← Book details Eemaan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 161 OF 300

Sashe 161

Eemaan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Saketa Mujaheed yayi har sannan bai daina kallonta ba sai kuma kawai ya juya ya nufi kofa ya fita, ta bi sa da kallo tana share hawayen dake xubowa idonta a hankali, komawa tayi gefen gado ta xauna a sanyaye, ko minti biyar ba ayi da fitar Mujaheed ba Inna ta dawo dakin tace "Tashi mu tafi Ahmadu na kiran ki ya ji ba'asi... Yau in sha Allahu xai mana iyaka da shi, kada ya sake shigo min tunda yayi aure, Ina murna na rabu da shi kuma sai kullum ya wani xo min xalo xalo kamar da ajiyarsa da ya mance min a nan???" Imaan tace "Ni dai ba abinda yayi min fa, kuma bance ki je ki ce ma Abba komai ba, ai ni ce ban gaishesa ba shi sa, kuma na hakura ni dai" Sake baki Inna tayi tana kallonta, Imaan ta mike ta nufi kofa tace "Komai sai ki tafi wajen Abba baki jira kin ji abinda ya faru ba..." daga haka ta fice a dakin ta bar Inna a tsaye. A hankali Imaan ta bude kofar parlon su ta shiga gabanta na faduwa, da ta tuna abinda Mujaheed yace wai xai gaya ma Daddy sai hankalin ta ya tashi, amma ta san baxai ma fada ba kawai tsorata ta yayi, Ammi ce kadai xaune parlor tana kallo, ta xauna kasa a hankali ta gaisheta, Ammi na kallonta tace "How are you feeling?" Tace "Na ji sauki Ammi" Ammi tace "Toh Allah ya sauwake, ga abinci can kitchen idan xa ki ci" ta girgixa kai tace "Na ci a wajen Inna" Ammi bata ce komai ba, hakan yasa ta mike ta nufi dakinta, a hankali ta nufi inda wayarta ke ajiye ta dauka xuciyarta na bugawa don bata san abinda xata gani ba, ta xauna gefen gado ta sauke ajiyar xuciya a hankali, can dai ta kunna wayar tana kallon screen din taga message da missed call a gaban screen din, missed call din ta fara shiga taga na sadeeq ne kuma just few minutes ago ya kirata, bude text din tayi tana dubawa kamar idanuwanta xa su fito, ta maimaita text din ya fi sau a kirga, can ta 6ata fuska kamar xata yi kuka, tafi minti goma a xaune, sai can kuma tayi wa Maryam forward din message din, bayan ta tabbata ya tafi tayi deleting gaba daya a wayar, ta d'an yi murmushi ta mike ta cire Hijab din jikinta ta linke ta kashe wutan dakin ta kwanta. Washegari da ya kasance Monday Imaan ta ji sauki sosai hakan yasa tayi shirin wucewa schl da safe, tana tattara few textbooks dinta da xata tafi da su makaranta taga wayarta dake gaban madubi yyi haske, karasawa tayi ta dau wayar taga text din Maryam ne ya shigo tana requesting ta hau WhatsApp su yi chatting, reply tayi mata da cewa sai ta dawo schl daga haka ta ajiye wayar ta fita dakin. Karfe hudu saura Imaan suka fito schl tare da Mariya dake ta mata labari tun basu fito aji ba, tsaye su ka ga Sadeeq jikin motarsa ya rungume hannu idonsa sanye da glasses, Sosai gaban Imaan ya fadi, Mariya ta wara ido tana kallonsa tace "Ya Sadeeq Drivers fa?" Shi dai bai ce mata komai ba, Kallon Imaan Mariya tayi tana murmushi tace "Sai gobe xan ci gaba Imaan" tuni kanninta biyu shiga mota yayan nasu, Imaan ta gyada mata kai tana d'an murmushi tace "Allah ya kai mu" Har Mariya xata shiga motar sai kuma ta kalli Imaan tace "Baxa ku gaisa da yayana ba" Imaan ta kalli Sadeeq dake kallonta ba ko kiftawa, daga inda take tsaye a hankali tace "Ina yini" ya gyada kai yace "Lafiya lau" daga haka ya xaga ya bude maxaunin driver ya shiga ya tada motar suka wuce. Imaan na dawowa islamiyya that same day taga Miss call din Sadeeq, kasa kiransa tayi da farko don bata san me xata ce masa ba, can dai tayi dialing number a hankali ta kai kunne, yana fara ring ya katse ya kirata, tayi gathering courage tayi picking, murya can kasa tayi masa sallama ya amsa yace "You are ignoring my calls ko" ta xaro ido tace "A'a wllh, bana kusa da wayar ne ai yanxu muka dawo islamiyya, jiya kuma Ina part din Inna wayar kuma na part din mu" yace "Ohk, I tot u where ignoring it shi sa ma ban xo ba yau, ya jikin?" Ta langwabar da kai tace "Na ji sauki" yace "Maa Sha Allah" shiru tayi ta rasa abun cewa, can yace "Did you see my text or u don't just want to talk about it?" D'an murmushin karfin hali tayi tace "Sure I saw it, I... but.. I can try doing as u wish, but I can't perform the action in the text" Dariya yayi yace "Ohk then...." Ta turo baki bata ce komai ba, yace "I will call you later xan fita masallaci" tace "Allah ya kai mu" daga haka ya katse wayar. Ranan Thursday da safe bayan Imaan ta gama shirin boko ta sami Ammi a kitchen a hankali tace "Ammi tunda ba islamiyya yau idan na dawo schl plss Ina son in je in gaida Gwaggwo daga nan sai in kai ma Aunty halima katin sauka" Ammi tace "Jiya ba ce min kika yi Thursday da Friday duk xa ku je islamiyyar ba da yamma?" Imaan ta xaro ido tace "Ance sai Friday morning and evening" Ammi ta tabe baki tace "Toh ki kira daddy ki gaya masa, ai ba ni xa ki gaya ma ba" Murmushi Imaan tayi tace "Ae har na gaya masa jiya da daddare" Ammi tace "Toh Allah ya kai mu" Imaan tace "Ameen" shayi ta hada a cup ta fita da bread da egg dinta a plate xuwa dinning. Tana dawowa schl ranan ko abincin kirki bata ci ba tayi wanka ta shirya cikin bakin abayanta ta sa Hijab har kasa ta fito parlor, Ammi dake kallonta tace "Kar ki kai magrib a hanya Imaan" xaro ido Imaan tayi tace "Ammi ni fa cewa Daddy nayi xan kwana" Ammi tace "Kwana kuma?" Imaan ta marairaice tace "Ehh Ammi na gaya masa, ki kirasa ma" Ammi tace "Toh schl din fa?" Imaan tace "A'a ai nace maki islamiyya xan je da safe da kuma yamma tunda Saturday ne saukan ai" Ammi tace "Ba ruwana ni ban ce ki kwana ba da kin gaisheta ki kai ma Halima kati ki juyo, am I clear???" imaan tayi shiru tana kallonta kamar xata yi kuka, Ammi ta ci gaba da abinda take, a hankali Imaan tace "Toh sai na dawo" Ammi tace "Dama kada ki kuskura ki kai magrib a titi ni dai na gaya maki" imaan ta nufi kofa bata ce komai ba har ta fita parlon. Imaan na isa gidan gwaggwo dama gaisheta kawai tayi tace "Ina sauri xan je gidan Anty Halima in kai mata kati in dawo...." Gwaggwo na kallonta tace "Toh shikenan sai kin dawo, ya saurayin naki Sadeeq?" Yar dariya tace "Yana nan, shi xai kai ni gidan Aunty Halima din ma, amma kar ki gaya ma Ammi fa" Gwaggwo tace "Au tare ku ke shine bai shigo mu gaisa ba" imaan tace "A'a yanxu dai ya kirani yana hanya" Gwaggwo tace "Toh Allah ya kawo sa lafiya, Mujaheed na lafiya da amaryar sa dai koh?" Imaan ta turo baki tace "Nima dai ban sani ba" Gwaggwo tace "Baki je gidan ba kenan" imaan tace "Mun je da Gwaggwo amma matar bata da mutunci, ni dama baxan sake xuwa gidansa ba har abada" Gwaggwo tace "Ikon Allah, toh Allah dai ya kyauta, amma ai babu xancen baxa ki kara xuwa gidan yayanki ba Imaan" Imaan ta dau wayarta dake ring ganin Sadeeq ne ta mike tana kallon Gwaggwo tace "Sai na dawo" Gwaggwo tace "Har ya iso" Kai ta gyada mata, Gwaggwo tace "Toh Allah ya kiyaye, hanya a dai kula kin ji" Imaan ta nufi kofa ta fita parlon, yana xaune mota ta karasa ta bude front seat, kallonta ya dinga yi, a hankali tace "Ina yini" ya d'an yi murmushi yana shafa kansa murya can kasa yace "Lafiya lau Hijab queen, you look beautiful in it always, but yau ma sai kin sa?" Shiru tayi tana kallonsa, Yana mata murmushi yace come in" a hankali ta shiga motar ta rufe ba tare da ta yarda sun hada ido ba, ya tada motar yace "Xa ki kai ma Halima card din first koh?" Ta gyada masa kai, driving yake kamar bai son yi, lkci lkci kuma yana kallonta ta gefen ido, shiru babu wanda yace komai cikinsu har suka isa gidan Aunty Halima after 15 mins ride, ya juya yana kallonta a hankali yace "Be fast Imaan" ta gyada masa kai ta sauka ta nufi cikin gidan ya bi ta da ido, jinginar da kansa yayi jikin mota ya lumshe idanuwansa, can ya bude ya dau wayarsa yayi dialing number ya kai kunne, ana dagawa, cikin cool voice dinsa yace "Selim... I think I am just sorry, I had to disappoint you guys, may be some other times xa ku santa, kawai na fasa deal din" Best dinsa Selim dake sauraronsa da mamaki yace "I don't get you Sadeeq..." Sadeeq ya d'an yi shiru sai kuma calmly yace "I can't bring her to that place, she's more than decent and innocent, though I have neva had bad intention toward her... but, I am sorry for the disappointment, I will compensate this deal for what ever amount you guys will require" Selim yace "You are sick, mu ne ba mu san ciwon kanmu ba ko, mu ne ba mu san ciwon babes din mu ba, what's the use of all this Sadeeq, after necessary arrangements da aka gama ka xo kana kawo mana wani surutu, this is very unusual of you, haka on ur Birthday wai wani she's sick baxata xo ba, wato mu namu Girlfriends din ne pure water....." Sadeeq dai tabe baki kawai yyi bai ce komai ba, Yana jin friends din nasa dake guest inn din nasa suna surutu daga karshe ya katse wayarsa, dialing number Mariya yayi, tana dagawa ya gaya mata wani babban wajen cin abinci
Chapter 161 · 0% Book details