Sashe 20
Luu Luu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
" Ma sha Allah.....Allah ya kula mana da rayuwar su " Ya fada yana jin dadin hakan har cikin ransa. Duk da cewa falaak ce kawai jininsa.......amma yana jin hairaan a matsayin diyarsa halak malak........don daga jikin safiyya ta fito.....'ya'yan safiyya kuwa jinin safeena yana jin nasa ne. Idan ahalin suka hadu......yana manta cewa bashi da wani magaji tsayayye guda daya......yana manta cewa a yanzun ida ya fadi ya mutu sarautar qasar AGADEZ tana iya barin cikin gidansu ta fada zuwa hannun yaran gidan baffanninsa.....yasan komai na Allah ne.....muddin kuma akwai yiwuwar zaman sarautar hannunsu ba wanda ya isa ya karba,ballantana ma shi bai dauki gadon da wani zafi ba.... Don ko a baya zamanin kakanninsu ta taba barin hannun kakansa sai daga baya ta dawo musu.
"Ranka ya dade.....bawai zakayi sabbin amare ba fa kuma a juya mana baya" Ta fada cikin sigar tsokanar data sakashi murmusawa har kyakkyawar wushiryarsa ta fito.
★★★★
Qarfe shida da rabi na yammacin ranar motar qirar Lamborghini ta ajiyeta a sashen ajiyar motoci na musamman dake gidan.
Bude murfin motar akayi,daga gaba wani kakkauran matashi dake da komai baqi ya fito yana bude seat din baya.
Iska ta furzar daga bakinta tana jefo qafafunta waje.......gaba daya jikinta yayi laushi saboda dadewar da tayi a zaune a office.
Yau din harta gota lokacin tashinta saboda alwashin da taci tabbas sati me zuwa sabbin design na kamfaninsu zai fara zaga kasuwannin duniya.
Duk da a jigace take,amma hakan bai hana bayyanuwar kwantaccen kyan da take dashi ba. Jikinta yana busa lallausan qamshin nan nata a kowanne motsi da zatayi,iska kuma na dada zaqulo qamshin nata sanda take kada tattausar lafayar data nade jikinta da ita,lafayar data yafata iyakar kafada,kanta zaune das da daurin dankwalin wani veil baqi me taushi daya zauna mata kamar hula.
"Birra" Ta kira sunanta a gajiye..... Gajiyar data sake zame mata ado,don sai suka qara adadin yauqin halitta da yangar data zame mata ta asalin halittarta. Sign kawai tayi mata na ta karbi tarkacen office dinta dake hannun saaleem ta fara takawa zuwa gaba tana furta.
"Wash Allah na". Gami da yarfar da hannu.
Taku goma kacal tayi idanunta suka sauka kan Shehinaz ita da baqonta dake zaune suna facing juna..... Da alama magana ne sukayi me matuqar muhimmancin da har basa sanin meke faruwa daura dasu.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*MY NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
PAGE 14
Idanu akhnan ta fiddo tana kuma rage dan saurin data aro daaa don isa ciki ta watsar da gajiyarta. Mamaki da tsoro suna cikata tana kuma sake ware idanunta akan baqon Shehinaz din,wanda bata sani ba,kaifin idanunta ne suka sanya yaji kallon a jikinsa ya maido dubansa sashen da take?,abinda ya dauko hankalin Shehinaz kenan itama ta maido dubanta inda taga yana kalla.
Hannu ta dagawa akhnan cikin sakin murmushi,tashin farko taji ba zata iya maida mata koda da daga hannun ba bare murmushi ballantana akai ga takawarta zuwa inda suke,sai kawai ta dauke kai ta maida hankalinta zuwa hanyar da zata sadata da ainihin gidan zuciyarta na wani irin bugawa,bugawar da batasan meye dalilinta ba.....bacin rai ne?,ko kuma mamaki ne?,ba zata iya tantancewa ba.
Da kallo dukkansu sukabi bayanta har ta bacewa ganinsu,sai Shehinaz ta dauke dubanta ta mayar kan Jamaal tana maye mamakin dake saman fuskarta da murmushi.
Duk yadda taso wucewa daki kamar yadda ta tsara kafin ta iso gidan amma sai ta yada zango a parlor,abinda kusan ya bawa duka hadimanta mamaki. Saboda wani baqon abune da bata saba yinsa ba. Lokuta da dama ma idan ta dawo ta wuce ciki ba lallai bane ka sake ganinta ba sai washegari.
Hannatou keda hidima da ita tana kai kawon bata abunsha da tasan takan sha idan ta dawo gidan. Buhaina na qoqarin tattare kayan office din data cire a nan,takalminta laffayarta dan kwalinta da jewelry dinta duka data zare. Ta saba komai tana ajjiyeshi ne a inda yayi mata,akwai masu kula da komai din su tattalashi. Xasu kwashe jewelry dinta a gogeshi kowanne a maidashi cikin box dinsa. A sake goge takalmanta ayi musu feshi a maidasu cikin qawatacciyar ma'ajiyar takalman dake cikin dressing room dinta. Wannan ya sanya komai nata idan ka kalla zakace ba'a sakashi ko ba'a taba sakashi ba,don hatta da qasan takalmanta babu wani datti da zai alamta maka haka. Tana da mugun qyanqyami.......sai Allah ya hadata da hadimai na amana dake iyayi mata komai kamar ko fiye ma da yadda takeso. Ganin hankalinta ba'a gurin yake ba sai Hannatou ta janye hirar da take dan sako mata.
Agogo ta kalla dake bango don tuni ta cire na hannunta an wuce mata dashi. Ta soma gajiya da zaman jiran shigowar Shehinaz,kuma alamu sun nuna bata da niyya ko yunqurin shigowa a yanzu,dole ta miqe don wucewa ciki ranta na sake sosuwa. Taso qwarai Shehinaz ta shigo da zafi zafinta kafin ta sauya ra'ayin yi mata magana.
Dab da zata wuce hanyar da zata sadaka da dakunan baccinsu taji shigowar aisa. Ta biya ta wani guri ne bayan sun tashi daga office,don haka yau tafiyar tasu daban daban take.
"Kinga Shehinaz?" Ta tambayeta da muryarta a sanyaye. Bude idanu aisa tayi tana kallonta.
"Eh na ganta ita da jamaal.......so masha Allah wallahi......Il a une maturité étonnante,II a une apparence trés religieuse(akwai alamun kamala sosai tare dashi,da alamun addini sosai tare dashi)" Ta fada kanta tsaye fuskarta na gasgata abinda ta fada har cikin zuciyarta yake fitowa.
Baki da idanu kawai akhnan ta saki tana duban aisa,maqogoranta taji kamar ya bushe duk da bata jima da shan ruwa ba.......ta tattaro ragowar yawun bakinta ta hadiya sannan tace.
"Aisa.....Êtes-vouse conscient de ce que vous dites(kina sane da abinda kike fada?)......kina tunanin mace irin Shehinaz ta dace da kidahuman mazan da babu wayewa a tare dasu?"
"Qidahumai?" Aisa na maimaita kalmar cike da mamaki.
"Biftu?.....wai me kika dauki ma'anar KIDAHUMIN NAMIJI?.....Namijin da baiyi karatun boko ba?......namijin da ilimin arabiyya kawai yake dashi?,shine kidahumi?.....kinsan kura kuren dake cikin wannan tunanika naki guda biyu?".
"Ehnnnn........ki gayamin,Vouse lui lavez le cerveau(ke kike wanke mata tunani).......wannan mummunar hanya ce......hanya ce mara bullewa.......a ajin da darajar rayuwarta?........namiji me wannan suffar II n'était pas qualifié(bai cancanci) ya zama mijinta ba.......ba wani guri da mataki na rayuwa da zai iya tsaya miki........ba wani abu me muhimmanci da zai iya tunkararsa saidai ya tsaya a bayanki ki zame masa garkuwa.......banason irin wannan namijin......koda yaushe nafison NAMIJI ZAKI NAMIJI GARKUWA.......wayewarsa da iliminsa basu isa su tsaya a kowanne mataki da me ilimin boko zai tsaya ba.......mu gaya ma kanmu gaskiya kuma itama ki gaya mata gaskiya...." Ta qarashe maganan cikin fada da bacin ran da aisa ta jima bata ga ta yishi ba,sai kuma tayi gaba fuuuu da dan guntun saurinta ta wuce dakinta har aisa na jiyo qarar rufe qofar duk da qofofine da sam saika qaraci zamanka dasu bakaji qarar koda motsinsu ba.
"Mon dieu du ciel(oh Allah na)" Aisa ta fada tana komawa ta zauna saman kujerar dake daura da ita. Ba zafi abun yayi mata ba......mamakin dauka zafin da akhnan din tayi ne yake daure mata kai. Tabbas a dukka su ukun suna iya shawara akan rayuwar daya su tsaida matsaya ko si zartar. Tun asali tasan burace buracen akhnan akan iri mijin da ya cancanci ta aureshi masu yawan gaske ne.......tun asali tasan akhnan din burinta babba a wajen namiji ya zama me cikakkiyar wayewa.......me zuzzurfan matakin karatu a duniya gaba daya.......namiji me zarra sosai......tsayayye jarumi maras tsoro ko shakka......bata da burin namiji me ilimin addini muddin yana da ilimin da zai kiyaye ibadarsa daidai........abu na qarshe data tsana tafi kuma raina ajawalinsa shine.......namijin da zaiyu karatun arabiyya. Takan fadi wani lokaci idan magana ta tashi.
"Banga hikima ba......banga basira da wayo a karanta arabic ba.......a matsayinka na namiji da aka sani da zallar gwagwarmaya.......ina wani gwagwarmaya a karatun da iyakacinsa ka zama malami me koyarwa ko karantarwa?.
A sannan zata iya cewa bata fiya ganin aibu ko rashin dabara a maganganun akhnan nan ba.......amma sannu a hankali da girma ya ratsasu.......rayuwa ta rarrabasu zuwa wasu qasashe......cikin jinsina da yare sai dukka wannan tunanin yabar jikinsu.....Musamman su din da karatu ya cilla aisa Egypt yakai Shehinaz madeena.........akhnan tata qaddarar ta kaita French. Kusan kowanne ya dawo ne da sabon tunani......sabuwar rayuwa da sabbin mutane cikin rayuwar tashi.
Tsaye kawai tayi gaban babban madubin dake toilet dinta tana duban kanta da kanta. Iska take zuqa tana fesarwa tanason saisaita yanayinta,tsahon wasu mintuna zuciyarta ta fara magana da ita.
"Ki nutsu akhnan......ki nutsu.......baki isa ki sauya qaddarar kowa ba.......baki isa ki tsarawa su aisa qaddararsu ba.......taki qaddarar ce kadai a hannunki......kina iya lanqwasata ta sigar da kikaga dama(a nata tunanin kenan)......karki bata wannan relation
Amitié din(dangantaka da qawance),damuwa da damuwar wani ba dabi'arki bace.....ki concentration akan abinda yake gabanki".
"Mais(amma) Shehinaz ce fa?" Ta fadi a fili da siririyar muryarta tana jin abun yana tsaye mata a wuya,tasan ta damu ne kawai saboda Shehinaz dince.......su din kamar wani sashe ne na tata rayuwar.
"Idan Shehinaz ce zuciya da tunaninku ba daya bane......dole a samu banbanci cikin rayuwarku" Wani sashe na zuciyarta ya sake tunasar da ita.
Dole ta tattare komai tayi wani watsin tsiya dashi,duk da tana ji abun yana ci mata zuciya,tayi wanka ta fito har sannan bata sake jin motsin kowa ba,sai ta zauna a nutse ta shirya cikin wani budadden wando da blouse data lafe ta fidda shape din jikinta.
"Ranka ya dade.....bawai zakayi sabbin amare ba fa kuma a juya mana baya" Ta fada cikin sigar tsokanar data sakashi murmusawa har kyakkyawar wushiryarsa ta fito.
★★★★
Qarfe shida da rabi na yammacin ranar motar qirar Lamborghini ta ajiyeta a sashen ajiyar motoci na musamman dake gidan.
Bude murfin motar akayi,daga gaba wani kakkauran matashi dake da komai baqi ya fito yana bude seat din baya.
Iska ta furzar daga bakinta tana jefo qafafunta waje.......gaba daya jikinta yayi laushi saboda dadewar da tayi a zaune a office.
Yau din harta gota lokacin tashinta saboda alwashin da taci tabbas sati me zuwa sabbin design na kamfaninsu zai fara zaga kasuwannin duniya.
Duk da a jigace take,amma hakan bai hana bayyanuwar kwantaccen kyan da take dashi ba. Jikinta yana busa lallausan qamshin nan nata a kowanne motsi da zatayi,iska kuma na dada zaqulo qamshin nata sanda take kada tattausar lafayar data nade jikinta da ita,lafayar data yafata iyakar kafada,kanta zaune das da daurin dankwalin wani veil baqi me taushi daya zauna mata kamar hula.
"Birra" Ta kira sunanta a gajiye..... Gajiyar data sake zame mata ado,don sai suka qara adadin yauqin halitta da yangar data zame mata ta asalin halittarta. Sign kawai tayi mata na ta karbi tarkacen office dinta dake hannun saaleem ta fara takawa zuwa gaba tana furta.
"Wash Allah na". Gami da yarfar da hannu.
Taku goma kacal tayi idanunta suka sauka kan Shehinaz ita da baqonta dake zaune suna facing juna..... Da alama magana ne sukayi me matuqar muhimmancin da har basa sanin meke faruwa daura dasu.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*MY NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
PAGE 14
Idanu akhnan ta fiddo tana kuma rage dan saurin data aro daaa don isa ciki ta watsar da gajiyarta. Mamaki da tsoro suna cikata tana kuma sake ware idanunta akan baqon Shehinaz din,wanda bata sani ba,kaifin idanunta ne suka sanya yaji kallon a jikinsa ya maido dubansa sashen da take?,abinda ya dauko hankalin Shehinaz kenan itama ta maido dubanta inda taga yana kalla.
Hannu ta dagawa akhnan cikin sakin murmushi,tashin farko taji ba zata iya maida mata koda da daga hannun ba bare murmushi ballantana akai ga takawarta zuwa inda suke,sai kawai ta dauke kai ta maida hankalinta zuwa hanyar da zata sadata da ainihin gidan zuciyarta na wani irin bugawa,bugawar da batasan meye dalilinta ba.....bacin rai ne?,ko kuma mamaki ne?,ba zata iya tantancewa ba.
Da kallo dukkansu sukabi bayanta har ta bacewa ganinsu,sai Shehinaz ta dauke dubanta ta mayar kan Jamaal tana maye mamakin dake saman fuskarta da murmushi.
Duk yadda taso wucewa daki kamar yadda ta tsara kafin ta iso gidan amma sai ta yada zango a parlor,abinda kusan ya bawa duka hadimanta mamaki. Saboda wani baqon abune da bata saba yinsa ba. Lokuta da dama ma idan ta dawo ta wuce ciki ba lallai bane ka sake ganinta ba sai washegari.
Hannatou keda hidima da ita tana kai kawon bata abunsha da tasan takan sha idan ta dawo gidan. Buhaina na qoqarin tattare kayan office din data cire a nan,takalminta laffayarta dan kwalinta da jewelry dinta duka data zare. Ta saba komai tana ajjiyeshi ne a inda yayi mata,akwai masu kula da komai din su tattalashi. Xasu kwashe jewelry dinta a gogeshi kowanne a maidashi cikin box dinsa. A sake goge takalmanta ayi musu feshi a maidasu cikin qawatacciyar ma'ajiyar takalman dake cikin dressing room dinta. Wannan ya sanya komai nata idan ka kalla zakace ba'a sakashi ko ba'a taba sakashi ba,don hatta da qasan takalmanta babu wani datti da zai alamta maka haka. Tana da mugun qyanqyami.......sai Allah ya hadata da hadimai na amana dake iyayi mata komai kamar ko fiye ma da yadda takeso. Ganin hankalinta ba'a gurin yake ba sai Hannatou ta janye hirar da take dan sako mata.
Agogo ta kalla dake bango don tuni ta cire na hannunta an wuce mata dashi. Ta soma gajiya da zaman jiran shigowar Shehinaz,kuma alamu sun nuna bata da niyya ko yunqurin shigowa a yanzu,dole ta miqe don wucewa ciki ranta na sake sosuwa. Taso qwarai Shehinaz ta shigo da zafi zafinta kafin ta sauya ra'ayin yi mata magana.
Dab da zata wuce hanyar da zata sadaka da dakunan baccinsu taji shigowar aisa. Ta biya ta wani guri ne bayan sun tashi daga office,don haka yau tafiyar tasu daban daban take.
"Kinga Shehinaz?" Ta tambayeta da muryarta a sanyaye. Bude idanu aisa tayi tana kallonta.
"Eh na ganta ita da jamaal.......so masha Allah wallahi......Il a une maturité étonnante,II a une apparence trés religieuse(akwai alamun kamala sosai tare dashi,da alamun addini sosai tare dashi)" Ta fada kanta tsaye fuskarta na gasgata abinda ta fada har cikin zuciyarta yake fitowa.
Baki da idanu kawai akhnan ta saki tana duban aisa,maqogoranta taji kamar ya bushe duk da bata jima da shan ruwa ba.......ta tattaro ragowar yawun bakinta ta hadiya sannan tace.
"Aisa.....Êtes-vouse conscient de ce que vous dites(kina sane da abinda kike fada?)......kina tunanin mace irin Shehinaz ta dace da kidahuman mazan da babu wayewa a tare dasu?"
"Qidahumai?" Aisa na maimaita kalmar cike da mamaki.
"Biftu?.....wai me kika dauki ma'anar KIDAHUMIN NAMIJI?.....Namijin da baiyi karatun boko ba?......namijin da ilimin arabiyya kawai yake dashi?,shine kidahumi?.....kinsan kura kuren dake cikin wannan tunanika naki guda biyu?".
"Ehnnnn........ki gayamin,Vouse lui lavez le cerveau(ke kike wanke mata tunani).......wannan mummunar hanya ce......hanya ce mara bullewa.......a ajin da darajar rayuwarta?........namiji me wannan suffar II n'était pas qualifié(bai cancanci) ya zama mijinta ba.......ba wani guri da mataki na rayuwa da zai iya tsaya miki........ba wani abu me muhimmanci da zai iya tunkararsa saidai ya tsaya a bayanki ki zame masa garkuwa.......banason irin wannan namijin......koda yaushe nafison NAMIJI ZAKI NAMIJI GARKUWA.......wayewarsa da iliminsa basu isa su tsaya a kowanne mataki da me ilimin boko zai tsaya ba.......mu gaya ma kanmu gaskiya kuma itama ki gaya mata gaskiya...." Ta qarashe maganan cikin fada da bacin ran da aisa ta jima bata ga ta yishi ba,sai kuma tayi gaba fuuuu da dan guntun saurinta ta wuce dakinta har aisa na jiyo qarar rufe qofar duk da qofofine da sam saika qaraci zamanka dasu bakaji qarar koda motsinsu ba.
"Mon dieu du ciel(oh Allah na)" Aisa ta fada tana komawa ta zauna saman kujerar dake daura da ita. Ba zafi abun yayi mata ba......mamakin dauka zafin da akhnan din tayi ne yake daure mata kai. Tabbas a dukka su ukun suna iya shawara akan rayuwar daya su tsaida matsaya ko si zartar. Tun asali tasan burace buracen akhnan akan iri mijin da ya cancanci ta aureshi masu yawan gaske ne.......tun asali tasan akhnan din burinta babba a wajen namiji ya zama me cikakkiyar wayewa.......me zuzzurfan matakin karatu a duniya gaba daya.......namiji me zarra sosai......tsayayye jarumi maras tsoro ko shakka......bata da burin namiji me ilimin addini muddin yana da ilimin da zai kiyaye ibadarsa daidai........abu na qarshe data tsana tafi kuma raina ajawalinsa shine.......namijin da zaiyu karatun arabiyya. Takan fadi wani lokaci idan magana ta tashi.
"Banga hikima ba......banga basira da wayo a karanta arabic ba.......a matsayinka na namiji da aka sani da zallar gwagwarmaya.......ina wani gwagwarmaya a karatun da iyakacinsa ka zama malami me koyarwa ko karantarwa?.
A sannan zata iya cewa bata fiya ganin aibu ko rashin dabara a maganganun akhnan nan ba.......amma sannu a hankali da girma ya ratsasu.......rayuwa ta rarrabasu zuwa wasu qasashe......cikin jinsina da yare sai dukka wannan tunanin yabar jikinsu.....Musamman su din da karatu ya cilla aisa Egypt yakai Shehinaz madeena.........akhnan tata qaddarar ta kaita French. Kusan kowanne ya dawo ne da sabon tunani......sabuwar rayuwa da sabbin mutane cikin rayuwar tashi.
Tsaye kawai tayi gaban babban madubin dake toilet dinta tana duban kanta da kanta. Iska take zuqa tana fesarwa tanason saisaita yanayinta,tsahon wasu mintuna zuciyarta ta fara magana da ita.
"Ki nutsu akhnan......ki nutsu.......baki isa ki sauya qaddarar kowa ba.......baki isa ki tsarawa su aisa qaddararsu ba.......taki qaddarar ce kadai a hannunki......kina iya lanqwasata ta sigar da kikaga dama(a nata tunanin kenan)......karki bata wannan relation
Amitié din(dangantaka da qawance),damuwa da damuwar wani ba dabi'arki bace.....ki concentration akan abinda yake gabanki".
"Mais(amma) Shehinaz ce fa?" Ta fadi a fili da siririyar muryarta tana jin abun yana tsaye mata a wuya,tasan ta damu ne kawai saboda Shehinaz dince.......su din kamar wani sashe ne na tata rayuwar.
"Idan Shehinaz ce zuciya da tunaninku ba daya bane......dole a samu banbanci cikin rayuwarku" Wani sashe na zuciyarta ya sake tunasar da ita.
Dole ta tattare komai tayi wani watsin tsiya dashi,duk da tana ji abun yana ci mata zuciya,tayi wanka ta fito har sannan bata sake jin motsin kowa ba,sai ta zauna a nutse ta shirya cikin wani budadden wando da blouse data lafe ta fidda shape din jikinta.