawarta Chef Yakudima, tace su tambayi su Yaya Ma'aruff su biya musu su shiga makarantar koyon girke-girken ta tunda gashi za'a shiga hutu.
      Ruky na bala'in son harkar girke-girke, Nimrah ce ma sai a hankali tanan ɓangaren, dan ma Ruky na jan ra'ayinta shine ma take ɗan taɓawa. Suna tsaka da wannan hirar ne Mammah ta fito. Koda taji batun da suke sai itama ta gamsu da shawarar Biebah ɗin, tace ta binciko ya tsarin yake. Cike da farin ciki Ruky ta rungume Mammah. Dariya suka saka mata harda su Kulu da suka fito, dan kowa yasan yanda take son harkar. Daga nan aka fara hirar girki. Nimrah da yake ba so take ba taƙi saka baki, Hanoon ma sai wani yatsine-yatsinen fuska take yi.
     Mammah datai tunanin ya kamata a gyaro ɗakin Dada duk da baiyi magana ba tace Nimrah taje ta gyaro tunda ba hirar take ba. Nimrah bata son aiki, dan haka kamar zatai kuka ta fara roƙon Ruky ta rakata suyi, ita ko Ruky hankalinta nakan kallon videos ɗin Chef Yakudima a YouTube channel tace bazata ba. Nimrah taji haushi kuwa ta wuce fuuuu. Sai kawai Hanoon ta saka mata dariya. Ta juyo zatai magana Ruky ta ƙyafta mata ido alamar karta kulata. Bako ta tanka ɗin ba ta wuce, itama Rukyn ta cigaba da kalle-kallen ta kamar ba'ai komai ba. Biebah data fahimci abinda sukayi sai taji tausayin Hanoon tayi kamata, dan wlhy tasan wata tsiyar zasu ƙulla mata ne, ga dai Afeef nan ya koma ɗangyasa ƙafa yau, baki yayi tumm na kumbura abin tausayi.

       ★Tunda ta buɗe ƙofar ta shigo, wani ƙamshi mai ratsa zuciya ya daki hancinta, kasa haƙuri tai sai da ta wani lumshe idanunta tana sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi. Harga ALLAH tana son ƙamshi, dan ƙamshi duniya ne. Ɗakin ta fara bi da kallo bayan ta zube kayan sharar, babu wani tarkace sannan babu datti, sai saman gadon ne ma dake barbaje da takardu, sai laptop. Sannan daga study table ɗin da basu san sanda aka shirya shi ba an saka wani babban board fari, an mammana hotuna a jikinsa. Ba iya gane hotunan take ba, saboda an saka board ɗin sama sosai, hotunan kuma kanana ne kamar na passport.
Received at 5:42 PMReactions:
68
Chapter 52 · 0% Book details