Sashe 83
Luu Luu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A wannan yammacin tana jin dukka dauriyarta ta qare,tana buqatar riskar akhnan din a inda take,ta zauna da ita,tayi maganan fahimta da ita,irin maganan da UWA zatayi da DIYARTA.
Ta kusa da parlor din qarshe ta samu buhaina tana faman goge gogen falon da sassanyan turaren daya kama sassan,wanda anihinsa an samar dashi ne daga companyn INCENSE BY KABO DAUGHTER +234 803 211 9803. Wani turare ne na dindindin daya kama komai na parlor din. Tana tsananin son qamshin,amma ita kanta batasan daga inda ake samo turaren ba.
"Ta fito dazun,ta zagaya ta wancan shiyyar qarshen sassanta" Buhaina ta fadi kanta a duqe da girmamawa. Kai morsa safiyya ta jinjina.
"Buhaina" Ta kirata a sanyaye
"Allah ya baki yawan rai".
"Kuyi qoqarin riqe amana da kyau......ku kula da akhnan kaman yadda masarautar agadez ta yarda daku ta dauki amanar abu mafi soyuwa a ranta ta baku".
"In sha Allahu......in sha Allah da dukkanin iyawarmu,sai inda qarfinmu ya qare" Ta fada cikin girmamawa tare da jin qarin qaunar matar da ganin darajarta me tarin yawa a idanunta.
Awa daya saura lokacin karatu ya shiga ya qaraso cikin masarautar,ya kuma samu jagorancin me wada cikin girmamawa zuwa ga sashen guda da me martaba ya mallaka masa a duk sanda yake da buqatar zama.
"Allah ya qara kusanci.....dukkanin gurin nan mallakinka ne halak malak muddin rayuwarka......ga osama nan......" Ya fada yanayin nuni da wani nutsatsen saurayi.
"Me martaba yace abaka shi don yi maka dukkan wata hidima ta cikin gidan nan,kome kake da buqata kuma kana iya sanar dani,in sha Allah za'a samar maka dashi da gaggawa". Me wada ya fadi bayan ya gabatarwa da haisam kansa a mazaunin babban bawan dake da alhakin kula da hadiman dake da alhakin kula da sassannin iyalai name martaba,wanda a yanzun haisam ya shiga qarqashinsu. Koshi me wada yayi mamakin kawo haisam din kusa da villas din iyalin me martaba haka har kusa kusa,amma bayan kallon farko da ya yiwa haisam din,kwarjininsa ya cikashi ya kuma ga dacewa da cancantar hakan.
Cikin nutsuwa ya gyada kai
"Ina godiya,zan sanar idan akwai buqatar wani abu"
"Na barka lafiya" Me wada ya furta yana juyawa gami da barin wajen.
A nutse abdii wanda a yau ya samu nasara haisam ya taho dashi yake qarewa sashen kallo. Babban bangare ne da aka wadatashi da dukkan nau'in kayan alatu......saidai bai ko kama koda kwata kwata kwatar gidansu na nan cikin agadez ba.....ballantana har ya taka ya tsallaka ya kuma kai kimar sassan da prinsii haisam din yake mallakinsa cikin masarautar jimma. Kallon abun abdii yakeyi yana dariya qasa qasa,wannan shine daidai da karin maganar da yakan ji lokaci lokaci,ana cewa wai a rashin sani kaza ta kwana kan dami. Baisan adadin gidaje irin wadannan dama wadanda suka bigeshi a girma kyau da daraja ba da muhammad haisam ya badasu kyauta ga mutanen da basu da muhallin rayuwa ba,yana kuma kan bayarwa,don ko a tahowar nan tasu ana gab da kammala ginin estate guda me dauke da gidaje dubu da zai rarrabawa mutanen da basu da matsugunni,da kuma 'yan gudun hijirar da gwamnati ta yarda da zamansu. A yanzun aka saka masa bindiga baisan adadin gidajen da obbo din nasa ya gina ya bayar ba,gidaje kuma complete gida da furniture da komai,bawai kangon gida ba.
"Gaskiya ne.....nan fa babban karramawa aka yi maka ko?......da gaske ne da akace qaramin sani qunqumi" Abdii ya qarasa fadi yana sakin dariya sosai,har yana fadawa saman daya daga cikin sofas din parlor din.
"Abdii' ya kira sunanshi da wani irin tone da yaja hankalin abdii din,sai ya miqe ya zauna daga dariyar da yake qyaqyatawa.
"Ka manta da rules dina?" Ya sake tambayarsa calmly yana shawagi cikin parlor din. Gaban wani window ya isa,yasa hannu ya yaye labulen ya kuma buda window din,take sassanyar iska ta fara shigowa ciki.
"Afwan obbo.....bazan sake ba". Abdii ya fada cikin d'ari d'ari. Burinsa su zauna a nan din tare da haisam din,to ya tabbatar indai baiyi wasa ba kadan daga aikin haisam ya maidashi gida. Wannan ne kuma sam bazai iya haqura ko lamuncewa ba,qafarsa qafar haisam din,don bazai bar komai da zai cutar dashi ya rabeshi ba,zai zame masa kaman garkuwa ne koda obbo din baya son haka,zai riqe wannan amanar ta motii da nanay.
Idanunsa ya sauke ta gurin,wani irin guri ne me kyau yake fuskantar gurin,wanda da ya duba da kyau sai ya fuskanci ginin benensa na sama akwai balcony na musamman da aka fiddata tana fuskantar gurin. Wani sirrintaccen murmushin qasaita ha kubce masa,kawai ya hango gurin da zai zauna ne yayi karatunsa cikin nutsuwa,sai ya maida window din ya rufe yana dawowa da baya.
"Kana iya tafiya sai na nemeka" Yace da abdii kai tsaye.
Idanu abdii ya fiddo waje yana duban haisam din.
"Amma obbo......"
"Shshshsh" Ya fadi yana dora yatsansa akan lips dinsa gami da zubewa abdii din idanunsa.
Janye kallonsa yayi daga kan haisam din,ya karyar da wuya kalar abun tausayi sannna ya juya ya soma takawa. Har yakai qofa ya tsaya.
"Ko kace na yafi zan dawo obbo.....Allah bazan iya zama can gidan ni kadai ba.....zan dawo,Allah obbo zan dawo" Ya qarasa fada da sauri yana fita a sassan don kada ma haisam din ya fadi abinda zai karya tsarinsa.
Murmushi kawai yabi bayan abdii dashi,ya sani dama indai abdii ne saidai kawai yayi haquri ya qyaleshi,to amma dole ya kiyaye wasu abubuwa muddin zamansu yana so ya yiwu,dole ya ajiyewa abdii wani jadawalin tsare tsare.
A nutse yaci gaba da bincike dukkan wani loko da saqo na sassan,yana kuma nazartar komai. Saboda qwarewa da yadda aikin sarrafa tsaro yabi jikinsa......ba wani guri da yake sauka hakanan ba tare daya karanci kimiyyar yanayi da kuma tsarin gini dana tsaron gurin ba.
Kusan komai yayi masa,ba wani abu da yaji zuciyarsa bata gamsu dashi ba,don haka ya soma takawa yans fitowa da nufin karantar dukka farfajiyar dake kewaye da ginin kafin ya wuce zuwa makaranta.
*AKHNAN*
A qalla ta kusa mintuna goma Idanunta a runtse,tana kuma jin yadda iska ke wasa da gashinta daga hagunta zuwa damanta.
(08187255862 lu'u lu'u paying)
A yau cikin rad'in kanta taji buqatar fitowa daga sassanta zuwa wannan kebantaccen gurin,wani guri da yake daga baya kuma daga qarshen sassanta wanda yayi linking da sashen dake maqwaftaka da nata,sashen daya zamana ba kowa a ciki iya saninta tsahon sanda aka ginashi,don haka take matuqar son zaman gurin a lokuta da dama saboda akwai privacy sosai a gurin.
Kowanne zaren tunani da kuma tarin lissafe lissafen mafita ne suke kai kawo cikin kanta. Mammina din dai,ita kadai lissafinta yake bata duk inda taje ta bugashi ta dawo.......ita daya ce mafitarta dake tafin hannunta. Hatta da mamminan an sanar mata zuwanta kusan sau hudu,amma taqi yarda a barta ta shigo ballantana ta samu damar ganinta,amma a yanzu zuciyarta na jaddada mata ita kadai ce dai zata isar da ita ga muradinta........MORSA ce kawai keda wannan matsayin,amma bata fatan abinda zai sanya ta roqi kowacce alfarma daga gurin morsa safiyyan har abada.
Tun daga nesa data zuba mata idanu sosai,sai take ganin wani sashe na kamanceceniya tsakaninta da safeena dinta,abinda ya karyar mata da zuciya kenan,ya taso da wani irin yanayi me qarfi ya azashi saman zuciyarta.
A nutse ta iso gabanta,duk da akhnan din taji alamun taku amma hakan bai sanyata ta bude idanunta ba,saboda ta sani,koma waye yake shigowa gurin cikin mutum biyu ne mafiya muhimmanci a rayuwarta,mammina ko sultane,wanda bata sanya ran zai tako inda take a cikin irin yanayi da suke ciki ita dashi yanxu.
Tsaiwar takun ya sakata bude idanun nata a hankali,saidai kuma wadda ta gani din bata taba tsammanin ganin nata ba.
Abinda tafi hasashe da tunanin zata iya aikatawa shine,ta miqe kawai ta matsa daga gurbin da matar ke tsaye,don ba wani dalili ko hujja na hada muhalli da mutumin dake adawa da dukkan wani jin dadi da kuma walwalarka......bashi da amfani musayar numfashi da mutumin da yayi sila ko sanadin shigarka wani qunci,saidai kuma komai ya sauya......wannan tunanin ya canza daga sanda idanun su suka gauraya dana morsa safiyya.
Kallon kallo suka yiwa junansu,kowannensu abinda yake yawo daban a ranshi. Batasan me ya hanats tashi ba har zuwa sanda morsa safiyya ta tako a hankali ta zauna a gefanta.
"Biftu" Ta kirata a tausashe,sunan da haruffan kuma suka sauka har cikin kunnen haisam dake takawa ta gefan farfajiyar a hankali yana duba wasu irin furanni da aka zagaye katangar gurin da aka samar da ita ta wannan bangaren da itacen bamboo masu daraja. Kadan yadan juya,amma fuskantar ba wani bane a gurin,murya ce daga can wani guri sai yaci gaba da abinda yakeyi din hankalinsa kwance ba tare daya damu da neman daga inda sautin yake ba.
"Biftu.....me yasa zaki daga hankalinki har haka?,me yasa zaki nemi cutar da kanki akan abinda yake ibada ne?......biftu,ki kori shaidanin da yake miki saqa a mugun zare,ki yaqi baqin tunanin dake wahalar da kanki da kuma rayuwarki mana......ba ta inda aure yake qasqantar da darajar diya mace,face ma daga mata martaba da kima da yakeyi,koda bata samun dukka abinda tayi buri ko hasashe a cikinsa.......amma martabar wannan igiyar da darajar sunan AURE dake kanta kadai ya isheta girma da alfahari......don Allah biftu,ki kyautata zato a rayuwarki ta gaba.....kiyi haquri ki fahimci zahirin rayuwa.......muna buqatar ganin wanzuwar jinin safeena......muna buqatar zuri'ar safeena ta wanzu a doron duniya a doron qasa kaman yadda kowannenmu ya samu nasa rassan.......safeena ce kawai bata samu wannan ba.....ki tausaya mata ta zamu zuri'a mara yankewa,ba wanda zai mata wannan sai ke......ba wanda yake da wannan ikon a hannunsa yanzu sai ke......inda ahmad yana raye......dukkan fatanmu da burinmu zaifi karkata a kansa fiye dake,amma zuwa yanzu,duk wani me sauran FATA da BURI akan AHMAD ya gama sarewa,ya gama lullube babin taba wanzuwarsa a masarautar AGADEZ. Daidai da sultane bashi da wani sauran BURI ko mafarki a kansa.....ke dindai.....ke kadai ce yanzu duk wani burinmu game da zuri'ar SAFEENA" Morsa safiyya ta samu takai qarshe da qyar muryarta na rawar dake nuna bayyanuwar raunin nan nata dake da wahalar bayyana.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
Ta kusa da parlor din qarshe ta samu buhaina tana faman goge gogen falon da sassanyan turaren daya kama sassan,wanda anihinsa an samar dashi ne daga companyn INCENSE BY KABO DAUGHTER +234 803 211 9803. Wani turare ne na dindindin daya kama komai na parlor din. Tana tsananin son qamshin,amma ita kanta batasan daga inda ake samo turaren ba.
"Ta fito dazun,ta zagaya ta wancan shiyyar qarshen sassanta" Buhaina ta fadi kanta a duqe da girmamawa. Kai morsa safiyya ta jinjina.
"Buhaina" Ta kirata a sanyaye
"Allah ya baki yawan rai".
"Kuyi qoqarin riqe amana da kyau......ku kula da akhnan kaman yadda masarautar agadez ta yarda daku ta dauki amanar abu mafi soyuwa a ranta ta baku".
"In sha Allahu......in sha Allah da dukkanin iyawarmu,sai inda qarfinmu ya qare" Ta fada cikin girmamawa tare da jin qarin qaunar matar da ganin darajarta me tarin yawa a idanunta.
Awa daya saura lokacin karatu ya shiga ya qaraso cikin masarautar,ya kuma samu jagorancin me wada cikin girmamawa zuwa ga sashen guda da me martaba ya mallaka masa a duk sanda yake da buqatar zama.
"Allah ya qara kusanci.....dukkanin gurin nan mallakinka ne halak malak muddin rayuwarka......ga osama nan......" Ya fada yanayin nuni da wani nutsatsen saurayi.
"Me martaba yace abaka shi don yi maka dukkan wata hidima ta cikin gidan nan,kome kake da buqata kuma kana iya sanar dani,in sha Allah za'a samar maka dashi da gaggawa". Me wada ya fadi bayan ya gabatarwa da haisam kansa a mazaunin babban bawan dake da alhakin kula da hadiman dake da alhakin kula da sassannin iyalai name martaba,wanda a yanzun haisam ya shiga qarqashinsu. Koshi me wada yayi mamakin kawo haisam din kusa da villas din iyalin me martaba haka har kusa kusa,amma bayan kallon farko da ya yiwa haisam din,kwarjininsa ya cikashi ya kuma ga dacewa da cancantar hakan.
Cikin nutsuwa ya gyada kai
"Ina godiya,zan sanar idan akwai buqatar wani abu"
"Na barka lafiya" Me wada ya furta yana juyawa gami da barin wajen.
A nutse abdii wanda a yau ya samu nasara haisam ya taho dashi yake qarewa sashen kallo. Babban bangare ne da aka wadatashi da dukkan nau'in kayan alatu......saidai bai ko kama koda kwata kwata kwatar gidansu na nan cikin agadez ba.....ballantana har ya taka ya tsallaka ya kuma kai kimar sassan da prinsii haisam din yake mallakinsa cikin masarautar jimma. Kallon abun abdii yakeyi yana dariya qasa qasa,wannan shine daidai da karin maganar da yakan ji lokaci lokaci,ana cewa wai a rashin sani kaza ta kwana kan dami. Baisan adadin gidaje irin wadannan dama wadanda suka bigeshi a girma kyau da daraja ba da muhammad haisam ya badasu kyauta ga mutanen da basu da muhallin rayuwa ba,yana kuma kan bayarwa,don ko a tahowar nan tasu ana gab da kammala ginin estate guda me dauke da gidaje dubu da zai rarrabawa mutanen da basu da matsugunni,da kuma 'yan gudun hijirar da gwamnati ta yarda da zamansu. A yanzun aka saka masa bindiga baisan adadin gidajen da obbo din nasa ya gina ya bayar ba,gidaje kuma complete gida da furniture da komai,bawai kangon gida ba.
"Gaskiya ne.....nan fa babban karramawa aka yi maka ko?......da gaske ne da akace qaramin sani qunqumi" Abdii ya qarasa fadi yana sakin dariya sosai,har yana fadawa saman daya daga cikin sofas din parlor din.
"Abdii' ya kira sunanshi da wani irin tone da yaja hankalin abdii din,sai ya miqe ya zauna daga dariyar da yake qyaqyatawa.
"Ka manta da rules dina?" Ya sake tambayarsa calmly yana shawagi cikin parlor din. Gaban wani window ya isa,yasa hannu ya yaye labulen ya kuma buda window din,take sassanyar iska ta fara shigowa ciki.
"Afwan obbo.....bazan sake ba". Abdii ya fada cikin d'ari d'ari. Burinsa su zauna a nan din tare da haisam din,to ya tabbatar indai baiyi wasa ba kadan daga aikin haisam ya maidashi gida. Wannan ne kuma sam bazai iya haqura ko lamuncewa ba,qafarsa qafar haisam din,don bazai bar komai da zai cutar dashi ya rabeshi ba,zai zame masa kaman garkuwa ne koda obbo din baya son haka,zai riqe wannan amanar ta motii da nanay.
Idanunsa ya sauke ta gurin,wani irin guri ne me kyau yake fuskantar gurin,wanda da ya duba da kyau sai ya fuskanci ginin benensa na sama akwai balcony na musamman da aka fiddata tana fuskantar gurin. Wani sirrintaccen murmushin qasaita ha kubce masa,kawai ya hango gurin da zai zauna ne yayi karatunsa cikin nutsuwa,sai ya maida window din ya rufe yana dawowa da baya.
"Kana iya tafiya sai na nemeka" Yace da abdii kai tsaye.
Idanu abdii ya fiddo waje yana duban haisam din.
"Amma obbo......"
"Shshshsh" Ya fadi yana dora yatsansa akan lips dinsa gami da zubewa abdii din idanunsa.
Janye kallonsa yayi daga kan haisam din,ya karyar da wuya kalar abun tausayi sannna ya juya ya soma takawa. Har yakai qofa ya tsaya.
"Ko kace na yafi zan dawo obbo.....Allah bazan iya zama can gidan ni kadai ba.....zan dawo,Allah obbo zan dawo" Ya qarasa fada da sauri yana fita a sassan don kada ma haisam din ya fadi abinda zai karya tsarinsa.
Murmushi kawai yabi bayan abdii dashi,ya sani dama indai abdii ne saidai kawai yayi haquri ya qyaleshi,to amma dole ya kiyaye wasu abubuwa muddin zamansu yana so ya yiwu,dole ya ajiyewa abdii wani jadawalin tsare tsare.
A nutse yaci gaba da bincike dukkan wani loko da saqo na sassan,yana kuma nazartar komai. Saboda qwarewa da yadda aikin sarrafa tsaro yabi jikinsa......ba wani guri da yake sauka hakanan ba tare daya karanci kimiyyar yanayi da kuma tsarin gini dana tsaron gurin ba.
Kusan komai yayi masa,ba wani abu da yaji zuciyarsa bata gamsu dashi ba,don haka ya soma takawa yans fitowa da nufin karantar dukka farfajiyar dake kewaye da ginin kafin ya wuce zuwa makaranta.
*AKHNAN*
A qalla ta kusa mintuna goma Idanunta a runtse,tana kuma jin yadda iska ke wasa da gashinta daga hagunta zuwa damanta.
(08187255862 lu'u lu'u paying)
A yau cikin rad'in kanta taji buqatar fitowa daga sassanta zuwa wannan kebantaccen gurin,wani guri da yake daga baya kuma daga qarshen sassanta wanda yayi linking da sashen dake maqwaftaka da nata,sashen daya zamana ba kowa a ciki iya saninta tsahon sanda aka ginashi,don haka take matuqar son zaman gurin a lokuta da dama saboda akwai privacy sosai a gurin.
Kowanne zaren tunani da kuma tarin lissafe lissafen mafita ne suke kai kawo cikin kanta. Mammina din dai,ita kadai lissafinta yake bata duk inda taje ta bugashi ta dawo.......ita daya ce mafitarta dake tafin hannunta. Hatta da mamminan an sanar mata zuwanta kusan sau hudu,amma taqi yarda a barta ta shigo ballantana ta samu damar ganinta,amma a yanzu zuciyarta na jaddada mata ita kadai ce dai zata isar da ita ga muradinta........MORSA ce kawai keda wannan matsayin,amma bata fatan abinda zai sanya ta roqi kowacce alfarma daga gurin morsa safiyyan har abada.
Tun daga nesa data zuba mata idanu sosai,sai take ganin wani sashe na kamanceceniya tsakaninta da safeena dinta,abinda ya karyar mata da zuciya kenan,ya taso da wani irin yanayi me qarfi ya azashi saman zuciyarta.
A nutse ta iso gabanta,duk da akhnan din taji alamun taku amma hakan bai sanyata ta bude idanunta ba,saboda ta sani,koma waye yake shigowa gurin cikin mutum biyu ne mafiya muhimmanci a rayuwarta,mammina ko sultane,wanda bata sanya ran zai tako inda take a cikin irin yanayi da suke ciki ita dashi yanxu.
Tsaiwar takun ya sakata bude idanun nata a hankali,saidai kuma wadda ta gani din bata taba tsammanin ganin nata ba.
Abinda tafi hasashe da tunanin zata iya aikatawa shine,ta miqe kawai ta matsa daga gurbin da matar ke tsaye,don ba wani dalili ko hujja na hada muhalli da mutumin dake adawa da dukkan wani jin dadi da kuma walwalarka......bashi da amfani musayar numfashi da mutumin da yayi sila ko sanadin shigarka wani qunci,saidai kuma komai ya sauya......wannan tunanin ya canza daga sanda idanun su suka gauraya dana morsa safiyya.
Kallon kallo suka yiwa junansu,kowannensu abinda yake yawo daban a ranshi. Batasan me ya hanats tashi ba har zuwa sanda morsa safiyya ta tako a hankali ta zauna a gefanta.
"Biftu" Ta kirata a tausashe,sunan da haruffan kuma suka sauka har cikin kunnen haisam dake takawa ta gefan farfajiyar a hankali yana duba wasu irin furanni da aka zagaye katangar gurin da aka samar da ita ta wannan bangaren da itacen bamboo masu daraja. Kadan yadan juya,amma fuskantar ba wani bane a gurin,murya ce daga can wani guri sai yaci gaba da abinda yakeyi din hankalinsa kwance ba tare daya damu da neman daga inda sautin yake ba.
"Biftu.....me yasa zaki daga hankalinki har haka?,me yasa zaki nemi cutar da kanki akan abinda yake ibada ne?......biftu,ki kori shaidanin da yake miki saqa a mugun zare,ki yaqi baqin tunanin dake wahalar da kanki da kuma rayuwarki mana......ba ta inda aure yake qasqantar da darajar diya mace,face ma daga mata martaba da kima da yakeyi,koda bata samun dukka abinda tayi buri ko hasashe a cikinsa.......amma martabar wannan igiyar da darajar sunan AURE dake kanta kadai ya isheta girma da alfahari......don Allah biftu,ki kyautata zato a rayuwarki ta gaba.....kiyi haquri ki fahimci zahirin rayuwa.......muna buqatar ganin wanzuwar jinin safeena......muna buqatar zuri'ar safeena ta wanzu a doron duniya a doron qasa kaman yadda kowannenmu ya samu nasa rassan.......safeena ce kawai bata samu wannan ba.....ki tausaya mata ta zamu zuri'a mara yankewa,ba wanda zai mata wannan sai ke......ba wanda yake da wannan ikon a hannunsa yanzu sai ke......inda ahmad yana raye......dukkan fatanmu da burinmu zaifi karkata a kansa fiye dake,amma zuwa yanzu,duk wani me sauran FATA da BURI akan AHMAD ya gama sarewa,ya gama lullube babin taba wanzuwarsa a masarautar AGADEZ. Daidai da sultane bashi da wani sauran BURI ko mafarki a kansa.....ke dindai.....ke kadai ce yanzu duk wani burinmu game da zuri'ar SAFEENA" Morsa safiyya ta samu takai qarshe da qyar muryarta na rawar dake nuna bayyanuwar raunin nan nata dake da wahalar bayyana.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*