← Book details Nur Firdaus Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 31 OF 96

Sashe 31

Nur Firdaus Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

nur taji tausayin layla sosai dan intana kuka tana bada hakuri zaka rantse da Allah cewa bata san komi ba wanda ko yatsa aka samata a baki bazata iya taunawa ba, cikin tallafo fuskanta nur tace ni ban ce miki kidena kyautata masa ba, its ur dressing and timing. shi namiji ne ke mace, shi ba muharaminki bane da zakije masa daki da sssafe half naked, qaddara koda mahaifinmu ne na asali hakan bai dace ba, sabida kowani dan Adam yana da rauni na shaawa..babban misali itace ummi da mummy take kan kkri akan case dinta, kenan kinga mahaifi zai iya keta ma yar cikin sa haddi..gara ummi bata zama trigger ba tsantsan jarabawa ne amma ke kuma fa? in wani abu ya sameki zai kasance da lefinki aciki kin fahimce ni.?

cikin kuka sosai layla ta gyada kai kamar ta fahimta din nur firdaus ta lallasheta sosai har tay shiru yauma tea kawai suka sha suka fito a shirye tsaf tsaf farin kayansu da blue trousers dinsu yasha karin guga dukansu sunyi kyau kusan kowaccensu sarauniyar kyauce in her own way.

Lokacin da suka shiga mota Malam Liman ya ɗaukesu don kai su makaranta ta ICICE Academy a Abuja A yayin da suka kama hanya Nur Firdaus ta cigaba da karatun Alkur’ani ahnkli cikin wata irin nutsuwa wacce take karawa Malam Liman jin daɗi.

Layla dake zaune a bayan mota babu abunda takeji face tsananin haushin yadda duk abin da Nur Firdaus takeyi yake burge kowa.

a zuciyarta tana haɗiyen bakin ciki tace wani abun ma sai munje kaduna ko hm hmm Yanzu haka duk inda aka ji muryar Nur, sai a yabata, I just hope she dosnt get the trophy sumhow, itama taji yadda akeji .

bayan uban tulin kokarin danayi kwana biyu wajen jan hanklin sa amma lkci guda sadaat wai yazo yana bin bayanta agaba na hmm...wann abun bakaramin ci mata rai yakeyi ba haryan xu.

Tana cikin raya wnan tunanin aranta har suka isa kan titin makaranta sed kafin su karasa isa ƙofar shiga caraf saiga wata dankararryar black GLK me dauke da tambarin kanem shehuri, kafin kace wani abu Adnan shehuri ya Bayyana ata gabansu nan da nan malam liman yay parking ata wani fili nan kusa da gate din makaranta snn ya saukesu anan ya juya abunsa.

wani karamin panick attack ne yaso ya turnuke kirjin laylah ta tsaya ajikin wani flower tanajin kamar ana tsikarar kirjinta da madarar ruwan kishi dan sosai taji kirjinta na kkrin bugawa da matsanncin zafi.

adnan ya fito ya dan tsaya kusa da ƙatuwar motarsa mai masifar kyau gashi yyi wani irin azaban kyau cikin wata blue shadda mai shegen tsada da kyalli kyakkwar siririn fuskar shin nan na cike da kawataccen annuri acikin zumudi ya nufo inda suke da sauri sauri yana wani irin murmushi me taushi

kallo daya zaka masa kasan yay matukar kewar masoyiyarsa wacce gabaki daya taji kamar an sassare mata gabobin jiki dan suprise ne wanda kwata kwata bata shirya cin karo da shi yau ba

har ya iso wajen yana kallon Nur Firdaus da murmushi mai kyau a fuskansa, nur ta dago kanta sama ahankli suka hade idonsu waje guda, muryansa har wani rawa rawa yake ayayinda yace ""supriseee,.. ya dada kallonta farin cikin ganinta nadada kufce masa cikin dariya me sanyi kirjinshi na bugu yace habibty u look stunning anya kinyi missing dina kuwa?..

idonta take ya cika da ruwa tana dan murmushi akunyace muryanta na fita ahnkli sosai tace Adnan?how comes..what is this..

Dariya yay yace this is called "i cant live witout you anymore..nury i cant breath in banganki yau ba..so i have to come and see you.

nur firdaus ta kasa cewa komi tanata kallon shi da ruwan hawaye a idonta da bai sauko kasa ba tana murmshi mesanyi dan wani irin sabuwar kaunarsa taji na masifar tsattssafo mata aranta bana wasa ba

cikin dedeta nitsuwar sa yace hey i am sorry na san ban kasance tare da ke ba kwana biyu amma ina fatan dan wnn mamakin dana baki yasa na dan wanke kaina..

Nur Firdaus ta kalli Adnan din da tsananin mamaki jikinta ya ɗan yi sanyi saboda kunyar yadda tayita damuwa tanamai raya wasu abubuwa dayawa aranta harta fara tsammanin ko wani abu canza daga wajen sa ne.

duk kunyar idon students dake lekowa suna kallon su ata wajen yasata kasa magana na ɗan lokaci sai can sannan ta ja wata dguwr numfashi.

cikin wata murya mai taushi suka gaisa layla tana tsaye a kusa da su cikin wani yanayi batace mai uffan ba shima bai kulata ba.

nur ta kallesa tace
Adnan amma ka dawo kenan ko? pls tell me ure not going away anymore. jiya mukayi waya amma kuma shine ba ka sanar da ni zakazo yau ba ."

Adnan yana yar dariya
yace kawai naso ya zama miki bazata ne habibty, yana murmushi sosai yace "and dats not all, wait here ina zuwa kinji??

nur batace komi ba, layla tafaraji inama ace da ita akeyin wann fallasashen soyayyar dake burgewa kowa, dan gani tay yawancin student na ta lekowa ta wajensu ana gulma.

babu karya Adnan ya hadu kuma yanayinsa gabaki daya kallo daya xakamai kasan an sangartashi da uban gata da kuma dukiya.

gaban tsadaden motarsa ya bude ya dauko wata katoton wrap box da bonquet na rose flower akai shikansa da kyar ya cincinbo box din a hannunsa yana zuwa dashi ya miƙa ma nur firdaus sann ya cire wani ƙaramin abu aciki kamar ƙaramar jaka mai kyau wacce take cike da wasu irin kyaututtukar ababen ci irinsu chokoclate candies and lot more masu shegen tsada da kyar nur ta karɓa cikin jin kunya tana masa godiya shikuma ya cigaba da bata hakurin rashin samun time dinsa akanta na kwana biyu.

Layla da ke tsaye a tana kallon su da gefen idanu zuciyarta yana wani irin tafarfasa da baqar hassada da kuma tukukin kishi, a zuciyartan har matsar hawaye takeyi a boye wai Me yasa kullum yaa nur ce take samun abubuwan da nice nake mafarkin samun su,..sai kace naci ja'ba?...wht is wrong with me, Ni fa? Ni kuma fa?...

Adnan ya dan ɗauki lokaci yana hira da Nur Firdaus cikin shauƙi na soyayya, ayayin da Layla ke tsaye tana ƙoƙarin krikran murmushi, da kyar ma nur ta ja hanklinsa kan laylan suka gaisa sama sama, iya daurewa ta daure domin ta basar duk dama zuciyarta tana ta juyawa da ruwan wuta.

tahowar jadidah wajen ne yazo ya dan katse soyayyar tasu cikin raha da wasa da dariya jadida ta riko hannun layla data ja baya suka tsaya daf dasu, tanata gaya ma adnan yadda nur firdaus ta damu da bayanan shima yana fadin yanayin dayake shiga.

duk basusan cewa wuta suke hurawa akirjin layla ba

jadidah tace mude muna Allah Allah ranar yazo muga ranar aurenku. love is in the Air ynxu haka duk cikin schl ya dauka da zancen ku hmmm the power couples. dariya nur firdaus tay ahnkli tace ai saiki kamashi dan shine ya jawo mana wann tulin publicity da suprise dinsa.

Adnan yace well forgive me princess but i love u privately, publically, madly, unapologetically, and crazily... saidai yan makrnta suyi min uzuri..as a matter of fact i am counting days to marry you.

kunya sosai ya rufe nur firdaus bata iya ce mai komi ba, sabida da dan karfi ya fada jadida ta saka dariya me karfi tana mai bubbuga kafadun layla dan tana balain jn dadin yadda adnan yake mutuwar son nur wanda yasa layla ta kasa iya dauriya basu hankara ba kawai sukaji numfashinta yay sama can kamar wacce take da chronic asthmatic condition

nur firdaus tay saurin rikota da mamaki.

layla layla layla meyasa meki

jadida data rike hannun laylan take jikinta ya bata cewa chocking kawai layla tay sai taji mmki ya cika mata zuciya duk da bata kawo komi aranta ba

she is having a panick attack da sauri adnan yaje ya dauko ruwan gora amotar sa ya mika ma nur firdaus

jadidan ta rike layla sosai zasu bata ruwan kawai saita fara amai
batay me yawa ba ta tsaya hawaye ya cika fuskanta, nur tahau wanke mata baki tana kkrin zata bata ruwan abki cikin tsananin kishi layla ta ture hannunta ta cigaba da tarin, jadida ta karbi ruwan ta mika mata sann ta karba ta sha cikin kankanin lkci ta dawo dede.

tambayar duniyan nan an ma layla amma tace musu sam she is fine kura ne ya shake mata wuya sabida buga mata kafada da jadida tay da take dariya..

haka jadida ta bata hakuri maganan ya wuce kowa na lura da yadda layla ta sauya fuska ta dan tsime bata murmushi amma banda adnan danshi baima san metake ciki ba kuma bai wani damu da yanayinta ba. kowa na biye mata ana tambayarta ana mata sannu sannu amma shikam banda shi, hakan ya sa layla tafara tunanin yadda zata tabbatar da cewa komai ya lalace tsakaninsu da nur firdaus. aranta tace Wannan karon ba za ta bar soyayyarsu ta yi nasara ba.

yau din tamkar wata baqae rana ne datay mugun zafi wa rayuwar layla dan har zuciyarta taji zafi da kishi akan yar uwata nir firdaus iri wanda bata tabajinshi arywarta ba.

ga takaicin sadaat ga baqin cikin Adnan ta rasa wanne zataji da shi yau kusan duk wanda ya tabata a schl sai kaga ta hau fada dashi ko kaga ta sunkuyar dakai akan desk dinta tanata kuka kamar me aljanu.

daga bangaren nur firdaus kuwa kawarta jadida ce ta cike mata kunne da labarin irin shirin auren da akeyi ma Adnan idan mum dinsa taci zabe, domin kuwa ana shirin yin babban hidima ne a auren adnan din kalan wanda duk kasa zai dauka da labarinsa.

gyada mata kai kawai nur firdaus takeyi ana hirar acikin shirme da dariya amma har ranta bawani son hakan takeyi ba duk dama tasan iyakar abunda kawai zata yi tasaka ma adnan da alheri kenan ta saka shi farinciki snn ta kasance matarsa ta har abada.
Chapter 31 · 0% Book details