Sashe 42
Luu Luu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani mamaki ne ya sauko ya lullubeta ganin kukan da akhnan keyi,kuma ganinta bai sanyata ta dakatar da kukan ta ba. Bawai bata yin kuka bane.....a'ah.....hasalima ita din irin mutanen nan ne da abun kuka baya masu kadan,don ko a quruciyarsu a rana tayi kuka kadan tayi biyar zuwa bakwai,to amma tunda ta zama cikakkiyar mace waye ma zai bata ranta ballantana ya sakata kuka?.....ko na quruciyar ma da tayi ta yishi ne saboda yarinta da kuma dabi'a.
Ta manta rabon da taga akhnan din tana kuka,abun sai ya zame mata wani baqon abu. Cikin zuciyarta ta sake tabbatarwa,tunda har hawaye ya zuba daga idanun akhnan din lallai abun babba ne a zuciyarta.
Ta rasa yadda zatayi controlling dinta dole ta kira Shehinaz,saidai ko ita dinma akhnan bata saurara ba. Zafin da takeji a zuciyarta tana jin bashi da hanyar samun sassauci na farko irin su barta tayi kukan.
Mamaki yaqi barin aisa. Princess dinnan ta agadez?.....CEO ta sahel couture guda ta zauna tana kuka akan wani abu da a wajenta baida wannan girman?,to wai quruciya ce har yanzu a jikin akhnan ko kuma zallar radadi da k'i fadin ne yake taba zuciyarta?.
Duk yadda suka dauki abun da sauqi ita da Shehinaz sai suka lura sama da haka akhnan ta daukeshi. Wunin guda tana qunci,tsakanin aisa da Shehinaz dinma daga qarshe ba wanda ya fita office din.
*8:00 pm*
Yadda sultanate ya zubawa wayar idanu yana kallon abinda ke wakana haka itama morsa safiyya ta kafeshi da kaifafan idanunta tana kallon kowanne reaction nasa a duk gilmawar video din.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
PAGE 34
____________________________
*_M&A EGYPTIAN ABAYAS_*
*Assalamualaikum*
*_Ina dandazon tawagar gayyar MATA 'YAN QWALISA?_*
*_WADANDA SUKAYI AMANNA DA ADO SUNE MUTUNCIN D'IYA MACE?_*👘🥻
*Ina masu son sari ko siyan daya na Egyptian abaya masu quality su iso garesu cikin Aminci???*
*M&A EGYPTIAN ABAYA itace zabinku NA FARKO*
*kuse ABAYAS takanas kuma kai tsaye DAGA EGYPT su iso gareku cikin kasa da kwana goma KACAL!✌🏽*
*_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_*
*_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽
*Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu*
*muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA*
*Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah*
+20 114 341 0873 ko kuma
0810 959 7791
https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt
___________________________
An haifeta abar riritawa......abar yiwa tattali.....abar gatantawa da shagabawa,abu mafi girman daraja da tsada da agadez ke qunshe dashi.......wannan ya sanya ta zama abar kaffa kaffa da bawa kulawa. Ganinta koda a cikin gidan ma wani abune da ya zamana babbar sa'a ga duk wanda ya samu hakan.......bayan ta girma kuma,wannan jinin na sarauta ya fara motsawa a jikinta,wannan izzar isar taqamar da qasaitar da sarauta ke saukarwa ta sake mamaye jininta da kyau. A hankali ta fahimci irin tsadarta......ta gane darajarta,ta kuma karanci tattalin da ake mata,saita sake sawa ranta da gaske ita din ta musamman ce.....da gaske tasha bamban da dukka mata.....harta 'yar uwarta dake da daraja kwatankwacin tata wato FALAAK. Tana ji a ranta ita da falaak ba daya suke ba......akwai wasu tarin banbamce babance da darajoji data dara falaak din dashi nesa ba kusa ba.
Tana jin a yau kamar ya barar da dukka wani wadannan darajoji da kima tata da wadannan laifukan guda biyu da yayi mata. Ta yaya zata barshi yaci bulus?,ya kamata ta bincika tasan koshi waye.......ya kamata ta fara hukuntashi ta kunyatashi ta hanyar bashi kayi kaman yadda yayi mata a gaban idanun mutane......kafin kuma tasa a masa mafi munin hukunci a bayan idanun kowa......a nesantashi da qasar da take rayuwa a cikinta.
Abinda ke ranta yaqi wuce mata bare ta samu ta huta,har zuwa sanda ta zare kayan jikinta tsaf da takeji ta tsanesu ta bada umarnin a fita dasu,kada a sake dawo mata dasu cikin gidan,koda gilmawarsu bata qaunar ta sake gani,ta wuce zuwa bathroom dinta da yafi kama da wani parlor din alfarmar,ta wuce cikin jacuzzi ta sakarwa kanta ruwa me bala'in dumin da kadan ya rage yayi zafi sosai.
Batasan adadin awannin data dauka cikin ruwan ba yana saukar mata tsakiyar kanta ba. Idanunta kan ruwan dake gudu ta rariyar,tana jin inama wannan ranar ta wuce da dukka wani memory na dukka al'ummar da suke wajen abun ya faru?,inama ace zata iya shafe komai ta mantar da kowa komai ya wuce tamkar bai faru a ranar ba?.
Dukka hannuwanta ta saka tana maida jiqaqqiyar sumarta baya,wadda ta lafe saman farar fatarta tsahonta yana kaiwa dab da mazaunanta. Iska ta furzar daga bakinta ta cikin ruwan,tana tuna yadda ya tureta daga jikinsa ya kuma direta saman qafafunta.
Batasan sanda hawaye ya balle mata ba,kamar ita?......diya guda ga sultane.......akhnan muhammad?......har wani ya samu damar kusanci da jikinta?......har yana jin ta zame masa damuwar da zai tureta har haka?.
Wata mahaukaciyar tsanarsa ta taso mata......ta kuma yi mata tsaye a zuciyarta ta sakata sakin kuka sosai cikin ruwan.
Dama can ya shirya komai ne......dama can ya shirya faruwar hakan......banda haka ta yaya tana zaman zamanta yayi requesting yayi tsere da ita?,ita daya tallin tal!....duk tarin 'yan wasan da Niamey dama niger gaba daya take dasu?.
Batasan ta dauki lokaci me tsaho a bandakin ba sai da taji Shehinaz na knocking qofar daga waje,ta ciri wani siririn band ta daure gashinta sannan ta fito ta sabe jikinta ta koma cikin bathtub ta qarasa wankan.
Sanda ta fito da aisa da Shehinaz dukkaninsu suna zaune a mabanbantan gurare cikin dakin. Kowacce waya ce a hannunta,ba wannan hirar ba kuma karadin.
Da kanta ta sake yiwa kanta alqalanci.......tunda har a yau takejin nauyi da wani irin rashin dadi cikin ranta tsakaninta dasu aisa.....su aisa din da kafin mallakar hankulansu hatta da wanda suna iya shiga bandaki daya kat kenan......amma a yau takejin nauyin kallon idanunsa?.
Cikin dukkanin jikinta gaba daya take jin ta muzanta......cikin kowanne motsawa da zatayi ji take kaman aisa da Shehinaz suna kallonta ne......kamar suna mata kallon marar sa'a!......mara nasara!......
Da wannan tunanin ta sauya kayan da birra ta ajiye mata. Lumshe ido tayi tana shaqar wani qamshi na daban da taji yau kayan sukeyi. Lallausan qamshin nan na musamman daga turaren incense by kabo daughter(+234 803 211 9803 tasted and trusted).
Kawai aisa ta gwada yi mata kabbasar kayanne......sanin kyakkyawar alaqa da soyayyarta da qamshi,wataqila hakan zai sanyaya mata zuciyarta.
Ta samu nutsuwa sosai cikin sallarta,kamar yadda qamshin ya huda zuciyarta sosai ya soma rage radadin da takeji. Saidai sanda ta kammala sallar komawa tayi ta lafe cikin sofa tana nannade jikinta da kyau cikin after dress din me yalwa da tayi sallar da ita,ta kuma maida idonta ta rufe ruf ba tare da tace da kowa komai ba,tana shaqar lallausan qamshin kabbasar a hankali tana tattaro nutsuwarta.
Ganin haka ya sanya aisa qyarawa Shehinaz,sai kawai suka miqe a nutse suna ficewa a dakin gami da ja mata qofar kowa baice komai da ita ba.
★★ *HAISAM*★★
Daga yadda shirunsa ya kasance tun bayan sallama da yayi dasu khadeem bayan ya jagorancesu sallar magariba sannan sukayi sallama suka wuce filin sauka da tashi jiragen sama na Niamey din omari ya gama sanin an samu matsala.
Daga yanayin idanunsa kadai omari ya fahimci ranshi a tsananin bace yake,wani irin mutum ne shi da sam ba kasafai ya fiya magana ba koda ba cikin fushi yake ba ballantana yana cikin fushi. Yayi riqo sosai da hadith dinnan na ma'aiki S A W da yayi hani da magana cikin fushi,idan kana tsaye kuma ka zauna. Zai iya qayyade sau nawa ya taba ganinsa yana magana alhalin cikin fushi yake?.
A karo na barkatai omari ya sake dubansa. Ya sauya kayansa zuwa wasu Indonesian kurta farare tas masu laushi,wadanda aka yiwa ado da gray color din zare. Kanshi ba hula sai tattausan gashinsa dake a gyare tsaf.....kai bakace shine wannan da yayi tsere awa biyu baya da suka wuce ba.
Jikinsa da lallausan turaren nan nasa ya zaunawa qamshinsa ne yake fita a hankali da wani irin sanyi me kwantar da rai. Dan qaramin littafi ne a hannunsa da tunda suka zauna a motar shi yake dubawa shafi shafi.
Wannan din na cikin dabi'arsa ta biyu. Indai ranshi yana a bace ba abinda yake bashi peace da relief sai karatu. Yana iya gamawa da littafi guda idan yana cikin fushin da baison a matsa masa yayi magana duk yawan mas hafin littafin.
Yaso qwarai kada yace masa komai kamar yadda aikinsa ya nuna buqatarsa kenan,to amma kuma ya gaji da canki cankin ganin sun dauki hanya d'od'ar,su da suke da ticket na jirgin da zai sauka agadez qarfe bakwai da rabi na safiyar washegari. Bugu da qari driver din dake tuqasu a yanzu dan qasar ne,ba baqo bane irinsu ballantana yayi tunanin bace hanya yayi.
"Amma fa.....kamar awa guda kawai ya ragewa jirginmu ya tashi.....kuma naga mp din yana nuna mun dauki hanyar barin Niamey ne". Omari ya furta a nutse kaman bashi ba. Sau tari fushin haisam baya bayyana muraran,amma su suna kalla suke ganewa. Dukkaninsu suna shiga wani sabon hankali da sabuwar nutsuwar idan ran haisam ya baci,bawai don zai gaya musu maganganu marasa dadi,ko zaiyi fada da dayansu ba....aah.....sai don nauyinsa da sukeji da wani irin kwarjini da nutsuwa da Allah ya bashi. Zai qalubalanceka ne idan buqatar hakan ta kama da wani irin nutsuwa da hikima a kalamansa......zai kuma dafaka da ruwan jikinka idan baikai yace komai da kai ba.
Ba tare daya dauke littafin a fuskarsa ba ko ya dubi omari ba ya amsa masa.
Ta manta rabon da taga akhnan din tana kuka,abun sai ya zame mata wani baqon abu. Cikin zuciyarta ta sake tabbatarwa,tunda har hawaye ya zuba daga idanun akhnan din lallai abun babba ne a zuciyarta.
Ta rasa yadda zatayi controlling dinta dole ta kira Shehinaz,saidai ko ita dinma akhnan bata saurara ba. Zafin da takeji a zuciyarta tana jin bashi da hanyar samun sassauci na farko irin su barta tayi kukan.
Mamaki yaqi barin aisa. Princess dinnan ta agadez?.....CEO ta sahel couture guda ta zauna tana kuka akan wani abu da a wajenta baida wannan girman?,to wai quruciya ce har yanzu a jikin akhnan ko kuma zallar radadi da k'i fadin ne yake taba zuciyarta?.
Duk yadda suka dauki abun da sauqi ita da Shehinaz sai suka lura sama da haka akhnan ta daukeshi. Wunin guda tana qunci,tsakanin aisa da Shehinaz dinma daga qarshe ba wanda ya fita office din.
*8:00 pm*
Yadda sultanate ya zubawa wayar idanu yana kallon abinda ke wakana haka itama morsa safiyya ta kafeshi da kaifafan idanunta tana kallon kowanne reaction nasa a duk gilmawar video din.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
PAGE 34
____________________________
*_M&A EGYPTIAN ABAYAS_*
*Assalamualaikum*
*_Ina dandazon tawagar gayyar MATA 'YAN QWALISA?_*
*_WADANDA SUKAYI AMANNA DA ADO SUNE MUTUNCIN D'IYA MACE?_*👘🥻
*Ina masu son sari ko siyan daya na Egyptian abaya masu quality su iso garesu cikin Aminci???*
*M&A EGYPTIAN ABAYA itace zabinku NA FARKO*
*kuse ABAYAS takanas kuma kai tsaye DAGA EGYPT su iso gareku cikin kasa da kwana goma KACAL!✌🏽*
*_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_*
*_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽
*Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu*
*muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA*
*Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah*
+20 114 341 0873 ko kuma
0810 959 7791
https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt
___________________________
An haifeta abar riritawa......abar yiwa tattali.....abar gatantawa da shagabawa,abu mafi girman daraja da tsada da agadez ke qunshe dashi.......wannan ya sanya ta zama abar kaffa kaffa da bawa kulawa. Ganinta koda a cikin gidan ma wani abune da ya zamana babbar sa'a ga duk wanda ya samu hakan.......bayan ta girma kuma,wannan jinin na sarauta ya fara motsawa a jikinta,wannan izzar isar taqamar da qasaitar da sarauta ke saukarwa ta sake mamaye jininta da kyau. A hankali ta fahimci irin tsadarta......ta gane darajarta,ta kuma karanci tattalin da ake mata,saita sake sawa ranta da gaske ita din ta musamman ce.....da gaske tasha bamban da dukka mata.....harta 'yar uwarta dake da daraja kwatankwacin tata wato FALAAK. Tana ji a ranta ita da falaak ba daya suke ba......akwai wasu tarin banbamce babance da darajoji data dara falaak din dashi nesa ba kusa ba.
Tana jin a yau kamar ya barar da dukka wani wadannan darajoji da kima tata da wadannan laifukan guda biyu da yayi mata. Ta yaya zata barshi yaci bulus?,ya kamata ta bincika tasan koshi waye.......ya kamata ta fara hukuntashi ta kunyatashi ta hanyar bashi kayi kaman yadda yayi mata a gaban idanun mutane......kafin kuma tasa a masa mafi munin hukunci a bayan idanun kowa......a nesantashi da qasar da take rayuwa a cikinta.
Abinda ke ranta yaqi wuce mata bare ta samu ta huta,har zuwa sanda ta zare kayan jikinta tsaf da takeji ta tsanesu ta bada umarnin a fita dasu,kada a sake dawo mata dasu cikin gidan,koda gilmawarsu bata qaunar ta sake gani,ta wuce zuwa bathroom dinta da yafi kama da wani parlor din alfarmar,ta wuce cikin jacuzzi ta sakarwa kanta ruwa me bala'in dumin da kadan ya rage yayi zafi sosai.
Batasan adadin awannin data dauka cikin ruwan ba yana saukar mata tsakiyar kanta ba. Idanunta kan ruwan dake gudu ta rariyar,tana jin inama wannan ranar ta wuce da dukka wani memory na dukka al'ummar da suke wajen abun ya faru?,inama ace zata iya shafe komai ta mantar da kowa komai ya wuce tamkar bai faru a ranar ba?.
Dukka hannuwanta ta saka tana maida jiqaqqiyar sumarta baya,wadda ta lafe saman farar fatarta tsahonta yana kaiwa dab da mazaunanta. Iska ta furzar daga bakinta ta cikin ruwan,tana tuna yadda ya tureta daga jikinsa ya kuma direta saman qafafunta.
Batasan sanda hawaye ya balle mata ba,kamar ita?......diya guda ga sultane.......akhnan muhammad?......har wani ya samu damar kusanci da jikinta?......har yana jin ta zame masa damuwar da zai tureta har haka?.
Wata mahaukaciyar tsanarsa ta taso mata......ta kuma yi mata tsaye a zuciyarta ta sakata sakin kuka sosai cikin ruwan.
Dama can ya shirya komai ne......dama can ya shirya faruwar hakan......banda haka ta yaya tana zaman zamanta yayi requesting yayi tsere da ita?,ita daya tallin tal!....duk tarin 'yan wasan da Niamey dama niger gaba daya take dasu?.
Batasan ta dauki lokaci me tsaho a bandakin ba sai da taji Shehinaz na knocking qofar daga waje,ta ciri wani siririn band ta daure gashinta sannan ta fito ta sabe jikinta ta koma cikin bathtub ta qarasa wankan.
Sanda ta fito da aisa da Shehinaz dukkaninsu suna zaune a mabanbantan gurare cikin dakin. Kowacce waya ce a hannunta,ba wannan hirar ba kuma karadin.
Da kanta ta sake yiwa kanta alqalanci.......tunda har a yau takejin nauyi da wani irin rashin dadi cikin ranta tsakaninta dasu aisa.....su aisa din da kafin mallakar hankulansu hatta da wanda suna iya shiga bandaki daya kat kenan......amma a yau takejin nauyin kallon idanunsa?.
Cikin dukkanin jikinta gaba daya take jin ta muzanta......cikin kowanne motsawa da zatayi ji take kaman aisa da Shehinaz suna kallonta ne......kamar suna mata kallon marar sa'a!......mara nasara!......
Da wannan tunanin ta sauya kayan da birra ta ajiye mata. Lumshe ido tayi tana shaqar wani qamshi na daban da taji yau kayan sukeyi. Lallausan qamshin nan na musamman daga turaren incense by kabo daughter(+234 803 211 9803 tasted and trusted).
Kawai aisa ta gwada yi mata kabbasar kayanne......sanin kyakkyawar alaqa da soyayyarta da qamshi,wataqila hakan zai sanyaya mata zuciyarta.
Ta samu nutsuwa sosai cikin sallarta,kamar yadda qamshin ya huda zuciyarta sosai ya soma rage radadin da takeji. Saidai sanda ta kammala sallar komawa tayi ta lafe cikin sofa tana nannade jikinta da kyau cikin after dress din me yalwa da tayi sallar da ita,ta kuma maida idonta ta rufe ruf ba tare da tace da kowa komai ba,tana shaqar lallausan qamshin kabbasar a hankali tana tattaro nutsuwarta.
Ganin haka ya sanya aisa qyarawa Shehinaz,sai kawai suka miqe a nutse suna ficewa a dakin gami da ja mata qofar kowa baice komai da ita ba.
★★ *HAISAM*★★
Daga yadda shirunsa ya kasance tun bayan sallama da yayi dasu khadeem bayan ya jagorancesu sallar magariba sannan sukayi sallama suka wuce filin sauka da tashi jiragen sama na Niamey din omari ya gama sanin an samu matsala.
Daga yanayin idanunsa kadai omari ya fahimci ranshi a tsananin bace yake,wani irin mutum ne shi da sam ba kasafai ya fiya magana ba koda ba cikin fushi yake ba ballantana yana cikin fushi. Yayi riqo sosai da hadith dinnan na ma'aiki S A W da yayi hani da magana cikin fushi,idan kana tsaye kuma ka zauna. Zai iya qayyade sau nawa ya taba ganinsa yana magana alhalin cikin fushi yake?.
A karo na barkatai omari ya sake dubansa. Ya sauya kayansa zuwa wasu Indonesian kurta farare tas masu laushi,wadanda aka yiwa ado da gray color din zare. Kanshi ba hula sai tattausan gashinsa dake a gyare tsaf.....kai bakace shine wannan da yayi tsere awa biyu baya da suka wuce ba.
Jikinsa da lallausan turaren nan nasa ya zaunawa qamshinsa ne yake fita a hankali da wani irin sanyi me kwantar da rai. Dan qaramin littafi ne a hannunsa da tunda suka zauna a motar shi yake dubawa shafi shafi.
Wannan din na cikin dabi'arsa ta biyu. Indai ranshi yana a bace ba abinda yake bashi peace da relief sai karatu. Yana iya gamawa da littafi guda idan yana cikin fushin da baison a matsa masa yayi magana duk yawan mas hafin littafin.
Yaso qwarai kada yace masa komai kamar yadda aikinsa ya nuna buqatarsa kenan,to amma kuma ya gaji da canki cankin ganin sun dauki hanya d'od'ar,su da suke da ticket na jirgin da zai sauka agadez qarfe bakwai da rabi na safiyar washegari. Bugu da qari driver din dake tuqasu a yanzu dan qasar ne,ba baqo bane irinsu ballantana yayi tunanin bace hanya yayi.
"Amma fa.....kamar awa guda kawai ya ragewa jirginmu ya tashi.....kuma naga mp din yana nuna mun dauki hanyar barin Niamey ne". Omari ya furta a nutse kaman bashi ba. Sau tari fushin haisam baya bayyana muraran,amma su suna kalla suke ganewa. Dukkaninsu suna shiga wani sabon hankali da sabuwar nutsuwar idan ran haisam ya baci,bawai don zai gaya musu maganganu marasa dadi,ko zaiyi fada da dayansu ba....aah.....sai don nauyinsa da sukeji da wani irin kwarjini da nutsuwa da Allah ya bashi. Zai qalubalanceka ne idan buqatar hakan ta kama da wani irin nutsuwa da hikima a kalamansa......zai kuma dafaka da ruwan jikinka idan baikai yace komai da kai ba.
Ba tare daya dauke littafin a fuskarsa ba ko ya dubi omari ba ya amsa masa.