Sashe 77
Luu Luu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Matuqin baiyi koda horna ba gate din ya bude qaramar farfajiyar gidan ta bayyana,motar kuma ta kutsa kai zuwa cikin gidan,ta tsaya daga tsakiya,sannan mutum daya cikin mutane ukun dake tsaye a gurin suka qaraso da sassarfa da kuma tsananin girmamawa suka bude hannun da mammina ke zaune.
A qasaice ta sauko,wanda kafin qafafunta su qarasa direwa a qasa ta saki tamabayar.
"Ina tamim yake?".
"Bai qaraso ba" Suka amsa mata cikin matsanancin girmamawa suna sauke kawunansu a qasa.
"Muje na ganshi" Ta basu umarni na kai tsaye,wanda tana sauke maganar sukayi gaba da hanzari suna mata jagora.
Qawataccen parlor ne da aka zuba wadansu irin kayan alatu da sam bana qasar bane ba,wasu irin kayan alatu masu daukan hankali da nuna asalin tsadarsu da nauyin kudin da aka kashe domin siyansu.
Gaba daya daga cikinsu yayi zuwa daya daga cikin rufaffun qofofun da suke kulle,mammmina ta bishi a baya,har zuwa sanda ya murda dakin ya tura ya budewa mammina yana tsayawa daga gefe alamun bata daman shiga.
"Bacci yakeyi?" Ta jefa tambaya ga mutumin da yake tsaye din kansa a qasa. Tambayar tata da alama baiso ta fada a kansa ba,ko kuma baiso ta ruskeshi ba,don hannunsa ya aza saman kansa yana shafawa a nutse.
"A'ah......yadan sha......"
"Sake bashi kukayi?!" Ta furta a tsawace cikin wata irin fusatacciyar murya data haifar da shuru cikin falon. Ba wanda ya iya motsawa ko ya amsa a cikin su,sai sadda kawunansu da sukayi a qasa.
"Sau nawa zan gaya muku?.......sau nawa zan maimaita muku?" Ta sake musu tambayar da duk cikinsu ba wanda keda amsarta. Itama ta fahimci babu me iya bata amsa,don haka ta taka da hanzari tana cusa kai cikin dakin.
Yalwataccen daki ne da aka zuba masa set ma kayan gado masu tsananin tsada da daukan hankali,gami da dauke hankalinka daga ainihin duniyar da kake zuwa wani ni'imtaccen guri na daban.
Daga can saman yalwataccen gadon da aka qawatashi da wani tsadajjen bedsheets da comforter gami da pillows da aqalla sun kusa shida. Mutum ne kwance,wata irin birkitacciya kuma hargitstsiyar kwanciya da kana mata duba daya zakasan ba cikin nutsuwa akayita ba. Domin komai na gadon a yamutse yake,kaman yadda qafafunsa suke zube a qasa wadanda ke sanye da snickers din da ko samun daman ciresu ba'ayi ba.
Idanu ta zuba masa ranta tana jin yana wani irin baci. A duniya idan akwai wani abu qwaya daya daya kasance rashin sa'arta na duniya zata iya cewa almaz ne......yana daya daga cikin miyagun qaddarorinta.......yana daya daga cikin qaddarorin data gaza sarrafasu har sai da sukaso yin wasan kura da rayuwarta.
"Tasheshi" Ta fadi rai bace tana duban murdeden qaton da shine ya buda mata qofar dakin,bayan tayi dukkan qoqarinta don tayar da almaz din amma bai wani motsa ba.
Hannunsa yasa ya juya almaz yana kuma wancakalar dashi gefe,har sai da mammina taji abun har zuciyarta.
"Kada ka sake kwata irin wannan......kada ganinsa a haka ya sanya ka dauka wani wulaqantaccen kaya ne maras daraja......shi din daraja ce gareshi me yawan gaske". Qas yayi da kansa sannan ya furta.
" A gafarceni" Kana yadan ja baya daidai sanda almaz ke buda idanunsa da qyar wadanda sukayi masa nauyi.
A karo na biyu ya sake ganin inuwarta cikin idanunsa. A karo na biyu bayan hankalinsa ya fara kutsawa sassan jikinsa yana sake maimaita masa karatunta.....fuskarta......sunanta......alaqarsu......dangantarsu.......da kuma tarin wasu tsarika daya soma shiryawa kansa.
Tsarikan da ya jima yana gayawa kansa ba masu cika bane......tulin mafarkaine kawai masu qaryata zahiri.....kwatsam sai wani dan mitsitsin qyalli ya wulqa da sauri ya fara haska masa wata qofa.
"Ana" Ya fada da wani sauti me nauyi,wanda shi zai gaya maka zahirin nauyin dake cikin jikinsa dama hankalinsa. Idanunta ta dauke daga saman kyakkyawar fuskarsa......wannan fuskar dake tuna mata da tarin abubuwa masu yawan gaske da suka shude mata......wannan fuskar da kullum ta kalleta take tone wani birnannen abu da takejin ya kamata yayi nisan da ba zata iya koda tunawa dashi ba.......wannan fuskar dai da a haka take da wata irin kamala da nutsuwar da tasha banban da abinda ke shimfide a ruhin mamallakin fuskar.
"Ku sashi ya dawo daidai nan da minti sha biyar kacal ku fito ku sameni a parlor.......babu lokaci,kafin cikar wa'adin a nemomin tamim ya iskeni a nan yanzu" Ta furta gaba daya tana juya gami da ficewa a dakin.
Idanunsa ya maida ya lumshe kaman zai sake komawa baccin,saidai kuma wannan basamuden bai qyaleshi ba,ya kamashi yana tayar dashi. Bai musa ba ya miqe,don shima ya gaji da kwanciyar,yana buqatar wanda zai taimakeshi yace kwanciyar ta isa haka.
Zaune kawai tayi a falon,idanunta kafe guri daya,yayin da zuciyarta ke shirya mata yadda lamarin almaz zai iya zama barazana a gareta muddin komai bai hau kan saiti ba.
Mission da qudurinta akan almaz me girma ne.......wani abune da batasan yawan adadin shekaru darare da sa'o'in data laqume tana lissafin zuwansa ba.
Wani irin murmushi me bayyana tsananin qololuwar nishadin da zuciya ke ciki ne ya subuce mata,saita dauke hannuwanta tana goyesu a qirjinta tana kuma ci gaba da takawa d'ai d'ai.
Iya tuna yadda al'amarin zai kasance kadai walwala yake bata......wani irin sukuni yake saukar mata,tare da mantar da ita daya bangaren muhimmin aikin nata,duk kuwa da cewa wancan aikin zai iya zama mafi muhimmanci fiye da wannan.......saidai kuma ita din tana bawa MAIDA MARTANI da BADA SAKAMAKON ABINDA KA SHUKA da matuqar muhimmanci fiye da maida hankali ga abinda zai iya jawo mata asarar dukiya.
Daidai lokacin suke fitowa daga dakin. Almaz yana gaba yana biye da almaz din. A karo na biyu ya sake dubanta,yana tuna shekarun daya dauka bai sake sanyata a idanunsa ba,idan ba mantawa yayi ba shekaru shida kenan cif cif. Tana nan a yadda ya santa a baya,ba wani abu daya canzata,tsufa ko wani yanayi da zai nuna shekarun mutum suna tafiya sam babu ko daya a tare da ita. Idan har yana lissafi a daidai......ganinta yana samuwa a gareshi ne bayan kowacce shekara shida,a tsahon shekarun daya dauka a rayuwarsa,shekara ashirin da tara kaman yadda yaji ana fadi,sau uku tak! Ya taba ganinta,wannan shine cikon na hudun.
Gani ukunnan wani gani ne da yasha banban da dukkan wani gani da zaiwa kowanne dan adam,alaqa da kusanci da ake gaya masa wanda ke tsakaninsu har yanzu yana jinsu a wasu abubuwa da basu gama shiga damuwarsa ba......saidai a duk sanda zatazo ta tafi tana tsayewa a ransa da idanunsa da kuma tunaninsa,har xuwa sanda zata cike shekaru shidan ta sake dawowa. Dubanta yake sakeyi,yana mamakin abinda ya hanashi ganinta a shekaru shidan daya kwashe gidan prison yana zaune?......to amma kuma sai ya taqaita mamakinsa sanda ya tuna WAYE SANADIN FITARSA A YANZU DA YAKE TSAYE A NAN DIN?.
(08187255862 lu'u lu'u)
A nutse ta zauna tana dubansa gami da masa nuni da inda zai zauna din shima. Bai musa ba ya zauna da yanayin jikinsa da babu wani qarfi sam sam. Wani irin rashin qarfi da qwaya da kuma miyagun kayan shaye shaye suka dade da yin gaba da duk wani kuzari na jikinsa.
Idanu ta sake zuba masa,kaman yadda shima ita yake kalla,saidai kafin takai ga cewa komai tamim ya shigo bakinsa da sallamar neman izini.
Daga masarauta yake,kuma a wannan yammacin ya gama biyan salary din masu kula da dawakan sultane,wanda kusan duka ire iren wadannan abubuwan masu muhimmanci da suka shafi sultane a hannunsa suke. Da kayan ma'aikatan cikin gidan ya kamata ace sune a jikinsa,amma a yanzun sanye yake da wasu kaya. Wani irin yadi ne me kyau da tsada da aka yiwa dinkin 'yar shara,sai ya saka wata farar riga a ciki,sai dogon wandonta mahadin kayan,yayin da kansa ya kasance sanye da wata hula ire iren hulunan da akasan fulani na ta'ammali dasu.
Shigar shigen ta fulani ce,saidai sam shi din baya zubi ko kama dasu. Abune me wahalan gaske ka iya gare yare ko qabilan tamim,don yayi kamanni da wasu yaruka na qasar niger din,kaman yadda yayi zubi sosai da su.
Iya kallon mammina a gareshi kawai yana iya gaya masa matakin farinciki baqinciki ko tuhumarta a kanka. Don haka a yanzun yana shigowa ya ratsa a hankali ya yiwa kansa mazauni a inda yake ganin yafi dacewa dashi,wanda yana kammala zaman duk wani mahaluki dake numfashi a parlor din ya juya ya fice,mutum na qarshe kuma yaja musu qofar yana rufeta,sa'annan sukayi tsaye a nisan tazarar da aka lamunce musu suna kuma gadin koda tsuntsu daka iya nufar qofar da zummar shigewa.
"Anya zaka iya?.....anya ka shirya aikin nan almaz?" Mammina ta fadi fuskarta a hade tana dage dukka girarta guda biyun idanunta cikin na almaz din.
Duban seconds yayi mata,sannan ya janye idanunsa daga kanta yana sakin wani irin murmushi,hankalinsa kwance ya soma magana.
"Ana ko?.....Duk da iqirarin dangantakar da kike a tsakaninmu.....amma har yanxu bakisan waye almaz ba......bana tunkarar komai saina shirya masa.....bana kuma tunkarar komai saina tabbatar zan iya".
"Banga alama ba......" Ta fada tana katse hanzarinsa. Idanu ya zuba mata alamun neman qarin jawabi da idanunsa da suke a shanye koda yaushe saboda yawan buguwa.
"Kasan a yau ya kamata nazo na sameka a shirye kana karbar horo tsarikan dana baka?!" Tayi maganan a dan tsawace rai a bace tana dubansa. Still dai baice komai ba,don a rayuwarsa ya tsani tsawa ko ka gaya masa magana kai tsaye haka kome zaka bashi. Fahimtar hakan wataqila ya sanya mammina sassauta muryarta tana dubansa.
"Almaz......na baka dukkan wata masaniya,na kuma baka dukkan wani kundi......na baka shafukan rayuwarta kaf gaba daya.......tun daga quruciyarta har kawo yau.......me takeso?,me ta tsana?,me yafi burgeta?......shin me ya rage maka almaz?.....me ya rage banda nazo na sameka ka fara qoqarin zama irin wannan mutumin?.......ko kasan daga yau ya kamata komai ya fara motsawa?,daga yau ya kamata ace komai ya fara tafiya?". Shanyayyun idanunsa ya janye daga kanta,tsaki yakeso yaja saboda hayaniyar da take masa amma ya taushi kansa.
"Wannan yarinyar.......tsaurinta da tsarinta yayi yawa,banga kuma ta inda zan farauto soyayyarta harta aure ni ba".
A qasaice ta sauko,wanda kafin qafafunta su qarasa direwa a qasa ta saki tamabayar.
"Ina tamim yake?".
"Bai qaraso ba" Suka amsa mata cikin matsanancin girmamawa suna sauke kawunansu a qasa.
"Muje na ganshi" Ta basu umarni na kai tsaye,wanda tana sauke maganar sukayi gaba da hanzari suna mata jagora.
Qawataccen parlor ne da aka zuba wadansu irin kayan alatu da sam bana qasar bane ba,wasu irin kayan alatu masu daukan hankali da nuna asalin tsadarsu da nauyin kudin da aka kashe domin siyansu.
Gaba daya daga cikinsu yayi zuwa daya daga cikin rufaffun qofofun da suke kulle,mammmina ta bishi a baya,har zuwa sanda ya murda dakin ya tura ya budewa mammina yana tsayawa daga gefe alamun bata daman shiga.
"Bacci yakeyi?" Ta jefa tambaya ga mutumin da yake tsaye din kansa a qasa. Tambayar tata da alama baiso ta fada a kansa ba,ko kuma baiso ta ruskeshi ba,don hannunsa ya aza saman kansa yana shafawa a nutse.
"A'ah......yadan sha......"
"Sake bashi kukayi?!" Ta furta a tsawace cikin wata irin fusatacciyar murya data haifar da shuru cikin falon. Ba wanda ya iya motsawa ko ya amsa a cikin su,sai sadda kawunansu da sukayi a qasa.
"Sau nawa zan gaya muku?.......sau nawa zan maimaita muku?" Ta sake musu tambayar da duk cikinsu ba wanda keda amsarta. Itama ta fahimci babu me iya bata amsa,don haka ta taka da hanzari tana cusa kai cikin dakin.
Yalwataccen daki ne da aka zuba masa set ma kayan gado masu tsananin tsada da daukan hankali,gami da dauke hankalinka daga ainihin duniyar da kake zuwa wani ni'imtaccen guri na daban.
Daga can saman yalwataccen gadon da aka qawatashi da wani tsadajjen bedsheets da comforter gami da pillows da aqalla sun kusa shida. Mutum ne kwance,wata irin birkitacciya kuma hargitstsiyar kwanciya da kana mata duba daya zakasan ba cikin nutsuwa akayita ba. Domin komai na gadon a yamutse yake,kaman yadda qafafunsa suke zube a qasa wadanda ke sanye da snickers din da ko samun daman ciresu ba'ayi ba.
Idanu ta zuba masa ranta tana jin yana wani irin baci. A duniya idan akwai wani abu qwaya daya daya kasance rashin sa'arta na duniya zata iya cewa almaz ne......yana daya daga cikin miyagun qaddarorinta.......yana daya daga cikin qaddarorin data gaza sarrafasu har sai da sukaso yin wasan kura da rayuwarta.
"Tasheshi" Ta fadi rai bace tana duban murdeden qaton da shine ya buda mata qofar dakin,bayan tayi dukkan qoqarinta don tayar da almaz din amma bai wani motsa ba.
Hannunsa yasa ya juya almaz yana kuma wancakalar dashi gefe,har sai da mammina taji abun har zuciyarta.
"Kada ka sake kwata irin wannan......kada ganinsa a haka ya sanya ka dauka wani wulaqantaccen kaya ne maras daraja......shi din daraja ce gareshi me yawan gaske". Qas yayi da kansa sannan ya furta.
" A gafarceni" Kana yadan ja baya daidai sanda almaz ke buda idanunsa da qyar wadanda sukayi masa nauyi.
A karo na biyu ya sake ganin inuwarta cikin idanunsa. A karo na biyu bayan hankalinsa ya fara kutsawa sassan jikinsa yana sake maimaita masa karatunta.....fuskarta......sunanta......alaqarsu......dangantarsu.......da kuma tarin wasu tsarika daya soma shiryawa kansa.
Tsarikan da ya jima yana gayawa kansa ba masu cika bane......tulin mafarkaine kawai masu qaryata zahiri.....kwatsam sai wani dan mitsitsin qyalli ya wulqa da sauri ya fara haska masa wata qofa.
"Ana" Ya fada da wani sauti me nauyi,wanda shi zai gaya maka zahirin nauyin dake cikin jikinsa dama hankalinsa. Idanunta ta dauke daga saman kyakkyawar fuskarsa......wannan fuskar dake tuna mata da tarin abubuwa masu yawan gaske da suka shude mata......wannan fuskar da kullum ta kalleta take tone wani birnannen abu da takejin ya kamata yayi nisan da ba zata iya koda tunawa dashi ba.......wannan fuskar dai da a haka take da wata irin kamala da nutsuwar da tasha banban da abinda ke shimfide a ruhin mamallakin fuskar.
"Ku sashi ya dawo daidai nan da minti sha biyar kacal ku fito ku sameni a parlor.......babu lokaci,kafin cikar wa'adin a nemomin tamim ya iskeni a nan yanzu" Ta furta gaba daya tana juya gami da ficewa a dakin.
Idanunsa ya maida ya lumshe kaman zai sake komawa baccin,saidai kuma wannan basamuden bai qyaleshi ba,ya kamashi yana tayar dashi. Bai musa ba ya miqe,don shima ya gaji da kwanciyar,yana buqatar wanda zai taimakeshi yace kwanciyar ta isa haka.
Zaune kawai tayi a falon,idanunta kafe guri daya,yayin da zuciyarta ke shirya mata yadda lamarin almaz zai iya zama barazana a gareta muddin komai bai hau kan saiti ba.
Mission da qudurinta akan almaz me girma ne.......wani abune da batasan yawan adadin shekaru darare da sa'o'in data laqume tana lissafin zuwansa ba.
Wani irin murmushi me bayyana tsananin qololuwar nishadin da zuciya ke ciki ne ya subuce mata,saita dauke hannuwanta tana goyesu a qirjinta tana kuma ci gaba da takawa d'ai d'ai.
Iya tuna yadda al'amarin zai kasance kadai walwala yake bata......wani irin sukuni yake saukar mata,tare da mantar da ita daya bangaren muhimmin aikin nata,duk kuwa da cewa wancan aikin zai iya zama mafi muhimmanci fiye da wannan.......saidai kuma ita din tana bawa MAIDA MARTANI da BADA SAKAMAKON ABINDA KA SHUKA da matuqar muhimmanci fiye da maida hankali ga abinda zai iya jawo mata asarar dukiya.
Daidai lokacin suke fitowa daga dakin. Almaz yana gaba yana biye da almaz din. A karo na biyu ya sake dubanta,yana tuna shekarun daya dauka bai sake sanyata a idanunsa ba,idan ba mantawa yayi ba shekaru shida kenan cif cif. Tana nan a yadda ya santa a baya,ba wani abu daya canzata,tsufa ko wani yanayi da zai nuna shekarun mutum suna tafiya sam babu ko daya a tare da ita. Idan har yana lissafi a daidai......ganinta yana samuwa a gareshi ne bayan kowacce shekara shida,a tsahon shekarun daya dauka a rayuwarsa,shekara ashirin da tara kaman yadda yaji ana fadi,sau uku tak! Ya taba ganinta,wannan shine cikon na hudun.
Gani ukunnan wani gani ne da yasha banban da dukkan wani gani da zaiwa kowanne dan adam,alaqa da kusanci da ake gaya masa wanda ke tsakaninsu har yanzu yana jinsu a wasu abubuwa da basu gama shiga damuwarsa ba......saidai a duk sanda zatazo ta tafi tana tsayewa a ransa da idanunsa da kuma tunaninsa,har xuwa sanda zata cike shekaru shidan ta sake dawowa. Dubanta yake sakeyi,yana mamakin abinda ya hanashi ganinta a shekaru shidan daya kwashe gidan prison yana zaune?......to amma kuma sai ya taqaita mamakinsa sanda ya tuna WAYE SANADIN FITARSA A YANZU DA YAKE TSAYE A NAN DIN?.
(08187255862 lu'u lu'u)
A nutse ta zauna tana dubansa gami da masa nuni da inda zai zauna din shima. Bai musa ba ya zauna da yanayin jikinsa da babu wani qarfi sam sam. Wani irin rashin qarfi da qwaya da kuma miyagun kayan shaye shaye suka dade da yin gaba da duk wani kuzari na jikinsa.
Idanu ta sake zuba masa,kaman yadda shima ita yake kalla,saidai kafin takai ga cewa komai tamim ya shigo bakinsa da sallamar neman izini.
Daga masarauta yake,kuma a wannan yammacin ya gama biyan salary din masu kula da dawakan sultane,wanda kusan duka ire iren wadannan abubuwan masu muhimmanci da suka shafi sultane a hannunsa suke. Da kayan ma'aikatan cikin gidan ya kamata ace sune a jikinsa,amma a yanzun sanye yake da wasu kaya. Wani irin yadi ne me kyau da tsada da aka yiwa dinkin 'yar shara,sai ya saka wata farar riga a ciki,sai dogon wandonta mahadin kayan,yayin da kansa ya kasance sanye da wata hula ire iren hulunan da akasan fulani na ta'ammali dasu.
Shigar shigen ta fulani ce,saidai sam shi din baya zubi ko kama dasu. Abune me wahalan gaske ka iya gare yare ko qabilan tamim,don yayi kamanni da wasu yaruka na qasar niger din,kaman yadda yayi zubi sosai da su.
Iya kallon mammina a gareshi kawai yana iya gaya masa matakin farinciki baqinciki ko tuhumarta a kanka. Don haka a yanzun yana shigowa ya ratsa a hankali ya yiwa kansa mazauni a inda yake ganin yafi dacewa dashi,wanda yana kammala zaman duk wani mahaluki dake numfashi a parlor din ya juya ya fice,mutum na qarshe kuma yaja musu qofar yana rufeta,sa'annan sukayi tsaye a nisan tazarar da aka lamunce musu suna kuma gadin koda tsuntsu daka iya nufar qofar da zummar shigewa.
"Anya zaka iya?.....anya ka shirya aikin nan almaz?" Mammina ta fadi fuskarta a hade tana dage dukka girarta guda biyun idanunta cikin na almaz din.
Duban seconds yayi mata,sannan ya janye idanunsa daga kanta yana sakin wani irin murmushi,hankalinsa kwance ya soma magana.
"Ana ko?.....Duk da iqirarin dangantakar da kike a tsakaninmu.....amma har yanxu bakisan waye almaz ba......bana tunkarar komai saina shirya masa.....bana kuma tunkarar komai saina tabbatar zan iya".
"Banga alama ba......" Ta fada tana katse hanzarinsa. Idanu ya zuba mata alamun neman qarin jawabi da idanunsa da suke a shanye koda yaushe saboda yawan buguwa.
"Kasan a yau ya kamata nazo na sameka a shirye kana karbar horo tsarikan dana baka?!" Tayi maganan a dan tsawace rai a bace tana dubansa. Still dai baice komai ba,don a rayuwarsa ya tsani tsawa ko ka gaya masa magana kai tsaye haka kome zaka bashi. Fahimtar hakan wataqila ya sanya mammina sassauta muryarta tana dubansa.
"Almaz......na baka dukkan wata masaniya,na kuma baka dukkan wani kundi......na baka shafukan rayuwarta kaf gaba daya.......tun daga quruciyarta har kawo yau.......me takeso?,me ta tsana?,me yafi burgeta?......shin me ya rage maka almaz?.....me ya rage banda nazo na sameka ka fara qoqarin zama irin wannan mutumin?.......ko kasan daga yau ya kamata komai ya fara motsawa?,daga yau ya kamata ace komai ya fara tafiya?". Shanyayyun idanunsa ya janye daga kanta,tsaki yakeso yaja saboda hayaniyar da take masa amma ya taushi kansa.
"Wannan yarinyar.......tsaurinta da tsarinta yayi yawa,banga kuma ta inda zan farauto soyayyarta harta aure ni ba".