Sashe 46
Luu Luu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*kuse ABAYAS takanas kuma kai tsaye DAGA EGYPT su iso gareku cikin kasa da kwana goma KACAL!✌🏽*
*_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_*
*_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽
*Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu*
*muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA*
*Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah*
+20 114 341 0873 ko kuma
0810 959 7791
https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt
____________________________
"Har yanzu baki gama fuskantar matsayinki ba akhnan.......kinsan girman matsayinki da martabarki a qasar agadez?.......ina kikai jarumtarki?.....me yasa zaki bar qaramar damuwa ta mamayeki har haka?.....ba haka na sanki ba.....ba kuma haka nakeso naci gaba da ganinki ba" Ta furta cikin kambamata da kuma motsa mata matsayinta.
Idanunta ta lumshe ta kuma budesu a sarauce.
"Ina nan yadda nake mammina.....ban canza ba,bana jin kuma zan canza din.....saidai sultane daban yake a raina....dole damuwarsa dama komai nasa ya zama daban a raina......koda sahel couture a bayanshi take.......da girman qarfinki na amince kiyi abinda ya kamata na dan lokaci kafin komai ya daidaita". Shuru sukayi dukkaninsu,wani abu yana bugawa a tsakiyar qirji da zuciyar mammina.......ta tsuke idanunta daga inda take zaune,tunaninta kuma yana harbawa da nisa fiye da nisan dake tsakaninta da akhnan.
"Indai kina da uwa irina har abada ba zakiyi kuka ba.......ki dauki lokacinki.....kiyi amfani dashi har iya yadda kikeso.....mammina dinki zata kula miki da komai.....zata kuma ji miki da komai".
" Na gode" Ta furta da wata lanqwasashiyar murya,kuma bata qara cewa mammina din komai ba ta yanke kiran,ta ajiye wayar a gefanta ta zame tana kwanciya.
Da sauri yalwa ta miqa hannu ta karbi wayar daga hannunta tana duban yanayin fuskar uwar dakin nata. A nutse ta maida dubanta kan yalwa.
"A jikina ina jin akwai wani baqon abu......akwai wani abu na daban ba irin abu ba yau da kullum ba.......bansan me yake faruwa tsakanin sultane da akhnan ba......banga alamun komai tattare dashi ba,kamar yadda baiyi niyyar gayamin ba.....daren jiya mun kasance tsahon daren tare dashi muna hira......amma baicemin komai ba a kanta,bana buqatar tambayarsa komai,kaman yadda baiyi niyyar na sani ba......amma ina buqatar sanin komai din.....yalwa" Ta sake kiranta a karo na biyu.
"Allah ya taimakeki" Ta furta cikin girmamawa.
"Inason nasan meye wannan?......wanne laifi ne akhnan ke zaton ta yiwa sultane daya hanata nutsuwa......inason insan dalilin kiranta da sultane yayi zuwa agadez a satin nan". Kai yalwa ta jinjina sosai.
"An gama ranki ya dade......komai zai kasance a gabanki a bude". Yalwa ta furta cikin bata tabbaci,kamar yadda take da tabbacin a kanta.
"Sahel couture.......ina ganin kamar ya kamata a lura da kamfanin nan......sannan ayi amfani da dukka wata dama data samu a wannan taqin......wannan tsukin da kuma wannan lokacin.....lokaci ne me kyau daya dace a kula da sahel couture!" Ta qarashe da fadin sunan da wani harshe wani sauti daya tabbatarwa yalwa dukkana abinda ta fada tana nufin hakanne,abinda ya sanya yalwa komawa ta zauna sosai,tana bawa mammina hankalinta dama awannin rayuwarta gaba daya.
★★★★Ni'imtaccen qamshi ne me wani irin sanyi da laushi kawai ke fita daga ilahirin parlor din dama gidan gaba daya a safiyar ranar,daidai da qarfe sha daya na safe agogon qasar garin agadez dama niger gaba daya.
Su biyu ne rak zaune saman qawataccen dining din nasa da aka qawata da kalolin abincin da dan adam ka buqata kowacce safiya,wanda kusan komai da yake kai irin zabin abincinsa ne. Ba wani abinci da aka dafa me yawa,kowanne dan kadanne da bazai zama asara ba koda bai cinye gaba daya.
Wata sky blue din kurta ce a jikinsa me daukan idanu sosai,wadda aka yiwa adon zare a wuyanta da hannun rigar da wani kalar zare blue black. Iyakar tsahon rigar gwiwa sai wandonta da a wuyan qafan wandon shima aka yiwa ado da blue black din zaren.
Fuskarsa tayi wani fresh kaman yadda hasken qwayar idanunsa tayi wani irin tarwai. Sumarsa dake a kwance luf da wadda ke habarsa da kumatunsa sun sake fidda kwarjininsa sosai da kuma sigar kyansa.
Sosai yakejin zuciyarsa fresh......kaman yadda yanayin garin a safiyar farko da ya wayeta a qasar tayi masa,don wata iska me damshi damshi ke kadawa wadda ta sake tabbatarwa da kowanne me rai damina tana tafe,daminar da zata jiqa rayuka da tsirrai da sauran halittu da ni'imomi daga ubangijinsa.
Coffee ne a gabansa da aka zuba cikin wani qwataccen cup dake dauke da dan qaramin tray dinsa a qasa. Ba wai coffee din yake sha ko yake kallo ba,dukkan hankalinsa ya tattarasu ne akan malam Ousmane,yayin daya sanya coffee din a tsakiyar hannunwansa,ya zagayeshi yana soke yatsunsa a cikin na juna.
Bayanan malam Ousmane haris yake saurara,lokaci lokaci yana lumshe kyawawan idanunsa dake da brown din qwayar idanu wadda bata cika duhu ba sosai.
"Finally an samu hanyar shiga sultane palace......kuma wannan itace hanya guda daya da zaka zama ahalin masarautar,don muddin ka zama malami ga d'iyar sultane,suna mu'amalantarka ne tamkar d'ansu......musamman morsa safiyya.......tana da karrama dan adam sosai" Malam Ousmane ya qarasa fada cikin bawa haisan tabbaci.
Wata sassanyar ajiyar zuciya ya saki kana ya lumshe idanunsa ya kuma budesu duka lokaci guda akan Ousmane din.
"Akwai wani option dinne bayan wannan?" Ya furta a nutse,labbansa masu daukan hankali suna motsawa a hankali. Dan kadan malam Ousmane ya zuba masa idanu sannan ya girgiza kai yana cewa.
"A'ah" Can qasan ransa ya gama fahimtar abinda haisam ke nufi. Shigarsa gidan a mazaunin malami ne sam tsarin bai masa ba......to amma kuma ba wata hanyar da tafi haka sauqi.
"Kana da wata hanyar da tafi wannan ne sauqi?" Ousmane ya tambayi haisam din yana qoqarin tsareshi da ido. Kai kawai haisam ya girgiza ba tare daya dubi Ousmane din ba,yaja cup din coffee dinsa a nutse yana kurba gami da zubawa wani canister dake gabansa ido.
Kurba kusan biyar yayi,shuru yana sake ratsa wajen,Ousmane yayi qarfin halin ajiye ajiyar zuciya. Akwai buqatar ya fahimtar da haisam din,don wanann din wata dama ce babba a gurinsu,wucewarta kuma zai zaman kamar rasa gwaggwabar dama ne.
"Shiga agadez palace yana da muhimmancin haisam ka fahim......"
"......na fahimta Ousmane......." Ya katseshi yana mai bashi amsa. Can qasan zuciyarsa wani kishin tashi masarautar tana kamashi. Ba inda zaije a duniya sarautar jimma ta sauka daga jikinsa ko kuma zuciyarsa,wata sarauta ce da aka haifeta a asalin cikin jininsa,ta yaya zai iya rayuwa qarqashin wata sarautar?,qarqashin wani tsare tsaren da ba na mooti abba jifar ba?.
"Shiga gidan yana nufin sanin mutane da yawa dake rayuwa cikin gidan......mutanen dake rayuwa qarqashin kariya da alfarmar masarautar.......shiga gidan zai zama hanya mafi sauqi ta sanin mutane da dama da cudanya dasu........haka abun yake ba kuma laifi......amma zama malamin d'iyarsa da jikokinsa fa?.......banajin abune me yuwuwa". Haisam din ya fadi yana jin har cikin zuciyarsa abun be gamsheshi ba.
"Haka zaka shiga muhammad.......ka sanya a ranka daga yau kaine malami na gaba da zaici gaba da koyar da diyoyinsa........chapter closed,komai ya kammala.......fara gudanar aiki kawai muke jira,don duk wani jan qafa da zai biyo baya,tamkar qarin kwanakin da zakayine cikin aikin" Ya tsinci muryar bobbo muhammad dawud da baisan daga ina take ba. Sai daya daga qwayar idanunsa a nutse sannan ya lura video call ne Ousmane ya daga a wayarsa,fuskar abba muhammad dawud din kuwa ta fito tarwai a wayar,furfurar nan tasa dake nuna shekarunsa da kamalarsa dukka sun fita sosai.
Idanu suka hada da haisam din,sai ya jinjinawa haisam kai,ya kuma dunqule hannayensa dukka biyun cikin na juna yana jijjigawa. A hankali shima haisam din ya hada hannunsa hakan,wannan din wani salon alwashi ne da suke ciwa juna muddin zasu fara aiki me wahala da hatsari irin hakan,wani alqawari ne na cika aiki da suke yiwa junansu.
Daukewar kiran dif ya sanya haisam maida kallonsa kan Ousmane,suna hada ido ya saukar da nasa idon qasa yana fadin.
(08187255862 lu'u lu'u paying)
"Afuwa......bansan shine ya kira ba,bansan kuma na daga kiran kai tsaye ba,duk da already tun jiya mun gama maganar dashi,ya kuma tabbatar ba wata hanyar data wuce wannan......ko ina ya kamata bincikenmu yakai......muna da hadin kan hukumar tsaro har uku dake riqe da qasar nan" Kai haisam ya jinjina kawai baice komai ba,ya jawo wani kyakkyawan mazubi da ake zube dabino a ciki masu laushi da zaqi ya soma barewa,don dasu yakeson yasha tea din. Yana da zabi da madadi ashan sugar,mazarqwaila ko zuma ko dabino,sune abokan zaqinsa.
"Akwai yiwuwar sanar da shugaban qasarsu" Haisam ya fada kansa tsaye ba tare daya dubi Ousmane ba daya soma yin hanyar fita. Cak ya tsaya sannan ya dawo da baya da sauri.
"Amma akwai hatsari fa ayin hakan......" Dogayen yatsunsa ya daga masa alamun dakatarwa.
"Wannan kasadar tawa ce ba taku bace....idan ka fita ka turomin addisaleem". Wani yawu me tauri Ousmane ya hadiye. Yasan halin haisam din,kaifi daya ne......idan yace zaiyi ba abinda yake saukar dashi daga wannan bigiren. Ba lamari bane daya shafi addini ballantana ya jawo masa aya ko hadisin da sune kadai makaman dake iya saukeshi dama.......dabara ce da kuma fahimtarwa,ya kuma fuskanci bashi da buqatar wannan,sai kawai ya juya ya sauka yana kiran mass addisaleem kamar yadda ya buqata.
"Dukkan wadanda muka taho dasu daga addis ababa nakeso ka sanar musu,ina buqatar ganinsu nan da awa daya......ka saka abdii a ciki" Ya bawa addisaleem umarni kai tsaye.
"An gama" Ya fada yana rusunawa sannan ya juya yana fita a gaggauce.
Yana da kiyaye lokaci,yana kuma mutuntashi da martabashi qwarai. Idan shi yayi zabin lokaci don gudanar da wani abun,baya wuce adadin mintuna da awannin daya ware,idan shi aka bawa lokacin,zaiyi komai kaman yadda lokacin yace......idan abune kuma ya saka awa nawa zai dauka......baya shallake wadannan awannin yake qoqarin kammala komai.
Cikin kamala ya sauko zuwa dakin da ya gama wareshi a mazanin dakin da zai kasance wajen ganawarsa ta sirri da dukka wanda yakeso. Kaman yanzu dai da mutum shida harda abdii na bakwai suke jiransa.
*_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_*
*_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽
*Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu*
*muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA*
*Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah*
+20 114 341 0873 ko kuma
0810 959 7791
https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt
____________________________
"Har yanzu baki gama fuskantar matsayinki ba akhnan.......kinsan girman matsayinki da martabarki a qasar agadez?.......ina kikai jarumtarki?.....me yasa zaki bar qaramar damuwa ta mamayeki har haka?.....ba haka na sanki ba.....ba kuma haka nakeso naci gaba da ganinki ba" Ta furta cikin kambamata da kuma motsa mata matsayinta.
Idanunta ta lumshe ta kuma budesu a sarauce.
"Ina nan yadda nake mammina.....ban canza ba,bana jin kuma zan canza din.....saidai sultane daban yake a raina....dole damuwarsa dama komai nasa ya zama daban a raina......koda sahel couture a bayanshi take.......da girman qarfinki na amince kiyi abinda ya kamata na dan lokaci kafin komai ya daidaita". Shuru sukayi dukkaninsu,wani abu yana bugawa a tsakiyar qirji da zuciyar mammina.......ta tsuke idanunta daga inda take zaune,tunaninta kuma yana harbawa da nisa fiye da nisan dake tsakaninta da akhnan.
"Indai kina da uwa irina har abada ba zakiyi kuka ba.......ki dauki lokacinki.....kiyi amfani dashi har iya yadda kikeso.....mammina dinki zata kula miki da komai.....zata kuma ji miki da komai".
" Na gode" Ta furta da wata lanqwasashiyar murya,kuma bata qara cewa mammina din komai ba ta yanke kiran,ta ajiye wayar a gefanta ta zame tana kwanciya.
Da sauri yalwa ta miqa hannu ta karbi wayar daga hannunta tana duban yanayin fuskar uwar dakin nata. A nutse ta maida dubanta kan yalwa.
"A jikina ina jin akwai wani baqon abu......akwai wani abu na daban ba irin abu ba yau da kullum ba.......bansan me yake faruwa tsakanin sultane da akhnan ba......banga alamun komai tattare dashi ba,kamar yadda baiyi niyyar gayamin ba.....daren jiya mun kasance tsahon daren tare dashi muna hira......amma baicemin komai ba a kanta,bana buqatar tambayarsa komai,kaman yadda baiyi niyyar na sani ba......amma ina buqatar sanin komai din.....yalwa" Ta sake kiranta a karo na biyu.
"Allah ya taimakeki" Ta furta cikin girmamawa.
"Inason nasan meye wannan?......wanne laifi ne akhnan ke zaton ta yiwa sultane daya hanata nutsuwa......inason insan dalilin kiranta da sultane yayi zuwa agadez a satin nan". Kai yalwa ta jinjina sosai.
"An gama ranki ya dade......komai zai kasance a gabanki a bude". Yalwa ta furta cikin bata tabbaci,kamar yadda take da tabbacin a kanta.
"Sahel couture.......ina ganin kamar ya kamata a lura da kamfanin nan......sannan ayi amfani da dukka wata dama data samu a wannan taqin......wannan tsukin da kuma wannan lokacin.....lokaci ne me kyau daya dace a kula da sahel couture!" Ta qarashe da fadin sunan da wani harshe wani sauti daya tabbatarwa yalwa dukkana abinda ta fada tana nufin hakanne,abinda ya sanya yalwa komawa ta zauna sosai,tana bawa mammina hankalinta dama awannin rayuwarta gaba daya.
★★★★Ni'imtaccen qamshi ne me wani irin sanyi da laushi kawai ke fita daga ilahirin parlor din dama gidan gaba daya a safiyar ranar,daidai da qarfe sha daya na safe agogon qasar garin agadez dama niger gaba daya.
Su biyu ne rak zaune saman qawataccen dining din nasa da aka qawata da kalolin abincin da dan adam ka buqata kowacce safiya,wanda kusan komai da yake kai irin zabin abincinsa ne. Ba wani abinci da aka dafa me yawa,kowanne dan kadanne da bazai zama asara ba koda bai cinye gaba daya.
Wata sky blue din kurta ce a jikinsa me daukan idanu sosai,wadda aka yiwa adon zare a wuyanta da hannun rigar da wani kalar zare blue black. Iyakar tsahon rigar gwiwa sai wandonta da a wuyan qafan wandon shima aka yiwa ado da blue black din zaren.
Fuskarsa tayi wani fresh kaman yadda hasken qwayar idanunsa tayi wani irin tarwai. Sumarsa dake a kwance luf da wadda ke habarsa da kumatunsa sun sake fidda kwarjininsa sosai da kuma sigar kyansa.
Sosai yakejin zuciyarsa fresh......kaman yadda yanayin garin a safiyar farko da ya wayeta a qasar tayi masa,don wata iska me damshi damshi ke kadawa wadda ta sake tabbatarwa da kowanne me rai damina tana tafe,daminar da zata jiqa rayuka da tsirrai da sauran halittu da ni'imomi daga ubangijinsa.
Coffee ne a gabansa da aka zuba cikin wani qwataccen cup dake dauke da dan qaramin tray dinsa a qasa. Ba wai coffee din yake sha ko yake kallo ba,dukkan hankalinsa ya tattarasu ne akan malam Ousmane,yayin daya sanya coffee din a tsakiyar hannunwansa,ya zagayeshi yana soke yatsunsa a cikin na juna.
Bayanan malam Ousmane haris yake saurara,lokaci lokaci yana lumshe kyawawan idanunsa dake da brown din qwayar idanu wadda bata cika duhu ba sosai.
"Finally an samu hanyar shiga sultane palace......kuma wannan itace hanya guda daya da zaka zama ahalin masarautar,don muddin ka zama malami ga d'iyar sultane,suna mu'amalantarka ne tamkar d'ansu......musamman morsa safiyya.......tana da karrama dan adam sosai" Malam Ousmane ya qarasa fada cikin bawa haisan tabbaci.
Wata sassanyar ajiyar zuciya ya saki kana ya lumshe idanunsa ya kuma budesu duka lokaci guda akan Ousmane din.
"Akwai wani option dinne bayan wannan?" Ya furta a nutse,labbansa masu daukan hankali suna motsawa a hankali. Dan kadan malam Ousmane ya zuba masa idanu sannan ya girgiza kai yana cewa.
"A'ah" Can qasan ransa ya gama fahimtar abinda haisam ke nufi. Shigarsa gidan a mazaunin malami ne sam tsarin bai masa ba......to amma kuma ba wata hanyar da tafi haka sauqi.
"Kana da wata hanyar da tafi wannan ne sauqi?" Ousmane ya tambayi haisam din yana qoqarin tsareshi da ido. Kai kawai haisam ya girgiza ba tare daya dubi Ousmane din ba,yaja cup din coffee dinsa a nutse yana kurba gami da zubawa wani canister dake gabansa ido.
Kurba kusan biyar yayi,shuru yana sake ratsa wajen,Ousmane yayi qarfin halin ajiye ajiyar zuciya. Akwai buqatar ya fahimtar da haisam din,don wanann din wata dama ce babba a gurinsu,wucewarta kuma zai zaman kamar rasa gwaggwabar dama ne.
"Shiga agadez palace yana da muhimmancin haisam ka fahim......"
"......na fahimta Ousmane......." Ya katseshi yana mai bashi amsa. Can qasan zuciyarsa wani kishin tashi masarautar tana kamashi. Ba inda zaije a duniya sarautar jimma ta sauka daga jikinsa ko kuma zuciyarsa,wata sarauta ce da aka haifeta a asalin cikin jininsa,ta yaya zai iya rayuwa qarqashin wata sarautar?,qarqashin wani tsare tsaren da ba na mooti abba jifar ba?.
"Shiga gidan yana nufin sanin mutane da yawa dake rayuwa cikin gidan......mutanen dake rayuwa qarqashin kariya da alfarmar masarautar.......shiga gidan zai zama hanya mafi sauqi ta sanin mutane da dama da cudanya dasu........haka abun yake ba kuma laifi......amma zama malamin d'iyarsa da jikokinsa fa?.......banajin abune me yuwuwa". Haisam din ya fadi yana jin har cikin zuciyarsa abun be gamsheshi ba.
"Haka zaka shiga muhammad.......ka sanya a ranka daga yau kaine malami na gaba da zaici gaba da koyar da diyoyinsa........chapter closed,komai ya kammala.......fara gudanar aiki kawai muke jira,don duk wani jan qafa da zai biyo baya,tamkar qarin kwanakin da zakayine cikin aikin" Ya tsinci muryar bobbo muhammad dawud da baisan daga ina take ba. Sai daya daga qwayar idanunsa a nutse sannan ya lura video call ne Ousmane ya daga a wayarsa,fuskar abba muhammad dawud din kuwa ta fito tarwai a wayar,furfurar nan tasa dake nuna shekarunsa da kamalarsa dukka sun fita sosai.
Idanu suka hada da haisam din,sai ya jinjinawa haisam kai,ya kuma dunqule hannayensa dukka biyun cikin na juna yana jijjigawa. A hankali shima haisam din ya hada hannunsa hakan,wannan din wani salon alwashi ne da suke ciwa juna muddin zasu fara aiki me wahala da hatsari irin hakan,wani alqawari ne na cika aiki da suke yiwa junansu.
Daukewar kiran dif ya sanya haisam maida kallonsa kan Ousmane,suna hada ido ya saukar da nasa idon qasa yana fadin.
(08187255862 lu'u lu'u paying)
"Afuwa......bansan shine ya kira ba,bansan kuma na daga kiran kai tsaye ba,duk da already tun jiya mun gama maganar dashi,ya kuma tabbatar ba wata hanyar data wuce wannan......ko ina ya kamata bincikenmu yakai......muna da hadin kan hukumar tsaro har uku dake riqe da qasar nan" Kai haisam ya jinjina kawai baice komai ba,ya jawo wani kyakkyawan mazubi da ake zube dabino a ciki masu laushi da zaqi ya soma barewa,don dasu yakeson yasha tea din. Yana da zabi da madadi ashan sugar,mazarqwaila ko zuma ko dabino,sune abokan zaqinsa.
"Akwai yiwuwar sanar da shugaban qasarsu" Haisam ya fada kansa tsaye ba tare daya dubi Ousmane ba daya soma yin hanyar fita. Cak ya tsaya sannan ya dawo da baya da sauri.
"Amma akwai hatsari fa ayin hakan......" Dogayen yatsunsa ya daga masa alamun dakatarwa.
"Wannan kasadar tawa ce ba taku bace....idan ka fita ka turomin addisaleem". Wani yawu me tauri Ousmane ya hadiye. Yasan halin haisam din,kaifi daya ne......idan yace zaiyi ba abinda yake saukar dashi daga wannan bigiren. Ba lamari bane daya shafi addini ballantana ya jawo masa aya ko hadisin da sune kadai makaman dake iya saukeshi dama.......dabara ce da kuma fahimtarwa,ya kuma fuskanci bashi da buqatar wannan,sai kawai ya juya ya sauka yana kiran mass addisaleem kamar yadda ya buqata.
"Dukkan wadanda muka taho dasu daga addis ababa nakeso ka sanar musu,ina buqatar ganinsu nan da awa daya......ka saka abdii a ciki" Ya bawa addisaleem umarni kai tsaye.
"An gama" Ya fada yana rusunawa sannan ya juya yana fita a gaggauce.
Yana da kiyaye lokaci,yana kuma mutuntashi da martabashi qwarai. Idan shi yayi zabin lokaci don gudanar da wani abun,baya wuce adadin mintuna da awannin daya ware,idan shi aka bawa lokacin,zaiyi komai kaman yadda lokacin yace......idan abune kuma ya saka awa nawa zai dauka......baya shallake wadannan awannin yake qoqarin kammala komai.
Cikin kamala ya sauko zuwa dakin da ya gama wareshi a mazanin dakin da zai kasance wajen ganawarsa ta sirri da dukka wanda yakeso. Kaman yanzu dai da mutum shida harda abdii na bakwai suke jiransa.