Sashe 55
Luu Luu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta gama fahimta ta kuma gama gane komai,wannan karon al'amarin yafi kama da taron dangi akayi mata,momma......Nannie uwa uba sultane dinma.
Zata tsammaci hakan daga momma,harma sama da hakan,amma daga sultane kuma ko Nannie dukka baqon abu ne a wajenta.
Wai wanne dalili ne zai sanya ba zata tsani morsa safiyya ba?.......me yasa ba zataji bata qaunarta ba?. Tana da cikkakken imani da yaqinin komai ita ta assasashi,komai kuma ita ta shiryashi,in fact ma jikinta yana bata ita ta jawo komai ta hadashi daidai da muradinta da cikar burinta.
Tsam ta miqe tana zare ribbon din kanta,ta kuma daure gashinta tsakiyar kanta da wani irin zafi,jelar ta sauka gadon bayanta tana lilo. Banda umarnin daga sultane ya fito......bata tunanin yau duk duniya akwai wani wanda ya isa ya sanyata ta fuskanci wannan baqon. Umarnin sultane ne......zata cikashi,amma kuma ta hanyar da takeso,ta kuma hanyar da taga dama itama.
*FALAAK*
Sallamar morsa safiyya ya sanyata daga kanta daga duba shafin littafin dake hannunta,wanda kusan ta zauna ne kawai tana duba littafin saboda ragewa kanta lokaci da kuma dogon zama,amma sam ba wai don tana jin dadin karatun bane.
"Ya dai?" Morsa ta tambayeta tana zama daga gefe hadi da qoqarin gyara lullubin tattausan mayafin jikinta.
Ajiyar zuciya falaak din ta sauke tana rufe littafin.
"Gaba daya momma ji nake kaman karatun ya fita a kaina,oustaz Ousmane ya iya karatu morsa,gani nake kaman ba zamu samu wanda ya kaishi ba". Murmushi kadan momma ta saki tana daukan remote don sauya channel din dake aiki zuwa TRT africa.
"Ba'a gaggawar yanke hukunci,kuma kowanne dan adam da irin baiwarsa,sani ne bamuyi ba". Kai ta gyada a hankali falaak din,momma taci gaba da cewa.
"Ya iso tun tuni,suna masallaci da sultane,bayan sallar la'asar din zai shigo,kuma naji ma an idar da sallar.......ki yiwa baraka magana ta hada miki kansu Aafreen ku wuce gurin daukan karatun,kar a fara saba dokarsa tun a ranar farko". Numfashi falaak taja tana tabe baki. Wannan malamin me tarin doka da tsarin tsiya zataso ta ganshi,zataso ta gani ta kuma san irin ilimin da yake dashi haka da har ya zarta oustaz Ousmane yake sanya dokokin da ko shi bai taba sanya musu su haka ba.
*SULTANE*
Yadda haisam ya saba zama yayi musabaha da mutanen dake bayansa bayan kammala salla a masallacin juma'a na jimma,haka ma yanzun yayi. Abun da ya baiwa mutane da dama.mamaki aka shiga kallon kallo ganin yadda ya baiwa sultane hannu kansa tsaye. Irin wannan kwarjinin da yake musu kaman sam shi bai masa ba?.
Qasan ran sultane yake murmushi,wani irin nutsuwa na shigarsa tattare da haisam din. A cikin ayyukansa da dukka motsinsa ya fahimci yadda ilimin addini ya wadaceshi qwarai da gaske.
"Ayi masa tattaki zuwa,sannan a sake inganta gurin karatunsu idan yanayin da aka tanadarwa gurin bai masa ba" Umarnin da sultane ya bayar kenan. Cikin girmamawa haisam ya rusuna,da hausarsa da bata bada miqaqqen sauti da amo irin na cikakken bahaushe ba yace.
"Godiya nake".
Duk wani taku nasa yana tafiya ne da ilimi ankarewa da kuma karantar kowanne motsi na gidan. Kowanne taku da zaiyi yana yinsa ne cikin sanyawa abubuwa da yawa alama.......haddace yanayin abubuwa da kuma gilmawar kowanne mutum da motsin iskar dake kaiwa tana kawowa.
Kafin su isa gurin ya gama rarrabe tsarin sassannin da ainihin kebantacciyar daular da iyalin sultane ke ciki,adadin sassan ya kuma fahimci sassan matan nasa......banbancin hadimai na kowanne sashe,duk da bai gama tabbatar da hadiman sassan mammina da na momma ba.
Basu gama shiga gurin ba,amma tun daga farko yaji gurin yayi masa,tun daga farkon gurin kuma yasan gurin kebantaccen guri ne na musamman koda kuwa a cikin gidan.
Kai tsaye zaka iya kiransa da gandun daji,saboda yadda aka qawata gurin da nau'ikan shuke shuke 'yan qasar France. Akwai wata qirqirarriyar qorama me wasu fararen duwatsu da kifaye masu nau'ika daban daban dake kai.kawo a ciki. Ido ya lumshe ya shaqi iskar gurin a sirrance. Saita tuna masa da nasa sassan daya ajiye musamman a jimma,wanda yake da kwatankwacin wanna tsarin gaba dayansa.
A duk sanda yakeson duba wani babban littafi,yin research akan wata mas'ala,ko kuma yin research game da wani security issue daya shafi security intelligence yafi zama a nan,zai kammala komai a nutse yana kewaye da hadimai,don a irin wannan lokacin nanay kawai yake bawa izinin ganinsa,sai kuma mooti,wanda yawa yawan lokuta yafi zuwa ya sameshi a gurin hutawarsa dake cikin gidan,ko cikin fadarsa idan buqatar ganin ta canne.
Kanta na sunkuye tana ta qoqarin sake duba karatuttukan baya,yayin da har yanzu zuciyarta keta kai kawo,ta kuma kasa jin wani cikakken aminci da malamin.
Alamun takun da taji shi ya sakata daga kanta tana tsammanin ko su aeera ne suka tashi daga gurin da zasu dinga nasu karatun da yake gefanta kadan.
Karon farko idanunta ya sauka a kansu. Mutum uku ne......da guda biyu kawai ta sani a cikinsu. Maher daya kasance kaman dalibin oustaz Ousmane,sannan kuma jifa jifa takan ganshi tsakanin sassansu duk da batasan me yake zuwa yi ba. Na biyun bala ne......daya daga cikin manyan hadimansu,sai na ukun......
Mutum na ukun daya banbanta da kowa a cikinsu,mutum na ukun da ta ganshi ya fita daban,tamkar gold din da aka jefa tsakiyar gama garin qarafa.
Cikin nutsuwa yake maganar da bata iya jin me yake fada,amma dai ya janye rawaninsa zuwa qasar habarsa,abinda ya bawa kyawawan labbansa masu sulbi damar fitowa,suna kuma juyawa a hankali.
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" Ta furta da sauri da qaramin sauti tana janye idanunta gefe daya saboda wani mummunar faduwa da gabanta yayi zuciyarta na qara wani irin mahaukacin bugu da bata taba jin haka a tattare da ita ba sai yanzu.
Cikin jikinta takejin qarin kusantowarsu da gurin,yayin da bugun zuciyarta har yanzu yaqi daidaituwa,wasi wasi kuma ya cika mata zuciya tanason rarrabe waye malamin a cikinsu?.
Bala dai ta sanshi,saboda haka ba wata magana a kanshi,Maher kam bata tunanun oustaz Ousmane zai kawo Maher a mazaunin malaminsu bayan dalibi ne shi kansa a wajensa. Sai kuma na ukun?.......
Sam bai mata kama da malamin da zai shiga gidan sarauta da zummar koyarwa ba. Ta kowacce fuska kamanni dama yanayinsa. Wani irin kwantaccen kwarjini take gani yana haska kowanni motsi nasa,irin kwarjinin da a fuskar sultane kawai take ganinsa.
Eh akwai kamala me yawa da wata irin nutsuwa shimfide saman fuskarsa......yanayin shigarsa ya sake tabbatar mata da yawan ilimin daya ratsa halittarsa gaba daya,to amma......"
"Sheik haisam ya iso ranki ya dade....." Muryar bala daya tsugunna saman qafafunta ta dauko hankalinta zuwa wajen.
"SHEIK HAISAM" Ta maimaita sunan tana motsa labbanta,tana kuma jin wani irin sanyi da taushi a iya sunan kawai.
"Eh gashi can Allah ya taimakeki......sultane yace a gaya miki,a bashi dukkan girmamawar da shi zaa bashi,a yanzun sheik malaminsa ne". Kai take jinjinawa a hankali tana jin kanta kaman ya mata nauyi,bugun da zuciyarta kuma keyi yana nan bai sauya ba. Da iya saqon sultane kadai tana iya fahimtar muhimmancin da ya bawa abu
"Na barku lafiya" Bala ya fada yana tashi gami da juyawa suna barin gurin shida Maher.
Shurun da taji sai muryar Aafreen kadan take tashi ya sanyata waiwayawa kaman me ciwon wuya.
Fuskarsa shine abu na farko data soma sauke idanunta a kai. Wasu irin zagayayyun idanuwa masu girman da suka bayyana kansu tsakanin fuskarsa data zama circle cikin rawaninsa. Yana zaune sosai saman babban kilishin dake shimfide a wajen ba tare daya damu ya zauna kan kujerun da aka ajjiye masa ba a wajen masu tsananin taushi.
Aeera ce zaune a gabansa,ta bude littafinta na nuraniyya,ya dora yatsansa akai itama haka,da alama karanto masa takeyi,sai Aafreen dake zaune daga bayan aaera kadan,ta tallafe habarta da hannunta tana kallonsu fuskarta yalwace da fara'a,da alama akwai abinda yayi mata dadi.
Sake janye idanunta tayi tana kiran sunan Allah. Sai take jinta gaba daya kamar a rude take,kaman ta fita daga nutsuwarta ta dazu.
Canki canki takeyi,ita zata kai kanta?,ko kuma idan ya gama da yaran zai nemeta?.
To amma tunda suka shigo gurin bataga wani alama da zai nuna yasan da wanzuwarta a gurin ba,baiyi wani motsi ko yaya da zai alamta mata yasan tana gurin ba.
Bata da wani karsashi ko qwarin gwiwa,don haka ta zabi ci gaba da zama a gurin,ta sunkuyar da kanta kan littafin,duk da bata gane komai,bata kuma fahimtar komai,kacokam hankalinta yana wajensu da bata iya jin tasa muryar,sai muryar yaran kawai,su dinma yau cikin nutsuwa suke magana.
Jifa jifa tana satar kallo su,saidai ko sau daya ba wani alama daya nuna ansan da zamanta a wajen. Ta sauke ajiyar zuciya daidai sanda taji muryar aeera saman kanta.
"Kizo inji sheikh haisaaam". Yadda yarinyar ta furta sunan da wani irin tone sai taji sunan ya sakeyi mata dadi,ya kuma qayatar da ita dari bisa dari,qasan zuciyarta da dan mamakinsa na yadda ya aika tazo din ta tattare litattafanta ta miqe tana sake satar kallonsa. Tanason ta banbance yaushe ya kalleta har ya fahimci tana gurin ma?,saidai kuma har ta isa gurin ta tube takalmanta ta zauna a nutse bata gane komai ba.
"Wa'alaikumussalam warahmatullah" Ya furta Kansa yana saman littafin Aafreen da oustaz Ousmane yake basu aiki lokaci lokaci.
Qara tsanantuwa bugun zuciyarta yayi,har ta gaza yin qasa da kanta ta daga kanta tana dubansa kai tsaye. Abubuwa biyu suka rikitata,na farko wani baiwa dake cikin sautinsa da muryarsa da bata taba jin irinsa ba,na biyu kuma tasan yana son gaya mata batayi sallama ba.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
PAGE 46
__________________________
HALY JASHERU VENTURES.
munada tsuntsaye na kasashen waje masu kyau da daukar hankali kmn haka.
TATTABARU
French modain(Argentina)
Indian faintail (3in1)
indigo,opal,Andalu,Lahore,busa,Bukhara, indomie,Jacobin dasauransu.
Zata tsammaci hakan daga momma,harma sama da hakan,amma daga sultane kuma ko Nannie dukka baqon abu ne a wajenta.
Wai wanne dalili ne zai sanya ba zata tsani morsa safiyya ba?.......me yasa ba zataji bata qaunarta ba?. Tana da cikkakken imani da yaqinin komai ita ta assasashi,komai kuma ita ta shiryashi,in fact ma jikinta yana bata ita ta jawo komai ta hadashi daidai da muradinta da cikar burinta.
Tsam ta miqe tana zare ribbon din kanta,ta kuma daure gashinta tsakiyar kanta da wani irin zafi,jelar ta sauka gadon bayanta tana lilo. Banda umarnin daga sultane ya fito......bata tunanin yau duk duniya akwai wani wanda ya isa ya sanyata ta fuskanci wannan baqon. Umarnin sultane ne......zata cikashi,amma kuma ta hanyar da takeso,ta kuma hanyar da taga dama itama.
*FALAAK*
Sallamar morsa safiyya ya sanyata daga kanta daga duba shafin littafin dake hannunta,wanda kusan ta zauna ne kawai tana duba littafin saboda ragewa kanta lokaci da kuma dogon zama,amma sam ba wai don tana jin dadin karatun bane.
"Ya dai?" Morsa ta tambayeta tana zama daga gefe hadi da qoqarin gyara lullubin tattausan mayafin jikinta.
Ajiyar zuciya falaak din ta sauke tana rufe littafin.
"Gaba daya momma ji nake kaman karatun ya fita a kaina,oustaz Ousmane ya iya karatu morsa,gani nake kaman ba zamu samu wanda ya kaishi ba". Murmushi kadan momma ta saki tana daukan remote don sauya channel din dake aiki zuwa TRT africa.
"Ba'a gaggawar yanke hukunci,kuma kowanne dan adam da irin baiwarsa,sani ne bamuyi ba". Kai ta gyada a hankali falaak din,momma taci gaba da cewa.
"Ya iso tun tuni,suna masallaci da sultane,bayan sallar la'asar din zai shigo,kuma naji ma an idar da sallar.......ki yiwa baraka magana ta hada miki kansu Aafreen ku wuce gurin daukan karatun,kar a fara saba dokarsa tun a ranar farko". Numfashi falaak taja tana tabe baki. Wannan malamin me tarin doka da tsarin tsiya zataso ta ganshi,zataso ta gani ta kuma san irin ilimin da yake dashi haka da har ya zarta oustaz Ousmane yake sanya dokokin da ko shi bai taba sanya musu su haka ba.
*SULTANE*
Yadda haisam ya saba zama yayi musabaha da mutanen dake bayansa bayan kammala salla a masallacin juma'a na jimma,haka ma yanzun yayi. Abun da ya baiwa mutane da dama.mamaki aka shiga kallon kallo ganin yadda ya baiwa sultane hannu kansa tsaye. Irin wannan kwarjinin da yake musu kaman sam shi bai masa ba?.
Qasan ran sultane yake murmushi,wani irin nutsuwa na shigarsa tattare da haisam din. A cikin ayyukansa da dukka motsinsa ya fahimci yadda ilimin addini ya wadaceshi qwarai da gaske.
"Ayi masa tattaki zuwa,sannan a sake inganta gurin karatunsu idan yanayin da aka tanadarwa gurin bai masa ba" Umarnin da sultane ya bayar kenan. Cikin girmamawa haisam ya rusuna,da hausarsa da bata bada miqaqqen sauti da amo irin na cikakken bahaushe ba yace.
"Godiya nake".
Duk wani taku nasa yana tafiya ne da ilimi ankarewa da kuma karantar kowanne motsi na gidan. Kowanne taku da zaiyi yana yinsa ne cikin sanyawa abubuwa da yawa alama.......haddace yanayin abubuwa da kuma gilmawar kowanne mutum da motsin iskar dake kaiwa tana kawowa.
Kafin su isa gurin ya gama rarrabe tsarin sassannin da ainihin kebantacciyar daular da iyalin sultane ke ciki,adadin sassan ya kuma fahimci sassan matan nasa......banbancin hadimai na kowanne sashe,duk da bai gama tabbatar da hadiman sassan mammina da na momma ba.
Basu gama shiga gurin ba,amma tun daga farko yaji gurin yayi masa,tun daga farkon gurin kuma yasan gurin kebantaccen guri ne na musamman koda kuwa a cikin gidan.
Kai tsaye zaka iya kiransa da gandun daji,saboda yadda aka qawata gurin da nau'ikan shuke shuke 'yan qasar France. Akwai wata qirqirarriyar qorama me wasu fararen duwatsu da kifaye masu nau'ika daban daban dake kai.kawo a ciki. Ido ya lumshe ya shaqi iskar gurin a sirrance. Saita tuna masa da nasa sassan daya ajiye musamman a jimma,wanda yake da kwatankwacin wanna tsarin gaba dayansa.
A duk sanda yakeson duba wani babban littafi,yin research akan wata mas'ala,ko kuma yin research game da wani security issue daya shafi security intelligence yafi zama a nan,zai kammala komai a nutse yana kewaye da hadimai,don a irin wannan lokacin nanay kawai yake bawa izinin ganinsa,sai kuma mooti,wanda yawa yawan lokuta yafi zuwa ya sameshi a gurin hutawarsa dake cikin gidan,ko cikin fadarsa idan buqatar ganin ta canne.
Kanta na sunkuye tana ta qoqarin sake duba karatuttukan baya,yayin da har yanzu zuciyarta keta kai kawo,ta kuma kasa jin wani cikakken aminci da malamin.
Alamun takun da taji shi ya sakata daga kanta tana tsammanin ko su aeera ne suka tashi daga gurin da zasu dinga nasu karatun da yake gefanta kadan.
Karon farko idanunta ya sauka a kansu. Mutum uku ne......da guda biyu kawai ta sani a cikinsu. Maher daya kasance kaman dalibin oustaz Ousmane,sannan kuma jifa jifa takan ganshi tsakanin sassansu duk da batasan me yake zuwa yi ba. Na biyun bala ne......daya daga cikin manyan hadimansu,sai na ukun......
Mutum na ukun daya banbanta da kowa a cikinsu,mutum na ukun da ta ganshi ya fita daban,tamkar gold din da aka jefa tsakiyar gama garin qarafa.
Cikin nutsuwa yake maganar da bata iya jin me yake fada,amma dai ya janye rawaninsa zuwa qasar habarsa,abinda ya bawa kyawawan labbansa masu sulbi damar fitowa,suna kuma juyawa a hankali.
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" Ta furta da sauri da qaramin sauti tana janye idanunta gefe daya saboda wani mummunar faduwa da gabanta yayi zuciyarta na qara wani irin mahaukacin bugu da bata taba jin haka a tattare da ita ba sai yanzu.
Cikin jikinta takejin qarin kusantowarsu da gurin,yayin da bugun zuciyarta har yanzu yaqi daidaituwa,wasi wasi kuma ya cika mata zuciya tanason rarrabe waye malamin a cikinsu?.
Bala dai ta sanshi,saboda haka ba wata magana a kanshi,Maher kam bata tunanun oustaz Ousmane zai kawo Maher a mazaunin malaminsu bayan dalibi ne shi kansa a wajensa. Sai kuma na ukun?.......
Sam bai mata kama da malamin da zai shiga gidan sarauta da zummar koyarwa ba. Ta kowacce fuska kamanni dama yanayinsa. Wani irin kwantaccen kwarjini take gani yana haska kowanni motsi nasa,irin kwarjinin da a fuskar sultane kawai take ganinsa.
Eh akwai kamala me yawa da wata irin nutsuwa shimfide saman fuskarsa......yanayin shigarsa ya sake tabbatar mata da yawan ilimin daya ratsa halittarsa gaba daya,to amma......"
"Sheik haisam ya iso ranki ya dade....." Muryar bala daya tsugunna saman qafafunta ta dauko hankalinta zuwa wajen.
"SHEIK HAISAM" Ta maimaita sunan tana motsa labbanta,tana kuma jin wani irin sanyi da taushi a iya sunan kawai.
"Eh gashi can Allah ya taimakeki......sultane yace a gaya miki,a bashi dukkan girmamawar da shi zaa bashi,a yanzun sheik malaminsa ne". Kai take jinjinawa a hankali tana jin kanta kaman ya mata nauyi,bugun da zuciyarta kuma keyi yana nan bai sauya ba. Da iya saqon sultane kadai tana iya fahimtar muhimmancin da ya bawa abu
"Na barku lafiya" Bala ya fada yana tashi gami da juyawa suna barin gurin shida Maher.
Shurun da taji sai muryar Aafreen kadan take tashi ya sanyata waiwayawa kaman me ciwon wuya.
Fuskarsa shine abu na farko data soma sauke idanunta a kai. Wasu irin zagayayyun idanuwa masu girman da suka bayyana kansu tsakanin fuskarsa data zama circle cikin rawaninsa. Yana zaune sosai saman babban kilishin dake shimfide a wajen ba tare daya damu ya zauna kan kujerun da aka ajjiye masa ba a wajen masu tsananin taushi.
Aeera ce zaune a gabansa,ta bude littafinta na nuraniyya,ya dora yatsansa akai itama haka,da alama karanto masa takeyi,sai Aafreen dake zaune daga bayan aaera kadan,ta tallafe habarta da hannunta tana kallonsu fuskarta yalwace da fara'a,da alama akwai abinda yayi mata dadi.
Sake janye idanunta tayi tana kiran sunan Allah. Sai take jinta gaba daya kamar a rude take,kaman ta fita daga nutsuwarta ta dazu.
Canki canki takeyi,ita zata kai kanta?,ko kuma idan ya gama da yaran zai nemeta?.
To amma tunda suka shigo gurin bataga wani alama da zai nuna yasan da wanzuwarta a gurin ba,baiyi wani motsi ko yaya da zai alamta mata yasan tana gurin ba.
Bata da wani karsashi ko qwarin gwiwa,don haka ta zabi ci gaba da zama a gurin,ta sunkuyar da kanta kan littafin,duk da bata gane komai,bata kuma fahimtar komai,kacokam hankalinta yana wajensu da bata iya jin tasa muryar,sai muryar yaran kawai,su dinma yau cikin nutsuwa suke magana.
Jifa jifa tana satar kallo su,saidai ko sau daya ba wani alama daya nuna ansan da zamanta a wajen. Ta sauke ajiyar zuciya daidai sanda taji muryar aeera saman kanta.
"Kizo inji sheikh haisaaam". Yadda yarinyar ta furta sunan da wani irin tone sai taji sunan ya sakeyi mata dadi,ya kuma qayatar da ita dari bisa dari,qasan zuciyarta da dan mamakinsa na yadda ya aika tazo din ta tattare litattafanta ta miqe tana sake satar kallonsa. Tanason ta banbance yaushe ya kalleta har ya fahimci tana gurin ma?,saidai kuma har ta isa gurin ta tube takalmanta ta zauna a nutse bata gane komai ba.
"Wa'alaikumussalam warahmatullah" Ya furta Kansa yana saman littafin Aafreen da oustaz Ousmane yake basu aiki lokaci lokaci.
Qara tsanantuwa bugun zuciyarta yayi,har ta gaza yin qasa da kanta ta daga kanta tana dubansa kai tsaye. Abubuwa biyu suka rikitata,na farko wani baiwa dake cikin sautinsa da muryarsa da bata taba jin irinsa ba,na biyu kuma tasan yana son gaya mata batayi sallama ba.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
PAGE 46
__________________________
HALY JASHERU VENTURES.
munada tsuntsaye na kasashen waje masu kyau da daukar hankali kmn haka.
TATTABARU
French modain(Argentina)
Indian faintail (3in1)
indigo,opal,Andalu,Lahore,busa,Bukhara, indomie,Jacobin dasauransu.