Sashe 97
Luu Luu Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
"Kowa ya wuce zuwa aikin gabansa" Aisa ta bawa duk wanda ke tsaye a parlor din umarni,yayin da yalwa ta qarasa korar kowa.
Hannun shehnaz da akhnan din aisa ta kama da sauran dakakkiyar zuciyarta,ta kuma jasu kai tsaye zuwa daya daga cikin bedrooms din akhnan din suka shige ciki sannan ta maida qofar ta kulle ta kuma murza key.
Tunda ta hango tahowar yalwa ta miqe tsam tana fuskantarta gami da jiran isowarta.
Zubewa zatayi kaman yadda ta saba,saidai ayau hannu mammina ta saka ta riqe kafadar yalwa.
"Me ya faru?" Ta mata tambayar da dukkan zaquwarta nason jin abinda ya biyo baya.
Tamkar a gaban mammina din akayi komai haka yalwa ta tsara mata,sannan tayi qasa da kanta a yau din tana jin nauyi tsaiwa gaban mammina a maimakon durqushewa a gabanta suyi magana yadda ta saba.
Kamar saukar ruwa da daukewarsa gurin ya dauki shuru,sai kuma sautin siririyar dariyar mammina ta ratsa gurin.
"Zatasha guba?" Ta sake tambayar yalwa. Kai ta jinjina mata.
"Qwarai haka tace". Kai ta kuma jinjinawa.
"A gaban aqalla jama'ar da sukakai adadi nawa?".
"Hadimanta da yawa.....ciki harda ranta ya dade aisa da shehnaz". Kai ta sake jinjinawa.
"Hakan yayi kowa ya shiga lissafi.....ZATA SHA GUBA" Ta fadi kai tsaye tana sakin kafadar yalwa gami da yin taku uku baya don bada tazara tsakaninta da yalwa din.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Kai yalwa ta daga da sauri tana duban mammina din,abinda ya jawo hankalinta ta sake maida dubanta ga yalwa,da wannan murmushin da a idanu da yawa yake bayyana zallar kirkinta da karamcinta......saidai a wasu lokutan kebantattu,a wasu idanun a wasu yanayiyyikan yake zama baqin murmushi,kuma mafi munin murmushi.
"Zata sha guba kamar yadda tace.....nayi laifi?,ita ta zabawa kanta ko?" Ta qarasa maganar tana duban yalwa. Da sauri yalwa ta girgiza kai
"Ba shakka......zabinta kenan.....furucinta na qarshe kuma kenan". Dage dukka kafadunta biyu tayi tana takawa hankalinta kwance.
" Tamim za'a nemo?" Yalwa ta fada tana duban bayan mammina. Maganan yalwar taja hankalinta,ta tsaya can na wasu mintuna kafin ta waiwayo tana dubanta.
"Yaushe kika fara min hasashe da kutsa kai cikin wasu abubuwan da ba'a gayyaceki ko an nemi tajin ta bakinki ba?" Da hanzari tayi qasa da kanta,jikinta ya soma rawa a hankali,tana kuma tuna LAURATU a shekarun baya da suka shude......a shekarun daba ITACE AKAN WANNAN MATSAYIN BA LAURATU CE
"Afuwa nake nema.....kaina bisa wuyana.......ayimin aikin gafara" Ta fadi tana hade hannayenta guri daya,hannayen da rawa kawai sukeyi.
Ido sosai mammina ta zuba mata,tana karance da yanayin razanin data shiga. Iya wannan kawai ya gamsar da ita,saita juya a nutse ta fice ba tare data sake cewa yalwa komai ba.
Wani irin razanannen numfashi ta saki bayan ta tabbatar da fitarta,ta koma ta zauna dab'as saman mazaunanta tana sauke wani irin numfashi dake gauraye da tsoro.
Ba zata sake gangancin aikata abinda ta aikata a yanxun ba.....ba zatayi gangancin da abinda ya samu LAURE ya sameta ba,tanason LAFIYARTA tana son RAYUWARTA.
*Tofa!!!!.....ME KARATU?.....shin kana hasashen abinda nake HASASHE KUWA?.....kana iya hangen abinda nake HANGE KUWA?.....TUNANINKA YANA KAIWA INDA NAWA YAKAI?*
*SU WAYE ZASU MUTU?*
*WA ZA'A RASA?*
*WAYE ZAI TSIRA DA RAYUWARSA?*
*WAZAI TSALLAKE?*
*WAYE KUMA ZAI AFKA?*
*Kasan irin GIRMA da adadin TUGGU da MAKIRCIN DAKE DAURE da wannan masarauta kuwa?*
*Akwai wata BABBAR ALAQA dake tsakanin masarautun biyu......ETHIOPIA da AGADEZ*
*Akwai wani LULLUBABBEN SIRRI......akwai wata irin BAHAGUWAR SOYAYYA ME WAHALAR GASKE cikin labarin LU'U LU'U*
*WACECE MAMMINA NE?*
*WACECE SAFEENA?*
*WACECE MORSA SAFIYYA?*
*_NEMANSA TAKE CIKIN DUHU SAIDAI BATASAN YANA DAB DA ITA BA_*
*_GANI YAKE BA HURUMINSA BACE......BA DON ITA YA SHIGO MASARAUTAR AGADEZ BA......saidai bai san cewa itace RUBUTACCIYAR QADDARAR DATA SANYASHI SHIGOWA QASAR BA_*
*_BATA DAUKESHI A BAKIN KOMAI BA CIKIN RASHIN SANI TAKE MASA KALLON QASQANTACCE......SAIDAI BATASAN TARIN NAGARTAR DAKE LULLUBE DA WANNAN LU'U LU'UN BA.......WANI SIRR DAKE ZAMEWA ALFARMAR RAYUWARTA A GABA_*
*_TA YAYA SIRRIKA MASU TSANANIN NAUYI ZASU FARA FASHEWA?_*
*_TA YAYA ZUKATAN ZASU KAMU DA SOYAYYAR DA ZATA KAISU GA SADAUKARWA?_*
*_WACCE ALAQA CE TSAKANIN WADANNAN MASARAUTUN BIYU DA DUKKA BASUSAN DA ITA BA?_*
*_idan har kace a nan zaka dakata.....to tabbas zan maka jaje.......wannan itace shimfidaddiya kuma miqaqqiyar hanyar da zata kaimu ga wani SHINGE DAKE DAUKE DA WATA IRIN RIKITACCIYAR SOYAYYA DA WARWARAR MAQULLAN ASIRAI DAKE BINNE A QARQASHIN QASA_*
*KU KASANCE DANI A KASHI NA BIYU NA LABARIN*
*ina fata baku manta da ALMAZ ba???*
*NA GODE*
08187255862
Hannun shehnaz da akhnan din aisa ta kama da sauran dakakkiyar zuciyarta,ta kuma jasu kai tsaye zuwa daya daga cikin bedrooms din akhnan din suka shige ciki sannan ta maida qofar ta kulle ta kuma murza key.
Tunda ta hango tahowar yalwa ta miqe tsam tana fuskantarta gami da jiran isowarta.
Zubewa zatayi kaman yadda ta saba,saidai ayau hannu mammina ta saka ta riqe kafadar yalwa.
"Me ya faru?" Ta mata tambayar da dukkan zaquwarta nason jin abinda ya biyo baya.
Tamkar a gaban mammina din akayi komai haka yalwa ta tsara mata,sannan tayi qasa da kanta a yau din tana jin nauyi tsaiwa gaban mammina a maimakon durqushewa a gabanta suyi magana yadda ta saba.
Kamar saukar ruwa da daukewarsa gurin ya dauki shuru,sai kuma sautin siririyar dariyar mammina ta ratsa gurin.
"Zatasha guba?" Ta sake tambayar yalwa. Kai ta jinjina mata.
"Qwarai haka tace". Kai ta kuma jinjinawa.
"A gaban aqalla jama'ar da sukakai adadi nawa?".
"Hadimanta da yawa.....ciki harda ranta ya dade aisa da shehnaz". Kai ta sake jinjinawa.
"Hakan yayi kowa ya shiga lissafi.....ZATA SHA GUBA" Ta fadi kai tsaye tana sakin kafadar yalwa gami da yin taku uku baya don bada tazara tsakaninta da yalwa din.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Kai yalwa ta daga da sauri tana duban mammina din,abinda ya jawo hankalinta ta sake maida dubanta ga yalwa,da wannan murmushin da a idanu da yawa yake bayyana zallar kirkinta da karamcinta......saidai a wasu lokutan kebantattu,a wasu idanun a wasu yanayiyyikan yake zama baqin murmushi,kuma mafi munin murmushi.
"Zata sha guba kamar yadda tace.....nayi laifi?,ita ta zabawa kanta ko?" Ta qarasa maganar tana duban yalwa. Da sauri yalwa ta girgiza kai
"Ba shakka......zabinta kenan.....furucinta na qarshe kuma kenan". Dage dukka kafadunta biyu tayi tana takawa hankalinta kwance.
" Tamim za'a nemo?" Yalwa ta fada tana duban bayan mammina. Maganan yalwar taja hankalinta,ta tsaya can na wasu mintuna kafin ta waiwayo tana dubanta.
"Yaushe kika fara min hasashe da kutsa kai cikin wasu abubuwan da ba'a gayyaceki ko an nemi tajin ta bakinki ba?" Da hanzari tayi qasa da kanta,jikinta ya soma rawa a hankali,tana kuma tuna LAURATU a shekarun baya da suka shude......a shekarun daba ITACE AKAN WANNAN MATSAYIN BA LAURATU CE
"Afuwa nake nema.....kaina bisa wuyana.......ayimin aikin gafara" Ta fadi tana hade hannayenta guri daya,hannayen da rawa kawai sukeyi.
Ido sosai mammina ta zuba mata,tana karance da yanayin razanin data shiga. Iya wannan kawai ya gamsar da ita,saita juya a nutse ta fice ba tare data sake cewa yalwa komai ba.
Wani irin razanannen numfashi ta saki bayan ta tabbatar da fitarta,ta koma ta zauna dab'as saman mazaunanta tana sauke wani irin numfashi dake gauraye da tsoro.
Ba zata sake gangancin aikata abinda ta aikata a yanxun ba.....ba zatayi gangancin da abinda ya samu LAURE ya sameta ba,tanason LAFIYARTA tana son RAYUWARTA.
*Tofa!!!!.....ME KARATU?.....shin kana hasashen abinda nake HASASHE KUWA?.....kana iya hangen abinda nake HANGE KUWA?.....TUNANINKA YANA KAIWA INDA NAWA YAKAI?*
*SU WAYE ZASU MUTU?*
*WA ZA'A RASA?*
*WAYE ZAI TSIRA DA RAYUWARSA?*
*WAZAI TSALLAKE?*
*WAYE KUMA ZAI AFKA?*
*Kasan irin GIRMA da adadin TUGGU da MAKIRCIN DAKE DAURE da wannan masarauta kuwa?*
*Akwai wata BABBAR ALAQA dake tsakanin masarautun biyu......ETHIOPIA da AGADEZ*
*Akwai wani LULLUBABBEN SIRRI......akwai wata irin BAHAGUWAR SOYAYYA ME WAHALAR GASKE cikin labarin LU'U LU'U*
*WACECE MAMMINA NE?*
*WACECE SAFEENA?*
*WACECE MORSA SAFIYYA?*
*_NEMANSA TAKE CIKIN DUHU SAIDAI BATASAN YANA DAB DA ITA BA_*
*_GANI YAKE BA HURUMINSA BACE......BA DON ITA YA SHIGO MASARAUTAR AGADEZ BA......saidai bai san cewa itace RUBUTACCIYAR QADDARAR DATA SANYASHI SHIGOWA QASAR BA_*
*_BATA DAUKESHI A BAKIN KOMAI BA CIKIN RASHIN SANI TAKE MASA KALLON QASQANTACCE......SAIDAI BATASAN TARIN NAGARTAR DAKE LULLUBE DA WANNAN LU'U LU'UN BA.......WANI SIRR DAKE ZAMEWA ALFARMAR RAYUWARTA A GABA_*
*_TA YAYA SIRRIKA MASU TSANANIN NAUYI ZASU FARA FASHEWA?_*
*_TA YAYA ZUKATAN ZASU KAMU DA SOYAYYAR DA ZATA KAISU GA SADAUKARWA?_*
*_WACCE ALAQA CE TSAKANIN WADANNAN MASARAUTUN BIYU DA DUKKA BASUSAN DA ITA BA?_*
*_idan har kace a nan zaka dakata.....to tabbas zan maka jaje.......wannan itace shimfidaddiya kuma miqaqqiyar hanyar da zata kaimu ga wani SHINGE DAKE DAUKE DA WATA IRIN RIKITACCIYAR SOYAYYA DA WARWARAR MAQULLAN ASIRAI DAKE BINNE A QARQASHIN QASA_*
*KU KASANCE DANI A KASHI NA BIYU NA LABARIN*
*ina fata baku manta da ALMAZ ba???*
*NA GODE*
08187255862