Sashe 41
Luu Luu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana jin a yau kamar ya barar da dukka wani wadannan darajoji da kima tata da wadannan laifukan guda biyu da yayi mata. Ta yaya zata barshi yaci bulus?,ya kamata ta bincika tasan koshi waye.......ya kamata ta fara hukuntashi ta kunyatashi ta hanyar bashi kayi kaman yadda yayi mata a gaban idanun mutane......kafin kuma tasa a masa mafi munin hukunci a bayan idanun kowa......a nesantashi da qasar da take rayuwa a cikinta.
Abinda ke ranta yaqi wuce mata bare ta samu ta huta,har zuwa sanda ta zare kayan jikinta tsaf da takeji ta tsanesu ta bada umarnin a fita dasu,kada a sake dawo mata dasu cikin gidan,koda gilmawarsu bata qaunar ta sake gani,ta wuce zuwa bathroom dinta da yafi kama da wani parlor din alfarmar,ta wuce cikin jacuzzi ta sakarwa kanta ruwa me bala'in dumin da kadan ya rage yayi zafi sosai.
Batasan adadin awannin data dauka cikin ruwan ba yana saukar mata tsakiyar kanta ba. Idanunta kan ruwan dake gudu ta rariyar,tana jin inama wannan ranar ta wuce da dukka wani memory na dukka al'ummar da suke wajen abun ya faru?,inama ace zata iya shafe komai ta mantar da kowa komai ya wuce tamkar bai faru a ranar ba?.
Dukka hannuwanta ta saka tana maida jiqaqqiyar sumarta baya,wadda ta lafe saman farar fatarta tsahonta yana kaiwa dab da mazaunanta. Iska ta furzar daga bakinta ta cikin ruwan,tana tuna yadda ya tureta daga jikinsa ya kuma direta saman qafafunta.
Batasan sanda hawaye ya balle mata ba,kamar ita?......diya guda ga sultane.......akhnan muhammad?......har wani ya samu damar kusanci da jikinta?......har yana jin ta zame masa damuwar da zai tureta har haka?.
Wata mahaukaciyar tsanarsa ta taso mata......ta kuma yi mata tsaye a zuciyarta ta sakata sakin kuka sosai cikin ruwan.
Dama can ya shirya komai ne......dama can ya shirya faruwar hakan......banda haka ta yaya tana zaman zamanta yayi requesting yayi tsere da ita?,ita daya tallin tal!....duk tarin 'yan wasan da Niamey dama niger gaba daya take dasu?.
Batasan ta dauki lokaci me tsaho a bandakin ba sai da taji Shehinaz na knocking qofar daga waje,ta ciri wani siririn band ta daure gashinta sannan ta fito ta sabe jikinta ta koma cikin bathtub ta qarasa wankan.
Sanda ta fito da aisa da Shehinaz dukkaninsu suna zaune a mabanbantan gurare cikin dakin. Kowacce waya ce a hannunta,ba wannan hirar ba kuma karadin.
Da kanta ta sake yiwa kanta alqalanci.......tunda har a yau takejin nauyi da wani irin rashin dadi cikin ranta tsakaninta dasu aisa.....su aisa din da kafin mallakar hankulansu hatta da wanda suna iya shiga bandaki daya kat kenan......amma a yau takejin nauyin kallon idanunsa?.
Cikin dukkanin jikinta gaba daya take jin ta muzanta......cikin kowanne motsawa da zatayi ji take kaman aisa da Shehinaz suna kallonta ne......kamar suna mata kallon marar sa'a!......mara nasara!......
Da wannan tunanin ta sauya kayan da birra ta ajiye mata. Lumshe ido tayi tana shaqar wani qamshi na daban da taji yau kayan sukeyi. Lallausan qamshin nan na musamman daga turaren incense by kabo daughter(+234 803 211 9803 tasted and trusted).
Kawai aisa ta gwada yi mata kabbasar kayanne......sanin kyakkyawar alaqa da soyayyarta da qamshi,wataqila hakan zai sanyaya mata zuciyarta.
Ta samu nutsuwa sosai cikin sallarta,kamar yadda qamshin ya huda zuciyarta sosai ya soma rage radadin da takeji. Saidai sanda ta kammala sallar komawa tayi ta lafe cikin sofa tana nannade jikinta da kyau cikin after dress din me yalwa da tayi sallar da ita,ta kuma maida idonta ta rufe ruf ba tare da tace da kowa komai ba,tana shaqar lallausan qamshin kabbasar a hankali tana tattaro nutsuwarta.
Ganin haka ya sanya aisa qyarawa Shehinaz,sai kawai suka miqe a nutse suna ficewa a dakin gami da ja mata qofar kowa baice komai da ita ba.
★★ *HAISAM*★★
Daga yadda shirunsa ya kasance tun bayan sallama da yayi dasu khadeem bayan ya jagorancesu sallar magariba sannan sukayi sallama suka wuce filin sauka da tashi jiragen sama na Niamey din omari ya gama sanin an samu matsala.
Daga yanayin idanunsa kadai omari ya fahimci ranshi a tsananin bace yake,wani irin mutum ne shi da sam ba kasafai ya fiya magana ba koda ba cikin fushi yake ba ballantana yana cikin fushi. Yayi riqo sosai da hadith dinnan na ma'aiki S A W da yayi hani da magana cikin fushi,idan kana tsaye kuma ka zauna. Zai iya qayyade sau nawa ya taba ganinsa yana magana alhalin cikin fushi yake?.
A karo na barkatai omari ya sake dubansa. Ya sauya kayansa zuwa wasu Indonesian kurta farare tas masu laushi,wadanda aka yiwa ado da gray color din zare. Kanshi ba hula sai tattausan gashinsa dake a gyare tsaf.....kai bakace shine wannan da yayi tsere awa biyu baya da suka wuce ba.
Jikinsa da lallausan turaren nan nasa ya zaunawa qamshinsa ne yake fita a hankali da wani irin sanyi me kwantar da rai. Dan qaramin littafi ne a hannunsa da tunda suka zauna a motar shi yake dubawa shafi shafi.
Wannan din na cikin dabi'arsa ta biyu. Indai ranshi yana a bace ba abinda yake bashi peace da relief sai karatu. Yana iya gamawa da littafi guda idan yana cikin fushin da baison a matsa masa yayi magana duk yawan mas hafin littafin.
Yaso qwarai kada yace masa komai kamar yadda aikinsa ya nuna buqatarsa kenan,to amma kuma ya gaji da canki cankin ganin sun dauki hanya d'od'ar,su da suke da ticket na jirgin da zai sauka agadez qarfe bakwai da rabi na safiyar washegari. Bugu da qari driver din dake tuqasu a yanzu dan qasar ne,ba baqo bane irinsu ballantana yayi tunanin bace hanya yayi.
"Amma fa.....kamar awa guda kawai ya ragewa jirginmu ya tashi.....kuma naga mp din yana nuna mun dauki hanyar barin Niamey ne". Omari ya furta a nutse kaman bashi ba. Sau tari fushin haisam baya bayyana muraran,amma su suna kalla suke ganewa. Dukkaninsu suna shiga wani sabon hankali da sabuwar nutsuwar idan ran haisam ya baci,bawai don zai gaya musu maganganu marasa dadi,ko zaiyi fada da dayansu ba....aah.....sai don nauyinsa da sukeji da wani irin kwarjini da nutsuwa da Allah ya bashi. Zai qalubalanceka ne idan buqatar hakan ta kama da wani irin nutsuwa da hikima a kalamansa......zai kuma dafaka da ruwan jikinka idan baikai yace komai da kai ba.
Ba tare daya dauke littafin a fuskarsa ba ko ya dubi omari ba ya amsa masa.
"Buqatar tafiya a motar tafi ta tafiya a flight muhimmanci" Ya amsa a taqaice yana buda shafin gaba na littafinsa.
Shuru omari yayi yana sake zuba masa idanu. Wato halin zai gwada masa a aikace?.....shikam baya jurar wannan,bazai bari bama su shiga garin mutane da basusan komai nasu ba da wannan halin da haisam ya yanke nuna masa.
"Amma dukka wannan shariyar ta mece?,da magana a cikinka mafi kyau ka fito ka fadeta" Omari ya fada cikin nashi kalar iya rigimar yana hade rai da bata fuska kaman shi akawa laifin.
Bai kalleshi ba,amma yadda yayi maganar kadai haisam yasan me yake shirin yi,don haka yayi kaman baiji me yake cewa ba.
Bai magantun ba kuwa har sai da omari ya fidda rai zaice wani abu din,sannan ya rufe littafin a nutse bayan ya saka alama ya ajjiyeshi daga gefansa.
"Me kakeso nace maka omari?.......ince maka ka kyauta daka hadani tsere da wadda take ba muharramata ba?......ko ince maka kyauta daga sakani hada jiki da matar da take haramun nayi mata koda zuzzurfan kallo ballanta jikkunanmu su hadu?.....ko kuma nace maka ka kyauta data sanadinka d'iyar mutane ta kusa ransa lafiyarta ko ranta?". Idanu omari ya fidda yana duban haisam.
"Me kake cewa ne?....." Hannu haisam ya daga masa calmly yana lumshe idanunsa gami da budesu akansa.
"Karka musa akan komai.....zanta istigar......nasan Allah da zuciya yake amfani......amma zamuyi aiki dakai ne omari a bisa sharuddan da idan ba zaka iya kiyayesu ba.......zaka fita daga cikin deal dinnan......ina magana ne a matsayin boss dinka....a yanzu...a wannan lokacin.......not your friend?" Ya qarashe da sigar tambaya yana kallon idanun omari.
Idon haisam kadai ya gaya masa muhimmancin daya dauki aikin dashi. A komai haisam me sauqin fahimta ne,me kuma bada uzuri ne banda akan aikinsa. Zaiyiwa haisam uzuri sau million times idan har yanason hakan.....don yasan wayeshi a waje a kuma bayan aikinsa.
"Yes sir" Omari ya fada da dukka girmamawa da seriousness.
★Yadda ta farka a firgice shi ya sanya aisa dake daura dankwalinta gaban madubi tsorata itama. Sosai ta maida dubanta ga akhnan da farkawarta kenan a baccin.
(08187255862 lu'u lu'u paying)
Zama tayi sosai cikin kujerar tana saka fuskarta a tafin hannunta ba tare data damu da gyaran hargitsatsen gashin kanta ba.
Ajiyar zuciya aisa ta sauke tana maida hankalinta ga abinda takeyi cikin madubin. Tsakanin jiya da yau mafarkinta na uku kenan. Mafarkin data gama fahimtar ba akan komai bane sai akan abinda ya faru jiyan.
"Ya kamata ki sassautawa kanki haka,abinda ya faru ya riga ya faru,saidai kuma a kiyaye gaba" Aisa ta fadi hankalinta kwance. Ko kadan batajin zatayi tarayya da akhnan wajen tayata jin ciwon abinda ya faru da ita,komai daya farun tana dangantashi da zallar rashin jin magana da shawarar irin nasu ita da Shehinaz. Inda ta dauka shawararta,inda taji abinda ta fada mata for the first place ma da ba'azo nan din ba.
"Na wuce office......na bayar da sanarwar baki da lafiya don kada office dinki ya zama ba wani motsi......yana da kyau ki qwarara jikinki ki koma office dinki" Aisa ta fada tana yin gaba gami da ficewa daga dakin.
Da fari hawaye take zubarwa,amma maganganun aisa sai suka sake saka mata dafi a ranta. Da gaske ya cuceta ya tsaida komai nata. Walwalarta,nishadinta dama ayyukanta. Hakan kuma bai isa ba,har cikin baccin da take samun salama shima bai barta ba?. Wanne irin mutum ne shi?,wanne irin azzalumi ne?,anya ruhinta zai samu salama kuwa idan bata rama abinda yayi mata ba?.
Kuka me qaramin sauti ta saki ta jawo pillow tana kwantar da kanta gami da maida gashinta baya. Daidai sanda aisa ta dawo don ta manta tabar wayarta cikin dakin.
Abinda ke ranta yaqi wuce mata bare ta samu ta huta,har zuwa sanda ta zare kayan jikinta tsaf da takeji ta tsanesu ta bada umarnin a fita dasu,kada a sake dawo mata dasu cikin gidan,koda gilmawarsu bata qaunar ta sake gani,ta wuce zuwa bathroom dinta da yafi kama da wani parlor din alfarmar,ta wuce cikin jacuzzi ta sakarwa kanta ruwa me bala'in dumin da kadan ya rage yayi zafi sosai.
Batasan adadin awannin data dauka cikin ruwan ba yana saukar mata tsakiyar kanta ba. Idanunta kan ruwan dake gudu ta rariyar,tana jin inama wannan ranar ta wuce da dukka wani memory na dukka al'ummar da suke wajen abun ya faru?,inama ace zata iya shafe komai ta mantar da kowa komai ya wuce tamkar bai faru a ranar ba?.
Dukka hannuwanta ta saka tana maida jiqaqqiyar sumarta baya,wadda ta lafe saman farar fatarta tsahonta yana kaiwa dab da mazaunanta. Iska ta furzar daga bakinta ta cikin ruwan,tana tuna yadda ya tureta daga jikinsa ya kuma direta saman qafafunta.
Batasan sanda hawaye ya balle mata ba,kamar ita?......diya guda ga sultane.......akhnan muhammad?......har wani ya samu damar kusanci da jikinta?......har yana jin ta zame masa damuwar da zai tureta har haka?.
Wata mahaukaciyar tsanarsa ta taso mata......ta kuma yi mata tsaye a zuciyarta ta sakata sakin kuka sosai cikin ruwan.
Dama can ya shirya komai ne......dama can ya shirya faruwar hakan......banda haka ta yaya tana zaman zamanta yayi requesting yayi tsere da ita?,ita daya tallin tal!....duk tarin 'yan wasan da Niamey dama niger gaba daya take dasu?.
Batasan ta dauki lokaci me tsaho a bandakin ba sai da taji Shehinaz na knocking qofar daga waje,ta ciri wani siririn band ta daure gashinta sannan ta fito ta sabe jikinta ta koma cikin bathtub ta qarasa wankan.
Sanda ta fito da aisa da Shehinaz dukkaninsu suna zaune a mabanbantan gurare cikin dakin. Kowacce waya ce a hannunta,ba wannan hirar ba kuma karadin.
Da kanta ta sake yiwa kanta alqalanci.......tunda har a yau takejin nauyi da wani irin rashin dadi cikin ranta tsakaninta dasu aisa.....su aisa din da kafin mallakar hankulansu hatta da wanda suna iya shiga bandaki daya kat kenan......amma a yau takejin nauyin kallon idanunsa?.
Cikin dukkanin jikinta gaba daya take jin ta muzanta......cikin kowanne motsawa da zatayi ji take kaman aisa da Shehinaz suna kallonta ne......kamar suna mata kallon marar sa'a!......mara nasara!......
Da wannan tunanin ta sauya kayan da birra ta ajiye mata. Lumshe ido tayi tana shaqar wani qamshi na daban da taji yau kayan sukeyi. Lallausan qamshin nan na musamman daga turaren incense by kabo daughter(+234 803 211 9803 tasted and trusted).
Kawai aisa ta gwada yi mata kabbasar kayanne......sanin kyakkyawar alaqa da soyayyarta da qamshi,wataqila hakan zai sanyaya mata zuciyarta.
Ta samu nutsuwa sosai cikin sallarta,kamar yadda qamshin ya huda zuciyarta sosai ya soma rage radadin da takeji. Saidai sanda ta kammala sallar komawa tayi ta lafe cikin sofa tana nannade jikinta da kyau cikin after dress din me yalwa da tayi sallar da ita,ta kuma maida idonta ta rufe ruf ba tare da tace da kowa komai ba,tana shaqar lallausan qamshin kabbasar a hankali tana tattaro nutsuwarta.
Ganin haka ya sanya aisa qyarawa Shehinaz,sai kawai suka miqe a nutse suna ficewa a dakin gami da ja mata qofar kowa baice komai da ita ba.
★★ *HAISAM*★★
Daga yadda shirunsa ya kasance tun bayan sallama da yayi dasu khadeem bayan ya jagorancesu sallar magariba sannan sukayi sallama suka wuce filin sauka da tashi jiragen sama na Niamey din omari ya gama sanin an samu matsala.
Daga yanayin idanunsa kadai omari ya fahimci ranshi a tsananin bace yake,wani irin mutum ne shi da sam ba kasafai ya fiya magana ba koda ba cikin fushi yake ba ballantana yana cikin fushi. Yayi riqo sosai da hadith dinnan na ma'aiki S A W da yayi hani da magana cikin fushi,idan kana tsaye kuma ka zauna. Zai iya qayyade sau nawa ya taba ganinsa yana magana alhalin cikin fushi yake?.
A karo na barkatai omari ya sake dubansa. Ya sauya kayansa zuwa wasu Indonesian kurta farare tas masu laushi,wadanda aka yiwa ado da gray color din zare. Kanshi ba hula sai tattausan gashinsa dake a gyare tsaf.....kai bakace shine wannan da yayi tsere awa biyu baya da suka wuce ba.
Jikinsa da lallausan turaren nan nasa ya zaunawa qamshinsa ne yake fita a hankali da wani irin sanyi me kwantar da rai. Dan qaramin littafi ne a hannunsa da tunda suka zauna a motar shi yake dubawa shafi shafi.
Wannan din na cikin dabi'arsa ta biyu. Indai ranshi yana a bace ba abinda yake bashi peace da relief sai karatu. Yana iya gamawa da littafi guda idan yana cikin fushin da baison a matsa masa yayi magana duk yawan mas hafin littafin.
Yaso qwarai kada yace masa komai kamar yadda aikinsa ya nuna buqatarsa kenan,to amma kuma ya gaji da canki cankin ganin sun dauki hanya d'od'ar,su da suke da ticket na jirgin da zai sauka agadez qarfe bakwai da rabi na safiyar washegari. Bugu da qari driver din dake tuqasu a yanzu dan qasar ne,ba baqo bane irinsu ballantana yayi tunanin bace hanya yayi.
"Amma fa.....kamar awa guda kawai ya ragewa jirginmu ya tashi.....kuma naga mp din yana nuna mun dauki hanyar barin Niamey ne". Omari ya furta a nutse kaman bashi ba. Sau tari fushin haisam baya bayyana muraran,amma su suna kalla suke ganewa. Dukkaninsu suna shiga wani sabon hankali da sabuwar nutsuwar idan ran haisam ya baci,bawai don zai gaya musu maganganu marasa dadi,ko zaiyi fada da dayansu ba....aah.....sai don nauyinsa da sukeji da wani irin kwarjini da nutsuwa da Allah ya bashi. Zai qalubalanceka ne idan buqatar hakan ta kama da wani irin nutsuwa da hikima a kalamansa......zai kuma dafaka da ruwan jikinka idan baikai yace komai da kai ba.
Ba tare daya dauke littafin a fuskarsa ba ko ya dubi omari ba ya amsa masa.
"Buqatar tafiya a motar tafi ta tafiya a flight muhimmanci" Ya amsa a taqaice yana buda shafin gaba na littafinsa.
Shuru omari yayi yana sake zuba masa idanu. Wato halin zai gwada masa a aikace?.....shikam baya jurar wannan,bazai bari bama su shiga garin mutane da basusan komai nasu ba da wannan halin da haisam ya yanke nuna masa.
"Amma dukka wannan shariyar ta mece?,da magana a cikinka mafi kyau ka fito ka fadeta" Omari ya fada cikin nashi kalar iya rigimar yana hade rai da bata fuska kaman shi akawa laifin.
Bai kalleshi ba,amma yadda yayi maganar kadai haisam yasan me yake shirin yi,don haka yayi kaman baiji me yake cewa ba.
Bai magantun ba kuwa har sai da omari ya fidda rai zaice wani abu din,sannan ya rufe littafin a nutse bayan ya saka alama ya ajjiyeshi daga gefansa.
"Me kakeso nace maka omari?.......ince maka ka kyauta daka hadani tsere da wadda take ba muharramata ba?......ko ince maka kyauta daga sakani hada jiki da matar da take haramun nayi mata koda zuzzurfan kallo ballanta jikkunanmu su hadu?.....ko kuma nace maka ka kyauta data sanadinka d'iyar mutane ta kusa ransa lafiyarta ko ranta?". Idanu omari ya fidda yana duban haisam.
"Me kake cewa ne?....." Hannu haisam ya daga masa calmly yana lumshe idanunsa gami da budesu akansa.
"Karka musa akan komai.....zanta istigar......nasan Allah da zuciya yake amfani......amma zamuyi aiki dakai ne omari a bisa sharuddan da idan ba zaka iya kiyayesu ba.......zaka fita daga cikin deal dinnan......ina magana ne a matsayin boss dinka....a yanzu...a wannan lokacin.......not your friend?" Ya qarashe da sigar tambaya yana kallon idanun omari.
Idon haisam kadai ya gaya masa muhimmancin daya dauki aikin dashi. A komai haisam me sauqin fahimta ne,me kuma bada uzuri ne banda akan aikinsa. Zaiyiwa haisam uzuri sau million times idan har yanason hakan.....don yasan wayeshi a waje a kuma bayan aikinsa.
"Yes sir" Omari ya fada da dukka girmamawa da seriousness.
★Yadda ta farka a firgice shi ya sanya aisa dake daura dankwalinta gaban madubi tsorata itama. Sosai ta maida dubanta ga akhnan da farkawarta kenan a baccin.
(08187255862 lu'u lu'u paying)
Zama tayi sosai cikin kujerar tana saka fuskarta a tafin hannunta ba tare data damu da gyaran hargitsatsen gashin kanta ba.
Ajiyar zuciya aisa ta sauke tana maida hankalinta ga abinda takeyi cikin madubin. Tsakanin jiya da yau mafarkinta na uku kenan. Mafarkin data gama fahimtar ba akan komai bane sai akan abinda ya faru jiyan.
"Ya kamata ki sassautawa kanki haka,abinda ya faru ya riga ya faru,saidai kuma a kiyaye gaba" Aisa ta fadi hankalinta kwance. Ko kadan batajin zatayi tarayya da akhnan wajen tayata jin ciwon abinda ya faru da ita,komai daya farun tana dangantashi da zallar rashin jin magana da shawarar irin nasu ita da Shehinaz. Inda ta dauka shawararta,inda taji abinda ta fada mata for the first place ma da ba'azo nan din ba.
"Na wuce office......na bayar da sanarwar baki da lafiya don kada office dinki ya zama ba wani motsi......yana da kyau ki qwarara jikinki ki koma office dinki" Aisa ta fada tana yin gaba gami da ficewa daga dakin.
Da fari hawaye take zubarwa,amma maganganun aisa sai suka sake saka mata dafi a ranta. Da gaske ya cuceta ya tsaida komai nata. Walwalarta,nishadinta dama ayyukanta. Hakan kuma bai isa ba,har cikin baccin da take samun salama shima bai barta ba?. Wanne irin mutum ne shi?,wanne irin azzalumi ne?,anya ruhinta zai samu salama kuwa idan bata rama abinda yayi mata ba?.
Kuka me qaramin sauti ta saki ta jawo pillow tana kwantar da kanta gami da maida gashinta baya. Daidai sanda aisa ta dawo don ta manta tabar wayarta cikin dakin.