Sashe 10
Luu Luu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikakken ba'abzine ma'abocin tsaho da qibar da za'a iya kiranta da sunan murjewar jiki kawai. Sanye da jallabiyya 'yar qasar Morocco wadda tadansha banbam da sauran jallabiyya da aka saba gani,saboda bayan zubin dinkin morocco da akayi mata,kana dubanta zakasan farashinta na musamman ne saboda qasaitattun mutane irin me martana sultane muhammad hammud din.
Shigowarta bai sanyashi ya fasa shimfida lausassar fara dardumarshi ba,duk da hakan bai hanashi ganin tasirin fushin data shigo dashi ba.
Wani lokacin yana ganin SAFEENA a tare da ita........saidai ba safeenan bace. Akwai tarin abubuwa da banbamce bambance daya saka tazara ya kuma shata layi tsakaninta da safeena din. Yayin da wasu gamayyar halaye da jini kar d'arsa tsakanin mutanen da JINI ya zama sanadiyyar amsa sunan DAN UWA yake haifarwa. A qasaice ta samu kanta da takawa,tana kuma sake tsuke fuskarta wajen qoqarin bayyanar da dukka fushinta. A wannan lokacin a wannan karon bata jin zata iya......bata jin zata iya kauda fuska tayi kamar komai faru ba......batajin zata qaryata feelings dinta da abinda ke tasowa tun daga qasan maqoshint har zuwa saman harshenta.
"Barka da yammaci" Ta furta muryarta a cushe guri daya.
Da zuzzurfan kallon nan nasa ya bita,kallon da tabbas ta jishi har cikin jininta,to amma ba zata yarda ta kallo kwarjantattun qwayar idanun nan nasa dake hana mutum duk wani motsi da yayi niyya ko ya kamata yayi ba.
Muryar safeena ce..........amma safiyya ce tayi magana.......kamannin safeena ne amma kuma dabi'un na safiyya ne........safiyyan ce dai,da wannan sautin da wannan fusataccen yanayin nata daya tabbatar ba zaa kwashe lafiya ba a duk sanda ta shigo dashi. A nutse yake qare mata kallo,yana son tuna kwanakin daya dauka bai sanyata cikin idanunshi ba.
"Barkanki......kina lafiya?".
"Magana nazo muyi dakai" Ta fadi kanta tsaye ba tare data tsaya damuwa da amsa tambayar lafiyarta da yayi ba,hannuwanta kuma goye a qirjinta,yayin data kauda kanta wani sashe na daban ba tare data yarda ta kalleshi ba.
Kai ya jinjina,ta iya rigima da gasken gaske,irin rigimar da idan ta farata sai abinda hali yayi. Wata irin birkitacciya ce ita idan bataso ba,birkicewar da shi kansa a wasu lokutan yake kasa gaza shawo kanta.
"Allah yasa maganarki bata shafi khadeejatu ba?" Ya furta maganae da qwarin gwiwar da fushinta bai karya shi ko kassarashi ba ko kadan.
Har batasan sanda ta sauke hannayenta da sauri ba ta kuma maida fuskarta zuwa sashen da yake........yanayin sautinsa kawai ya tabbatar mata da gaske indai akan khadeejatu ne ba wani magana da zata tasirantu a ransa?.....kamar ma launin sautin nasa yana gaya mata tabar batun kan khadeeja karta sakoshi.
"Saboda idan a kanta ne baka da lokacin da zaka saurari safiyya?......saboda idan a kanta ne baka da sauran wani qwarin gwiwar jagoranci?" Tayi masa tambayoyin a jere tana zube masa kyawawan idanuwan nan nata da shekaru basuyi nasarar jirkitasu ba sam,idanun da yake hango tsantsar kamanninsu dana biftu dinsa(akhnan),idanun da sau tari kallon cikinsu suke sanyashi dagewa morsa safiyya qafa,saboda akwai wasu tarin kamanni masu daraja a cikinsu.
Qaramar cushion chair dake daura dashi me wani irin yanayi dake nuna alfarmarta ya jawo ya zauna akai cike da wani irin tarin nutsuwa,ya sake zuba mata dukka idanunsa yana kallon ta na wasu daqiqu kafin yace.
"Ba duka abinda kika lissafa bane.........ina nufin hakanne kawai don har yanzu ba wani abu guda daya da khadeejatu tayi wanda ya sabawa addini".
"Al'ada fa?" Ta sake tambayarsa a zafafe,duk da yadda idanunsa ke mata kwarjini sukeson dakusar da kaifin fushinta.
Sake tsareta yayi da kallo kafin ya dage kafadunsa biyu.
"Har a al'adar ma banajin ba daidai bane"
"Koda gudun aure ne?,da kore duk namijin da yazo da buqatar aurenta komai cancantarsa?" Tayi maganar a karo na biyu cike da qwarin gwiwar jin ta riqi hujjar da a yau zata dankwafar da duk wani dalili da sultane ke iya bayarwa don samarwa da akhnan din kariya.
Dif din da yayi da yadda yaci gaba da kallonta kawai ba tare da yace komai ba ya soma bata hope........ya soma bata fata akan sultane,ya kuma soma bata yaqinin a wannan karon saita balla wannan shingen.......wannan iyakar don gano ainihin meye a shirye a bayanta?.
Ga mamakinta murmushi sultane ya saki yana dan lumshe manyan idanunshi da akhnan tayi gado,ya dora hannunsa ya shafi tattausar sumarsa ta asalin abzinawa sannan ya maida bayansa ya jinginar da kujerar.
"Shin musulunci ya haramta bawa diya mace daman zabar miji ne?.......ko ya haramta zabar mijin da zaiyi daidai da daraja da martabar mace?".
Sak tayi kawai tana dubanshi.......wani bacin rai sabo yana sake taso mata gami da qara ninkuwa a ranta.
To ta ina sultane muhammad hammud ya cika sarki.......gwarzo kuma jarumi me wata irin madaukakiyar daraja a suna kawai bare akai ga nagarta........amma tabbas a nan FADUWARSA take........tarannan da akace dan adam yake bai cika goma ba.......anan tashi rashin cikar take.
Zuciya dama gangar jikinta gaba daya sukayi rauni. Yana kima ta miji a gurinta......yana da martaba ta shugaba a cikin qasarsa......yana da daraja ta shekaru daya bata. Dukka wadannan suna bidar gurbinsu a gurinta......dukkansu suna bidar muhallinsu a dukka kalamai da aikinta......amma kuma hakan yana nufin tayi shuru ta bari ayita yin abinda take jin ba daidai bane?. Hakan na nufin ta zuba idanu BAKI yana yawa akan abinda tayi imani shi kadai zai fita kusa dashi?,hakan yana nufin ta bada dama komai yaci gaba da wanzuwa a bahaguwar hanya?. Kowa ma yasan ba daidai bane ga WANDA yasan daidai.....wake da qarfin gyarawa cikin wadanda ke hangen rashin daidai din SAMA DA ITA?.
"Wannan shine alqawarin?......wannan shine tabbacin.....wannan shine alwashin......wannan shine cika buri wa gawar SAFEENA?" ta fada da wata irin murya data daki sultane a tsakiyar kansa.
"Hasbunallahu wani'imal wakeel" Ya furta yana watsa yatsuntsa saman fuskarsa kamar wanda ke gudun ganin wani abu.
"Safiyya!" Ya kira sunanta da wani irin yanayi yana sauke hannunsa daga saman fuskarsa. Duban da yayi mata daya ta karanci launin idanunsa dana fuskarsa ya sauya........hakan takeso,ta taba wani guri dake zuciyarsa........ko hakan zai sanya yayi abinda ya dace?.
"Me kikeso?" Ya sake tambayarta kai tsaye.
"Ka kira biftu.......kayi mata fada irin fadan da kowanne uba zai yiwa 'yarsa.......ka datse wannan halayyar.........ka kawo qarshen wannan wasan,Coupe le jeu.......ka tsaida wasan da takeyi da rayuwarta dama dukka damarmakinta.......wasan da nayi imani da yaqinin wulwulata akayi a tsakiyarsa ba tare data ankare ba.......ban yarda da zaitun ba......bazan taba kuma amint......." Da sauri ya daga mata hannu
"Ça suffit!(ya isa!)" Tsaf ta tsareshi da kallonta......ba abinda ya kawo wannan dakatarwar ta gaggawa sai kiran sunan mammina a ciki da tayi.
"Kada ki dauki zunubi......kada ki dauki alhaki akan abinda baki da hujja......me kikeso?" Yayi maganar muryarsa na sanyaya,sam ba zakace sarki muhammad hammud dinnan bane me yawa kwarjini.
*_AKHNAN_*
A hankali mammina ta bude baki da zummar sake magana,amma taba qofar parlor din data kasance ta glass ta katseta. Dukkaninsu suka maida dubansu ga qofar,kafin muryar barra'u ta ratso ta tsakanin curtains din.
"Ayimin afuwa ranki ya dade keda gimbiya......" Duk da barra'u ta katse musu magangunu masu muhimmanci da sukeyi,amma saita saita muryar ta da yanayinta tace mata.
"Fadi abinda yake tafe dake".
"Me martaba sultane ne yake son Gimbiya yanzu yanzu a shiyyarsa". Ba mammina ba.....hatta da akhnan maganar ta bata mamaki.
Abune me wahala sultane yayi aike takanas a irin wannan lokacin......ya buqaci ganin akhnan,ganin ma kuma ita kadai?,duk da suna kebewa sosai a lokutta da dama suyi hira irin na tsakanin 'ya da uba,amma yanayin wannan kiran yasha banban da kowanne. Kai mammina ta gyada.
"Saqonsa ya iso,tana tafe" Ta amsawa barra'u wadda amsar mammina ta sakata matsawa tabar gurin.
Dubanta ta maido kan akhnan,wadda ta jima tana kallon mammina kamar tana neman sanin dalilin kiran da sultane din yake musu ta saman fuskarta.
"Anya ba wani abu matar can taje ta gayawa sultane ba?" Akhnan tayi maganar da wani yanayi da zai tabbatar maka jikinta ya bata akwai wani abu daya faru.
"Ita din uwa take a wajenki.....kada ki munana mata zato.....tashi ki amsa kiran sultane". Kai akhnan ta shiga girgizawa.
"Babu inda zani saida ke mammina........banajin qwarin gwiwar tunkarar sultane a yau ni kadai".
Duk yadda taso ta kwatantawa akhnan bata fahimta din ba,har sai data aminta suka miqe tare akhnan din na riqe da yatsun mammina cikin nata.
Cikin qasa da second biyu yanayin fuskarta ya sauya yana sake gauraya da wani irin bacin rai. A kowanne motsi kuma a kowanne taku mammina ba zata taba qyale biftu ba?.....a kowanne taqi na rayuwa ba zata taba barin komai nata ya wanzu shi kadai ba?. Wannan kawai ya isa ya bata amsar cewa.......rayuwar biftu din tana cikin wata da'ira ne da ake sarrafa mata ita ga zaton ita ke sarrafa kayarta.
Morsa safiyya itace mutum ta farko da idanun akhnan suka sauka a kanta. Ta janye blue eyes dinta da bacin rai ya sanya suka sake shanyewa tana maida dubanta ga sultane dake zaune saman lallausar dardumarsa yana jan carbi.
Tasha kwatanta inama ace morsa safiyyan wata mutum ce ta daban,ba irin mutanen da ko yaushe mammina da sultane ke jaddada mata girman kowanne lamari daya shafeta bane?......ba shakka da hakan zata kasance sunanta shine a sahun farko cikin jerin sunayen mutanen da zata furzar dasu daga rayuwarta.
Daidai da bugawar daqiqa guda......wannan dangantakar ta UWA da aketa kiranta tsakaninta da morsa safiyya bata taba jinta ba,hasalima inda zatace wani qin jininta takeji sosai yana disa saman zuciyarta a kowanne motsi to batayi qarya ba.
Tamkar bata ganta zaune a wajen ba,ta taka cikin wata irin nutsuwa da izzar sarautar dake yawo a jininta ta sanya ta zauna mata,take kuma qara mata kyau da haiba matuqa,ta qarasa gaban sultane a nutse ta sulale tana duqawa saman qafafunta.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
Shigowarta bai sanyashi ya fasa shimfida lausassar fara dardumarshi ba,duk da hakan bai hanashi ganin tasirin fushin data shigo dashi ba.
Wani lokacin yana ganin SAFEENA a tare da ita........saidai ba safeenan bace. Akwai tarin abubuwa da banbamce bambance daya saka tazara ya kuma shata layi tsakaninta da safeena din. Yayin da wasu gamayyar halaye da jini kar d'arsa tsakanin mutanen da JINI ya zama sanadiyyar amsa sunan DAN UWA yake haifarwa. A qasaice ta samu kanta da takawa,tana kuma sake tsuke fuskarta wajen qoqarin bayyanar da dukka fushinta. A wannan lokacin a wannan karon bata jin zata iya......bata jin zata iya kauda fuska tayi kamar komai faru ba......batajin zata qaryata feelings dinta da abinda ke tasowa tun daga qasan maqoshint har zuwa saman harshenta.
"Barka da yammaci" Ta furta muryarta a cushe guri daya.
Da zuzzurfan kallon nan nasa ya bita,kallon da tabbas ta jishi har cikin jininta,to amma ba zata yarda ta kallo kwarjantattun qwayar idanun nan nasa dake hana mutum duk wani motsi da yayi niyya ko ya kamata yayi ba.
Muryar safeena ce..........amma safiyya ce tayi magana.......kamannin safeena ne amma kuma dabi'un na safiyya ne........safiyyan ce dai,da wannan sautin da wannan fusataccen yanayin nata daya tabbatar ba zaa kwashe lafiya ba a duk sanda ta shigo dashi. A nutse yake qare mata kallo,yana son tuna kwanakin daya dauka bai sanyata cikin idanunshi ba.
"Barkanki......kina lafiya?".
"Magana nazo muyi dakai" Ta fadi kanta tsaye ba tare data tsaya damuwa da amsa tambayar lafiyarta da yayi ba,hannuwanta kuma goye a qirjinta,yayin data kauda kanta wani sashe na daban ba tare data yarda ta kalleshi ba.
Kai ya jinjina,ta iya rigima da gasken gaske,irin rigimar da idan ta farata sai abinda hali yayi. Wata irin birkitacciya ce ita idan bataso ba,birkicewar da shi kansa a wasu lokutan yake kasa gaza shawo kanta.
"Allah yasa maganarki bata shafi khadeejatu ba?" Ya furta maganae da qwarin gwiwar da fushinta bai karya shi ko kassarashi ba ko kadan.
Har batasan sanda ta sauke hannayenta da sauri ba ta kuma maida fuskarta zuwa sashen da yake........yanayin sautinsa kawai ya tabbatar mata da gaske indai akan khadeejatu ne ba wani magana da zata tasirantu a ransa?.....kamar ma launin sautin nasa yana gaya mata tabar batun kan khadeeja karta sakoshi.
"Saboda idan a kanta ne baka da lokacin da zaka saurari safiyya?......saboda idan a kanta ne baka da sauran wani qwarin gwiwar jagoranci?" Tayi masa tambayoyin a jere tana zube masa kyawawan idanuwan nan nata da shekaru basuyi nasarar jirkitasu ba sam,idanun da yake hango tsantsar kamanninsu dana biftu dinsa(akhnan),idanun da sau tari kallon cikinsu suke sanyashi dagewa morsa safiyya qafa,saboda akwai wasu tarin kamanni masu daraja a cikinsu.
Qaramar cushion chair dake daura dashi me wani irin yanayi dake nuna alfarmarta ya jawo ya zauna akai cike da wani irin tarin nutsuwa,ya sake zuba mata dukka idanunsa yana kallon ta na wasu daqiqu kafin yace.
"Ba duka abinda kika lissafa bane.........ina nufin hakanne kawai don har yanzu ba wani abu guda daya da khadeejatu tayi wanda ya sabawa addini".
"Al'ada fa?" Ta sake tambayarsa a zafafe,duk da yadda idanunsa ke mata kwarjini sukeson dakusar da kaifin fushinta.
Sake tsareta yayi da kallo kafin ya dage kafadunsa biyu.
"Har a al'adar ma banajin ba daidai bane"
"Koda gudun aure ne?,da kore duk namijin da yazo da buqatar aurenta komai cancantarsa?" Tayi maganar a karo na biyu cike da qwarin gwiwar jin ta riqi hujjar da a yau zata dankwafar da duk wani dalili da sultane ke iya bayarwa don samarwa da akhnan din kariya.
Dif din da yayi da yadda yaci gaba da kallonta kawai ba tare da yace komai ba ya soma bata hope........ya soma bata fata akan sultane,ya kuma soma bata yaqinin a wannan karon saita balla wannan shingen.......wannan iyakar don gano ainihin meye a shirye a bayanta?.
Ga mamakinta murmushi sultane ya saki yana dan lumshe manyan idanunshi da akhnan tayi gado,ya dora hannunsa ya shafi tattausar sumarsa ta asalin abzinawa sannan ya maida bayansa ya jinginar da kujerar.
"Shin musulunci ya haramta bawa diya mace daman zabar miji ne?.......ko ya haramta zabar mijin da zaiyi daidai da daraja da martabar mace?".
Sak tayi kawai tana dubanshi.......wani bacin rai sabo yana sake taso mata gami da qara ninkuwa a ranta.
To ta ina sultane muhammad hammud ya cika sarki.......gwarzo kuma jarumi me wata irin madaukakiyar daraja a suna kawai bare akai ga nagarta........amma tabbas a nan FADUWARSA take........tarannan da akace dan adam yake bai cika goma ba.......anan tashi rashin cikar take.
Zuciya dama gangar jikinta gaba daya sukayi rauni. Yana kima ta miji a gurinta......yana da martaba ta shugaba a cikin qasarsa......yana da daraja ta shekaru daya bata. Dukka wadannan suna bidar gurbinsu a gurinta......dukkansu suna bidar muhallinsu a dukka kalamai da aikinta......amma kuma hakan yana nufin tayi shuru ta bari ayita yin abinda take jin ba daidai bane?. Hakan na nufin ta zuba idanu BAKI yana yawa akan abinda tayi imani shi kadai zai fita kusa dashi?,hakan yana nufin ta bada dama komai yaci gaba da wanzuwa a bahaguwar hanya?. Kowa ma yasan ba daidai bane ga WANDA yasan daidai.....wake da qarfin gyarawa cikin wadanda ke hangen rashin daidai din SAMA DA ITA?.
"Wannan shine alqawarin?......wannan shine tabbacin.....wannan shine alwashin......wannan shine cika buri wa gawar SAFEENA?" ta fada da wata irin murya data daki sultane a tsakiyar kansa.
"Hasbunallahu wani'imal wakeel" Ya furta yana watsa yatsuntsa saman fuskarsa kamar wanda ke gudun ganin wani abu.
"Safiyya!" Ya kira sunanta da wani irin yanayi yana sauke hannunsa daga saman fuskarsa. Duban da yayi mata daya ta karanci launin idanunsa dana fuskarsa ya sauya........hakan takeso,ta taba wani guri dake zuciyarsa........ko hakan zai sanya yayi abinda ya dace?.
"Me kikeso?" Ya sake tambayarta kai tsaye.
"Ka kira biftu.......kayi mata fada irin fadan da kowanne uba zai yiwa 'yarsa.......ka datse wannan halayyar.........ka kawo qarshen wannan wasan,Coupe le jeu.......ka tsaida wasan da takeyi da rayuwarta dama dukka damarmakinta.......wasan da nayi imani da yaqinin wulwulata akayi a tsakiyarsa ba tare data ankare ba.......ban yarda da zaitun ba......bazan taba kuma amint......." Da sauri ya daga mata hannu
"Ça suffit!(ya isa!)" Tsaf ta tsareshi da kallonta......ba abinda ya kawo wannan dakatarwar ta gaggawa sai kiran sunan mammina a ciki da tayi.
"Kada ki dauki zunubi......kada ki dauki alhaki akan abinda baki da hujja......me kikeso?" Yayi maganar muryarsa na sanyaya,sam ba zakace sarki muhammad hammud dinnan bane me yawa kwarjini.
*_AKHNAN_*
A hankali mammina ta bude baki da zummar sake magana,amma taba qofar parlor din data kasance ta glass ta katseta. Dukkaninsu suka maida dubansu ga qofar,kafin muryar barra'u ta ratso ta tsakanin curtains din.
"Ayimin afuwa ranki ya dade keda gimbiya......" Duk da barra'u ta katse musu magangunu masu muhimmanci da sukeyi,amma saita saita muryar ta da yanayinta tace mata.
"Fadi abinda yake tafe dake".
"Me martaba sultane ne yake son Gimbiya yanzu yanzu a shiyyarsa". Ba mammina ba.....hatta da akhnan maganar ta bata mamaki.
Abune me wahala sultane yayi aike takanas a irin wannan lokacin......ya buqaci ganin akhnan,ganin ma kuma ita kadai?,duk da suna kebewa sosai a lokutta da dama suyi hira irin na tsakanin 'ya da uba,amma yanayin wannan kiran yasha banban da kowanne. Kai mammina ta gyada.
"Saqonsa ya iso,tana tafe" Ta amsawa barra'u wadda amsar mammina ta sakata matsawa tabar gurin.
Dubanta ta maido kan akhnan,wadda ta jima tana kallon mammina kamar tana neman sanin dalilin kiran da sultane din yake musu ta saman fuskarta.
"Anya ba wani abu matar can taje ta gayawa sultane ba?" Akhnan tayi maganar da wani yanayi da zai tabbatar maka jikinta ya bata akwai wani abu daya faru.
"Ita din uwa take a wajenki.....kada ki munana mata zato.....tashi ki amsa kiran sultane". Kai akhnan ta shiga girgizawa.
"Babu inda zani saida ke mammina........banajin qwarin gwiwar tunkarar sultane a yau ni kadai".
Duk yadda taso ta kwatantawa akhnan bata fahimta din ba,har sai data aminta suka miqe tare akhnan din na riqe da yatsun mammina cikin nata.
Cikin qasa da second biyu yanayin fuskarta ya sauya yana sake gauraya da wani irin bacin rai. A kowanne motsi kuma a kowanne taku mammina ba zata taba qyale biftu ba?.....a kowanne taqi na rayuwa ba zata taba barin komai nata ya wanzu shi kadai ba?. Wannan kawai ya isa ya bata amsar cewa.......rayuwar biftu din tana cikin wata da'ira ne da ake sarrafa mata ita ga zaton ita ke sarrafa kayarta.
Morsa safiyya itace mutum ta farko da idanun akhnan suka sauka a kanta. Ta janye blue eyes dinta da bacin rai ya sanya suka sake shanyewa tana maida dubanta ga sultane dake zaune saman lallausar dardumarsa yana jan carbi.
Tasha kwatanta inama ace morsa safiyyan wata mutum ce ta daban,ba irin mutanen da ko yaushe mammina da sultane ke jaddada mata girman kowanne lamari daya shafeta bane?......ba shakka da hakan zata kasance sunanta shine a sahun farko cikin jerin sunayen mutanen da zata furzar dasu daga rayuwarta.
Daidai da bugawar daqiqa guda......wannan dangantakar ta UWA da aketa kiranta tsakaninta da morsa safiyya bata taba jinta ba,hasalima inda zatace wani qin jininta takeji sosai yana disa saman zuciyarta a kowanne motsi to batayi qarya ba.
Tamkar bata ganta zaune a wajen ba,ta taka cikin wata irin nutsuwa da izzar sarautar dake yawo a jininta ta sanya ta zauna mata,take kuma qara mata kyau da haiba matuqa,ta qarasa gaban sultane a nutse ta sulale tana duqawa saman qafafunta.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*