Sashe 85
Luu Luu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Indai ina raye baki rasa gatanki ba......indai ina raye kuma na shirya sadaukar da komai a kanki muddin hakan zai sakaki farinciki.....koda hakan yana nufin sadaukar da fahimtar junar dake tsakanina da sultane ne,zanyi iyakacin bakin qoqari na,har sai naga abinda ya turewa buzu nadi" Ta fada tana bawa akhnan tabbaci da yaqini da dukka idanun data zubawa akhnan din su.
Wani irin abu akhnan taji yana sauka saman zuciyarta dangane da mammina din. Wata irin qaunarta me girma ta taso ta soma lullubeta,a duniya tana da masoyi sama da mammina kuwa?,anya mammina batafu sultane sonta ba kuwa?,wanne abu ne a duniya zatayi ta sakawa mammina da dimbin tarin tulin soyayyar da take mata?,wannan soyayyar bata da kama......bata da daidai,sai kawai ta fada jikin mammina tana rungumeta da kyau,itama mamminan saita riqeta tana dan bubbuga bayanta gami da fadin.
"Calme-toi,tout ira bien".
★Tsaki ya sake ja sau adadin da baisan yawansa ba,sannan ya ture system din gabansa gefe yana murza tafukan hannunsa cikin na juna.
A nutse abdii ya daga kai ya kalleshi,tunda ya shigo yakeson tambayarsa abinda ya tabashi yau amma yana tsoron saba dokokin da aka shimfida masa kafin ya samu ya aminta da qyar su zauna tare. Maher kawai ya zaba su zauna dashi cikin gidan,saboda shi din ya kasance kamar wani ido ne gareshi cikin masarautar,saidai kuma kaida fata abdii yaqi aminta ya fita,dole haisam ya barshi,bayan ya zauna ya jera masa dukkan sharuddan da abdii kansa tsaye yace ya amince,duk kuwa da cewa yasan ba komai bane zai iya bi ba a dokokin.
Numfashi ya zuqa sosai yana fesarwa ta bakinsa
"What wrong with you haisam?" Ya furta da wata murya da daga shi sai zuciyarsa kadai ke iya jinta.
Sake lumshe idanunsa yayi,yanajin wani bacin rai kadan kadan yana lasar zuciyarsa.
"Why she's so stubborn?.a silly girl.....ya akayi ta kasance d'iyar kamilin mutum me daraja da dattako irin sultane.
"Yukhrijul hayya minal mayyit?" Ayar tazo cikin kansa. Numfashi ya sauke a ransa,yana ji a rayuwarsa bai taba jin wani abu da yaji sam baiyi masa ba,bai taba jin wani abu da yakejin haushinsa yana ginuwa cikin ransa ba irin yarinyar.
Totally irin matan nan ne masu tsananin girman kai?.....rashin iya magana?.....masu jin cewa izzarsu gaban na kowa yake?.
Tunda ya soma jin maganganunta bisa akasi,ba wani magana me dadi da yaji ta iya da wani,ba wani kyakkyawan lafazi data iya fiddashi daga bakinta. Ya jima baiga mace me tsaurin ido irin nata ba.....who's she?. Tambayar qarshe da ya yiwa kansa kenan wayarsa ta dauki sassanyan ringing dinnan nasa mara hayaniya da yawa,kafin yakai ga dagawa anyi knocking,sai abdii ya bude ya tafi budewa shi kuma ya daga wayar.
A nutse ya kammala wayar,ya kuma ajiyeta a nutse yana duban abdii daketa kai kawo yana zube wasu riguna a gabansa. Da idanu kawai ya tambayi abdii din ba tare da yace komai ba,sai ya dawo ya zauna yana murmushi.
"Me martaba ne ya aiko,yana gayyatarka cin abincin dare tare dashi nan da awa daya". Idanu haisam ya zuba masa a nutse,wani lokaci quruciya da wautar abdii tana damunsa,duk da tarin nutsuwarsa da kaifin basirarsa,to amma bai sani ba,kaman shi daya abdii din yakewa haka.
"Hakan da kake yana sakani tunanin anya zaka samu gurbi kuwa a NISS?". Idanunsa gaba daya abdii ya zaro waje yana duban haisam din.
"Captain obbo......" Yayi maganar yana kwantar da murya da alamun damuwa. Haisam bai daina kallonsa ba,sai ma girarsa daya dage sama yana duban idanun abdii din.
"Inajin kaman za'a dauki kalar ma'akacin da ba'a taba dauka ba........"
"......wajen iya aiki obbo" Abdii ya qarasa masa maganar da ba hakan yayi nufin qarasawa ba. Ido haisam ya rufe yana dafe goshinsa da tafin hannunsa. Kome zai cewa abdii xai sakashi doguwar magana ne a yanayin nan da sam shi bai shiryawa hakan ba,don haka ya yanke wancan maganar
"Me kace musu?".
" Kana godiya kuma zaka halarta in sha Allahu,kaga zamu shiga muga yadda yanayin nasu qarfin ikon yake.......ina duba maka rigar daya kamata ka saka ne" Yayi maganan yana daddaga kayan dake ajiye gaban haisam din.
Sake duban abdii yakeyi,wanda yayi burus kaman bai gane ba. Zuciyarsa na sake jin qaunar yaron,ranshi kuma yana dariya can qasa da bata bayyana ba. Bilhaqqi abdii yana mantawa aiki ne kawai abinda ya kawosu agadez,bawai nuna qarfin sarautar da masarautar Ethiopia ke dashi ba,ba kuma sunzo bane don a girmamasu ko a basu girma ba,hasalima hakan na iya nakasta tasirin aikinsu.
Maher ne yayi sallama,haisam ya amsa masa,ya qaraso cikin a nutse yana rusunawa cikin girmamawar da idan sun kebe ne kawai yake samun daman nuna masa.
"Barkanka Maher" Ya amsawa Maher din a ataqaice wanda shima hankalinsa yake kan kayan da abdii keta dagawa.
"Obbo......zaka fita ne?" Maher yayi tambayar a nutse yana zama.
"Tambayeshi" Ya furta yana masa nuni da sashen da abdii din ke zaune ba tare da ya sake bi ta kansu ba,sai ya ture duka kayan gabansa yana miqewa gami da duba lokaci.
Gayyatar tazo masa a bazata,kuma tabbas inda abdii ya fadi masa zai basu haquri ne. Ba kasafai ya fiya son a jashi cikin wasu alaqoqi ko dangantaka masu zurfi ba.
Murmushi maher ya saki bayan abdii ya bashi amsar tambayarsa. Da gaske rashin sani duhu ne da bashi da kama,inda sultane yasan da waye yake tare,ko wannan apartment din daya ajiye haisam zaisan yayi babban kuskure. Girma qarfi da izzar masarauta baya jin akwai ya masarautar oromo koda cikin Ethiopia ballantana sauran qasashe,amma a iya sanin Maher,ba qaramin mutum bane sultane zaiwa gayyata irin wannan.
"Da gaske sultane ya baka babban matsayi da bana tunanin a tarihinsa akwai wanda ya samu kwatankwacin haka......karkace ba zaka halarta ba obbo......amma abdii wannan kayan duka daka dauko maidasu zakayi" Maher ya fada yana dariya.
Ya sani,sau da dama abdii din yana manta mission dinsu na shigowa agadez,girma da matsayin haisam yana bugar dashi ya manta da wannan.
Yana takawa zuwa dakinsa yana juya maganganun Maher. Dukka maganganunsa suna kan hanya,hanya daya ce kawai zata kawo masa komai cikin sauqi,tunda dukka wani bincike da kuma signals sun basu hasken wanda suke nema yana rayuwa ne cikin daya daga cikin masarautun qasar niger,masarautar agadez kuma nada girman da zarginsa yasa yafi rinjaye a kanta.
A nutse ya isa dakinsa ya tura ya shiga,idanunsa akan private patio din gaban ginin benen wanda baida wani wadataccen haske. Ma'abocin son zama ne shi a irin guraren nan,don suna bashi iska me kyau,suna kuma bashi damar warware tunanikan da suka sarqafe masa kwanya. Duqawa yayi ya dauki wani abu kaman Bluetooth ya,ya budeshi,sai ga wani abu ya bayyana kaman keyboard dan mitsitsi. Wasu number dake bada kalan sky blue ya danna jikin qaramin Keyboard din,sannna ya zari Bluetooth daya ya cusa cikin kunnensa,ya maida dan qaramin box din ya ajiye ya fara takawa a hankali zuwa private patios din,don bai samu shiga gurin ba sam tunda ya fara zagaya sassan nasa.
Fes gurin yake a tsare da wani irin tsaftar da ba zaka dauka saman bene bane. Lullube da wasu irin marbles masu daraja da sheqi. Glass ne ya zama kaman Katanga na gurin,wannan shine zai bawa wanda yake ciki cikakken daman ganin hagu da dama da kuma gaban komai dake zagaye da sassan nasa.
Straight idanunshi suka sauka ga qawataccen ginin dake gabansa. Wani madaidaicin gini da yafi kama da gidajen da aka dauko cancakat daga qasashen turawa akazo aka dasashi gaban nasa.
Daga yanayin color na paint din ginin,yawan deco na flower da ya hanga,da kuma tsarin private patios din dake kallon nasa ya tabbatar gurin mallakar macace.
Akwai qarancin hasken dake nuna ba kowacce fitila bace ta sashen a kunne,kaman yadda farfajiyarsa ma bata cika haske sosai ba.
Maida dubansa yayi hannun hagunsa,daga can din wani guri ya hanga daban,wanda da alama kebantacce ne shima,ba gurine na mu'amalar mutane ba,a yadda ya nazarci gurin yafi masa kama da wani guri na ajiye ajiyen kayan da ba nan kusa ake tabasu ko ayi amfani dasu ba. Hannun damansa ya maida dubansa,daga can nesa shima wani muhallinne na daban,sai ya janye idonsa a nutse sanda muryar omari ta cika kunnensa da cikakkiyar sallamarss.
Ya motsa labbansa a nutse yana amsawa omari din sannan ya fara takawa yana dawowa bedroom dinsa gami da maida qofar da labulen daya raba tsakanin dakin da private patios din yana rufewa.
"Mr ilaalcha gadi buusuun.......ya kakeyi da 'yammatan masarauta?" Omari ya fadi da sigar tsokanar nan tasa. Ido haisam ya lumshe sannan ya bude duka lokaci guda.
(08187255862 lu'u lu'u paying)
"Ka adana yaren oromo omari.......ba yanzu ba,ka saka a kanka kuma,shi muhammad haisam idan aiki ya taso masa,baya gane kowa,baya kuma gane komai,har sai ranar daya kammala aikinsa.....koda ya kammala dinma,nanay kawai yake ganewa" Ya fada calmly,kuma har cikin zuciyarsa yana jin hakan. Aikinsa nada matuqar muhimmancin da yakejin bazai iya hadashi da kowa ba,bazai kuma iya badashi da komai ba.
Qaramin dariya omari ya saki,halayen haisam nada abun mamaki,sun jima a tare,amma har yanzu yana kan shan mamakinsa idan yayi wani sabon abu cikin halayensa da shi baisan dashi ba.
"Naga alama.......ka dole Menelik sai data kirani,sai data nemeni da tarin jin kunyarnan taka,tana cigiyarka,gidanka satittika da dama ba haske,bata ganin motsinka kona wani a cikin gidan........ba zaka duba ba haisam kuwa?,anya?"
"Omar" Ya kirashi cikin qosawa da maganganunsa.
"Kaji da ita mana?.......saamee Menelik dukka nabar maka,kaidain mijin mace hudu ne ko?".
"Haisam mana...." Omar ya fadi da zummar jan hankalinsa,da gaske tausayinsu yakeji,don shi kansa baisan ta hanyar da zamu cimma burinsu akanshi ba,daga ita har innocent saame.
"Look please........muna bakin aiki ne ka tuna.......duk wani kira da zaka sameshi daga gareni ta wannan device din me muhimmanci ne,baida alaqa da kowacce yarinya........my rules are as simple as ABC......ya kamata ka haddacesu haka" Yadda tone din muryarsa ya canza ya tabbatarwa da omari da gaske yana nufin abinda ya fada. Murmushi me sauti ya saki yana jinjina kai kaman haisam na gabanshi.
"Bana tunanin kana lafiya haisam......even little akayi magana akan abokiyar rayuwa
"Omaaarrrrr...." Ya kirashi yana jan sunansa da qarfi,don attention nasa kawai yake buqata,wannan zancan ya isheshi haka.
"I'm focusing on what matters most to me" Ya fada yana zuqar numfashi da yakejin kaman bazai kai masa ciki ba.
Wani irin abu akhnan taji yana sauka saman zuciyarta dangane da mammina din. Wata irin qaunarta me girma ta taso ta soma lullubeta,a duniya tana da masoyi sama da mammina kuwa?,anya mammina batafu sultane sonta ba kuwa?,wanne abu ne a duniya zatayi ta sakawa mammina da dimbin tarin tulin soyayyar da take mata?,wannan soyayyar bata da kama......bata da daidai,sai kawai ta fada jikin mammina tana rungumeta da kyau,itama mamminan saita riqeta tana dan bubbuga bayanta gami da fadin.
"Calme-toi,tout ira bien".
★Tsaki ya sake ja sau adadin da baisan yawansa ba,sannan ya ture system din gabansa gefe yana murza tafukan hannunsa cikin na juna.
A nutse abdii ya daga kai ya kalleshi,tunda ya shigo yakeson tambayarsa abinda ya tabashi yau amma yana tsoron saba dokokin da aka shimfida masa kafin ya samu ya aminta da qyar su zauna tare. Maher kawai ya zaba su zauna dashi cikin gidan,saboda shi din ya kasance kamar wani ido ne gareshi cikin masarautar,saidai kuma kaida fata abdii yaqi aminta ya fita,dole haisam ya barshi,bayan ya zauna ya jera masa dukkan sharuddan da abdii kansa tsaye yace ya amince,duk kuwa da cewa yasan ba komai bane zai iya bi ba a dokokin.
Numfashi ya zuqa sosai yana fesarwa ta bakinsa
"What wrong with you haisam?" Ya furta da wata murya da daga shi sai zuciyarsa kadai ke iya jinta.
Sake lumshe idanunsa yayi,yanajin wani bacin rai kadan kadan yana lasar zuciyarsa.
"Why she's so stubborn?.a silly girl.....ya akayi ta kasance d'iyar kamilin mutum me daraja da dattako irin sultane.
"Yukhrijul hayya minal mayyit?" Ayar tazo cikin kansa. Numfashi ya sauke a ransa,yana ji a rayuwarsa bai taba jin wani abu da yaji sam baiyi masa ba,bai taba jin wani abu da yakejin haushinsa yana ginuwa cikin ransa ba irin yarinyar.
Totally irin matan nan ne masu tsananin girman kai?.....rashin iya magana?.....masu jin cewa izzarsu gaban na kowa yake?.
Tunda ya soma jin maganganunta bisa akasi,ba wani magana me dadi da yaji ta iya da wani,ba wani kyakkyawan lafazi data iya fiddashi daga bakinta. Ya jima baiga mace me tsaurin ido irin nata ba.....who's she?. Tambayar qarshe da ya yiwa kansa kenan wayarsa ta dauki sassanyan ringing dinnan nasa mara hayaniya da yawa,kafin yakai ga dagawa anyi knocking,sai abdii ya bude ya tafi budewa shi kuma ya daga wayar.
A nutse ya kammala wayar,ya kuma ajiyeta a nutse yana duban abdii daketa kai kawo yana zube wasu riguna a gabansa. Da idanu kawai ya tambayi abdii din ba tare da yace komai ba,sai ya dawo ya zauna yana murmushi.
"Me martaba ne ya aiko,yana gayyatarka cin abincin dare tare dashi nan da awa daya". Idanu haisam ya zuba masa a nutse,wani lokaci quruciya da wautar abdii tana damunsa,duk da tarin nutsuwarsa da kaifin basirarsa,to amma bai sani ba,kaman shi daya abdii din yakewa haka.
"Hakan da kake yana sakani tunanin anya zaka samu gurbi kuwa a NISS?". Idanunsa gaba daya abdii ya zaro waje yana duban haisam din.
"Captain obbo......" Yayi maganar yana kwantar da murya da alamun damuwa. Haisam bai daina kallonsa ba,sai ma girarsa daya dage sama yana duban idanun abdii din.
"Inajin kaman za'a dauki kalar ma'akacin da ba'a taba dauka ba........"
"......wajen iya aiki obbo" Abdii ya qarasa masa maganar da ba hakan yayi nufin qarasawa ba. Ido haisam ya rufe yana dafe goshinsa da tafin hannunsa. Kome zai cewa abdii xai sakashi doguwar magana ne a yanayin nan da sam shi bai shiryawa hakan ba,don haka ya yanke wancan maganar
"Me kace musu?".
" Kana godiya kuma zaka halarta in sha Allahu,kaga zamu shiga muga yadda yanayin nasu qarfin ikon yake.......ina duba maka rigar daya kamata ka saka ne" Yayi maganan yana daddaga kayan dake ajiye gaban haisam din.
Sake duban abdii yakeyi,wanda yayi burus kaman bai gane ba. Zuciyarsa na sake jin qaunar yaron,ranshi kuma yana dariya can qasa da bata bayyana ba. Bilhaqqi abdii yana mantawa aiki ne kawai abinda ya kawosu agadez,bawai nuna qarfin sarautar da masarautar Ethiopia ke dashi ba,ba kuma sunzo bane don a girmamasu ko a basu girma ba,hasalima hakan na iya nakasta tasirin aikinsu.
Maher ne yayi sallama,haisam ya amsa masa,ya qaraso cikin a nutse yana rusunawa cikin girmamawar da idan sun kebe ne kawai yake samun daman nuna masa.
"Barkanka Maher" Ya amsawa Maher din a ataqaice wanda shima hankalinsa yake kan kayan da abdii keta dagawa.
"Obbo......zaka fita ne?" Maher yayi tambayar a nutse yana zama.
"Tambayeshi" Ya furta yana masa nuni da sashen da abdii din ke zaune ba tare da ya sake bi ta kansu ba,sai ya ture duka kayan gabansa yana miqewa gami da duba lokaci.
Gayyatar tazo masa a bazata,kuma tabbas inda abdii ya fadi masa zai basu haquri ne. Ba kasafai ya fiya son a jashi cikin wasu alaqoqi ko dangantaka masu zurfi ba.
Murmushi maher ya saki bayan abdii ya bashi amsar tambayarsa. Da gaske rashin sani duhu ne da bashi da kama,inda sultane yasan da waye yake tare,ko wannan apartment din daya ajiye haisam zaisan yayi babban kuskure. Girma qarfi da izzar masarauta baya jin akwai ya masarautar oromo koda cikin Ethiopia ballantana sauran qasashe,amma a iya sanin Maher,ba qaramin mutum bane sultane zaiwa gayyata irin wannan.
"Da gaske sultane ya baka babban matsayi da bana tunanin a tarihinsa akwai wanda ya samu kwatankwacin haka......karkace ba zaka halarta ba obbo......amma abdii wannan kayan duka daka dauko maidasu zakayi" Maher ya fada yana dariya.
Ya sani,sau da dama abdii din yana manta mission dinsu na shigowa agadez,girma da matsayin haisam yana bugar dashi ya manta da wannan.
Yana takawa zuwa dakinsa yana juya maganganun Maher. Dukka maganganunsa suna kan hanya,hanya daya ce kawai zata kawo masa komai cikin sauqi,tunda dukka wani bincike da kuma signals sun basu hasken wanda suke nema yana rayuwa ne cikin daya daga cikin masarautun qasar niger,masarautar agadez kuma nada girman da zarginsa yasa yafi rinjaye a kanta.
A nutse ya isa dakinsa ya tura ya shiga,idanunsa akan private patio din gaban ginin benen wanda baida wani wadataccen haske. Ma'abocin son zama ne shi a irin guraren nan,don suna bashi iska me kyau,suna kuma bashi damar warware tunanikan da suka sarqafe masa kwanya. Duqawa yayi ya dauki wani abu kaman Bluetooth ya,ya budeshi,sai ga wani abu ya bayyana kaman keyboard dan mitsitsi. Wasu number dake bada kalan sky blue ya danna jikin qaramin Keyboard din,sannna ya zari Bluetooth daya ya cusa cikin kunnensa,ya maida dan qaramin box din ya ajiye ya fara takawa a hankali zuwa private patios din,don bai samu shiga gurin ba sam tunda ya fara zagaya sassan nasa.
Fes gurin yake a tsare da wani irin tsaftar da ba zaka dauka saman bene bane. Lullube da wasu irin marbles masu daraja da sheqi. Glass ne ya zama kaman Katanga na gurin,wannan shine zai bawa wanda yake ciki cikakken daman ganin hagu da dama da kuma gaban komai dake zagaye da sassan nasa.
Straight idanunshi suka sauka ga qawataccen ginin dake gabansa. Wani madaidaicin gini da yafi kama da gidajen da aka dauko cancakat daga qasashen turawa akazo aka dasashi gaban nasa.
Daga yanayin color na paint din ginin,yawan deco na flower da ya hanga,da kuma tsarin private patios din dake kallon nasa ya tabbatar gurin mallakar macace.
Akwai qarancin hasken dake nuna ba kowacce fitila bace ta sashen a kunne,kaman yadda farfajiyarsa ma bata cika haske sosai ba.
Maida dubansa yayi hannun hagunsa,daga can din wani guri ya hanga daban,wanda da alama kebantacce ne shima,ba gurine na mu'amalar mutane ba,a yadda ya nazarci gurin yafi masa kama da wani guri na ajiye ajiyen kayan da ba nan kusa ake tabasu ko ayi amfani dasu ba. Hannun damansa ya maida dubansa,daga can nesa shima wani muhallinne na daban,sai ya janye idonsa a nutse sanda muryar omari ta cika kunnensa da cikakkiyar sallamarss.
Ya motsa labbansa a nutse yana amsawa omari din sannan ya fara takawa yana dawowa bedroom dinsa gami da maida qofar da labulen daya raba tsakanin dakin da private patios din yana rufewa.
"Mr ilaalcha gadi buusuun.......ya kakeyi da 'yammatan masarauta?" Omari ya fadi da sigar tsokanar nan tasa. Ido haisam ya lumshe sannan ya bude duka lokaci guda.
(08187255862 lu'u lu'u paying)
"Ka adana yaren oromo omari.......ba yanzu ba,ka saka a kanka kuma,shi muhammad haisam idan aiki ya taso masa,baya gane kowa,baya kuma gane komai,har sai ranar daya kammala aikinsa.....koda ya kammala dinma,nanay kawai yake ganewa" Ya fada calmly,kuma har cikin zuciyarsa yana jin hakan. Aikinsa nada matuqar muhimmancin da yakejin bazai iya hadashi da kowa ba,bazai kuma iya badashi da komai ba.
Qaramin dariya omari ya saki,halayen haisam nada abun mamaki,sun jima a tare,amma har yanzu yana kan shan mamakinsa idan yayi wani sabon abu cikin halayensa da shi baisan dashi ba.
"Naga alama.......ka dole Menelik sai data kirani,sai data nemeni da tarin jin kunyarnan taka,tana cigiyarka,gidanka satittika da dama ba haske,bata ganin motsinka kona wani a cikin gidan........ba zaka duba ba haisam kuwa?,anya?"
"Omar" Ya kirashi cikin qosawa da maganganunsa.
"Kaji da ita mana?.......saamee Menelik dukka nabar maka,kaidain mijin mace hudu ne ko?".
"Haisam mana...." Omar ya fadi da zummar jan hankalinsa,da gaske tausayinsu yakeji,don shi kansa baisan ta hanyar da zamu cimma burinsu akanshi ba,daga ita har innocent saame.
"Look please........muna bakin aiki ne ka tuna.......duk wani kira da zaka sameshi daga gareni ta wannan device din me muhimmanci ne,baida alaqa da kowacce yarinya........my rules are as simple as ABC......ya kamata ka haddacesu haka" Yadda tone din muryarsa ya canza ya tabbatarwa da omari da gaske yana nufin abinda ya fada. Murmushi me sauti ya saki yana jinjina kai kaman haisam na gabanshi.
"Bana tunanin kana lafiya haisam......even little akayi magana akan abokiyar rayuwa
"Omaaarrrrr...." Ya kirashi yana jan sunansa da qarfi,don attention nasa kawai yake buqata,wannan zancan ya isheshi haka.
"I'm focusing on what matters most to me" Ya fada yana zuqar numfashi da yakejin kaman bazai kai masa ciki ba.