Sashe 98
Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani sassanyan kyau da tayi ita kanta yaja hankalinta ina ga yaayanta? tayi imanin nan kusa za'a yi barin wannan jan ajin da kamewar tasa tayi fata fata,fatanta dai daya lah ya kawo komai da sauqi,saboda ta sani shi din bai iya
Kama komai da sauqi ba.
Tare suka jera nadeeya din tana ta mata hira,kamar yadda suka saba a baya ba amsa sai murmushinta me sanyin nan da yake sake qawata fuskarta.
Tun daga nesa inda yake tsaye ya hangi tahowarsu bayan ya daga kai daga latsa wayarsa da yakeyi. A hankali ya zare idanunsa daga kansu ya mayar ga hadiman gidan,wanda kusan duka maza ne suna kai kawo kowa yana gudanar da nasa aikin.
Qwayar idanunsa ya juya kadan ya rufeta sannan ya bude a lokaci guda yana gogarin controlling kansa game da mayafin jikinta.
Cikin jininsa qin mayafin yake,tun daga lokacin da ya fara ganinsa jikin nadeeya ya hanata amfani dashi,bata kuma sake ba.
Iska yaja sosai yana fesarwa hadi da dauke kansa yana kallon gefansa,so yake ya lalubi zuciyarsa yayi kaya control,meye nashi na shiga sha'anin shigar da duk taga dana ta zabawa kanta? nadeeya qanwarsa ce,jininsa ce wannan kuma fa?.
"'Matarka ce" yaji ana bashi amsa daga can wasan zuciyarsa. Kai ua girgiza a hankali
•ya juya da kansa yana sake maidawa kansu sanda suke gab da qarasowa inda yake.
Sarqewa idanunsu sukayi cikin na
Juna, kallon second biyu rak suka yiwa juna kiwa ya janye idonsa yana jun haushin kansa, toufeeq kam kasa jurewa yayi sai da ya saki qaramin tsaki yana jin hausnin abinda ya sake maidashi ga kallon fuskarta da tayi wani haske,skin dinta data dauki gyara fiye da zato ta hadu da hasken ranar safiyar,ranar da bata kammala budewa ba saboda gajimare daketa haduwa yana alamta haduwar hadari, irin hadarin farko farkon damina.
Suna isowa nadeeya bata tsaya jiran komai ba ta zame ta wuce ta barsu a gurin.
Shuru ya ratsa gurin,kowa a cikinsu yana ji da kansa,yana jin kuma faduwa ce ya yiwa dan uwansa magana. Iska ya sake furzarwa yana son abinda ya tsaya masa a maqoshi ya wuce,kamar bazai motsa ba kafin daga bisani ya fara takawa a hankali zuwa ciki. Bayansa ta gallawa harara,ta motsa bakinta zata ia tsaki amma saita hadiye abunta saboda tunawa da tayi da abinda ya faru da ita company sanadin tsakin,ta murguda bakinta wai duk ko zata huce sannan ta bishi a baya tana gunaguni gasa gasa
"Girman kai,fadin rai,bagin rai duk mutum shi daya" ta furta can qasan zuciyarta ba tare data bari ya fito sarari ba.
Tun tana hararar bavan nasa har taji kamar idanunta na neman juyewa,a hankali ta janye idanunta,tana dan rufesu kadan sannan ta sake budesu,kai tsaye saman baqar sumarsa da a kullum take cikin gyara ta sauka,ta kwanta sosai da wani irin gyara daya dace da shigarsa ta wani creamy color din yadi na maza,mara nauyi wanda kana iya hangen vest din jikinsa ta zallar cotton fara qar gar da ita.
Yadda yake dauke gafarsa da saukewa kadai zai nuna maka yawan kuzari da baiwar lafiya da Allah ya bashi,wani irin taku me cakude da
'yar sassarfa kadan wadda take sanyawa yake danyi mata nisa,har sai tadan qara nata saurin kadan. Shi kansa takun gani takeyi kamar akwai izza da gasaita a cikinsa
"Aikin kawai" ta furta tare da jan tsaki. A wannan karon tsakin nata ya bayyana,sai taga ya rage adadin takun nasa da yakeyi.
Gabanta ya fadi,ta dora zara zaran yatsuntsa da suka sha lallae saman bakinta tana dan fidda idanunta waje,ba tare da ya waiwayo ba sai taga yaci gaba da tafiyarsa,ta sauke boyayyar ajiyar zuciya yaci gaba da bin bayansa tana kame kallonta daqa kansa,kada wani tsautsayin yasa ta sake wani abun da dukkansu shi da ita zasu raba hali gaban suruka.
Da sallama a bakinsa ya tura gofar dakin maii,ita da 'var uwarta wassila suka hada baki wajen amsawa. Fuskar maji din fal da murmushi,wani farinciki yana sauka a zuciyarta. Ganinsu kadai tare ya haifar mata da farinciki me tarin yawa,tana ii a jikinta sãahar din itace addu'ar data jima tana yiwa toufeeq wajen roqa masa ubangiji yayi masa musaya mafi alkhairi da zai wanke dukkan quncin da ya samu kansa a ciki
"Qaraso mana ibnaty" maii dake duban sãahar cikin kulawa da murmushi ta fada. Tsananin kunya ce ta dabaibayeta,ta tako a hankali ta qaraso gabanta,sannan ta zame saman gwiwoyinta tana fadin
"Barka da asuba" gogarin dagota maji keyi amma sãahar din ta kasa sakewa bari ta mige kamar yadda maji keda buqata,dole ta barta fuskarta da murmushi tana dubanta tace
"Barkanmu ibnaty,ya kwanan bagon waje?"
"Alhamdulillah" ta amsa da gyar tana wasa da yatsunta
"Allah yayi muku albarka,yasa albarka a tarayyarku" maji ta fadi. Kasa amsawa tayi,sai daga kanta da tayi a hankali tana gaida wassila wadda suke magana qasa qasa da toufeeq,bata kuma iya jin ainihin abinda suke fadi. Itama kamar maji din,tana da matuqar kirki,hakanan ta karanci kamar akwai kyakkyawar mu'amala tsakaninta da toufeeq.
Qasa qasa maji ke janta da hira,saidai sam ta kasa sakewa da ita,surukuta sosai takeji,a gefe guda wanzuwar sa a waien yasa take jinta gaba daya a takure,saboda basu saba zama a muhalli guda ita da shi ba har irin haka. Duk da ta gefen idanunta tana lura da yadda ya karkata hankalinsa ga wayarsa,abinda ta karanta kwata kwata babu sabo ko shaquwa me yawa tsakaninsa da mahaifliyarsa. Inda itace tayi missing maama haka,ta tabbatar zuwa yanzu tana magale da ita.
Cikin harshen larabci wassila tayi magana da maji sannan ta juya ta yiwa toufeeq shima magana,ta cewa da saahar cikin gurbatacciyar hausarta
"Zanje na dawo surukata" sai ta gyada kai caking jin nauyin sunan data kirata dashi. Zata fita baaba ramatu na shigowa, fuskarta itama yalwace da fara'a tayi musu barka da fitowa suka kuma gaisa
"Ki hado mana breakfast din duka tare dasu,a nan zamuci" maji ta bada umarni, cikin girmamawa baaba ramatu ta juya ta fice.
Ba jimawa ta shigo ita da masu taimaka mata dauke da manyan trays guda uku,ta ajjiye a gabansu ta juya ta fita. Wayar hannunta maii ta ajjiye bayan ta kashe,ta jawo dukka trays din tsakaninsu ta dubi sãahar
"Matso maza diyata,cin abinci tare da juna yana gara dangon gauna soyayya da kuma fahimtar juna.
..tafaddal moha" ta garasa fada
tana sauke idanunta akan fuskar toufeeq,cikin zuciyarta tana juya halayyarsa da har yanzun bata barshi ba,a gefe guda kuma tana sake yarda da hirarsu da nadeeya ta daren jiya.
Tabbas akwai aiki a gabanta,wanda kuma zata aiwatar dashi. Sãahar nada kyakkyawar zuciyar da bazataso ahalinta su rasata ba,zatayi dukkan me yiwuwa ta tabbatar ta riqeta cikin iyalinta.
Bata taba kawowa zai sauko din kamar yadda maji ta buqata ba,sai gashi ya ajiye wayar tasa,ya kuma zamo daga saman sofa din da yake zaune,ya balle links din rigarsa yana tattare hannun rigar tasa sama. Bugun zuciyarta ne taji yana qaruwa saboda kusancin da suka samu sosai dashi,ya zamana yana tsakiyarsu ita da maji,qamshinsa me wani irin taushi,irin gamshin nan dake tashi a hankali ya fara karakaina a wajen,yana cakuduwa da nata
qamshin.
Dukka su biyun suka kai hannu lokaci guda a tare saman fararen plate din da baaba ramatu ta hado dasu don fara zubawa maji abinci,ya damqi saman hannunta a tausashe yana tsammanin plate din zai dauka. Karon farko kenan da hakan ta fara faruwa a tsakaninsu,a tare kowannensu ya dauke nashi hannun,wani irin abu yaji ya tsarga yarrr a jikinsa,tun daga hannun nasa ya aika sagon kowanne sashe na jikinsa. Yayin da saahar taji kamar wutar lantarki ce ta jata,cikin rashin saninsu kowannensu sai ya shiga yarfar da hannu,maji dake karantarsu a fakaice tace
"'Zuba mana moha" sake maida hannunsa yay,,ya buda komai ya zubawa maji ya ajjiye a gabanta
"Wannan yayimin yawa,kuci kai da
matarka,samu plate ka zubamin kadan" ta fada idanunta akan wayarta kamar batasan ta fadi wani abu ba. Sam bai taba mata musu ba,don haka ya dauki wani plate din ya zuba matan ya ajjiye mata,ya sanya cokali biyu cikin plate din kamar yadda ta umarta,sai ta ajiye wayartata tana gyaran zaman glass din fuskarta,ta jawo nata plate din da cup din tea tana murmushi tace
"Toh.... bismillah ko?"
"Dangari" sãahar ta furta a ranta,maji ta gama daureta da dukka jijiyoyin jikinta,batasan ta inda zata fura buda baki tana cin abinci a gaban wannan dan rainin hankalin ba,tana jin ta bata wani babban aiki ne da batasan yadda zata alwatar da shi ba.
Idanunsa ya lumshe shima vana budesu duka lokaci guda,ya motsa bakinsa kamar zalyi magana,sai yaga idanun maji din a kansa,don haka ya cinye duk wani uzuri da yaso bata,ya gyara zamansa yana lanqwashe gafafunsa ya dauki spoon daya tare da fara motsa abincin,ya riga ya fahimci abinda majin keso,zai kuma amintar da ita. Yadda taga yayin itama hakan tayi,saidai a nata bangaren ko loma daya ta kasa kaiwa bakinta,abin yayi mata yawa tako ina,gefe daya ga maji da takejin nauyi matuqa,daya bangaren kuma ga uban 'yan girman kan nan da takejin yadda ya sanya mata ido sosai. A nutse yake juya lomar abincin a bakinsa,duk da cewa bawai wani yunwa yakeji ba,amma saboda ya faranta ran maji din yake cin abincin. Yadda ta takura din shi hakan yayi masa,yana karantarta tsaf ta gasan idanunshi,wanda ba lallai bane ka karanci hakan kai tsaye.
*HUGUMA*
* TABARMAR KASHI_*
Book 02 Page 16
Ko a fuska ba zaka taba zaton karantar tata yake ba,har zuwa lokacin da maji ta magantu
"'Ki saki ilkinki dani khadijatu,ina jinki ne tamkar moha da nadeeya,ke yanzun diyata ce halak malak,zan iya raba kowacce damuwa tawa da sirrina dake" garamin murmushi ta saki tana jinjina kai. Tabe baki yayi kadan yana matsawa gefe daga gaban kwanukan alamar ya qoshi,duk wadan nan abubuwan gani yakeyi kawai salo ne irin na mata wanda kaidinsu ba qarami bane,sai yanzu ya karanci dalilin da ya sanya dukkansu ta tafi da hankalinsu,cikin ransa yake gulmarta,ta wani sadda kai qasa,tamkar ba itace wannan mara kunyar ba me shegen tsiwa dake iya yarfa masa maganar da duk duniya ba macen data isa ta gaya masa bayan maji
"Ban baku kowacce gudunmawa ba ko?" Maji ta fada tana murmushi,a nutse toufeeq ya waiwaya ya dubeta
"Wacce iri maji?"
Kama komai da sauqi ba.
Tare suka jera nadeeya din tana ta mata hira,kamar yadda suka saba a baya ba amsa sai murmushinta me sanyin nan da yake sake qawata fuskarta.
Tun daga nesa inda yake tsaye ya hangi tahowarsu bayan ya daga kai daga latsa wayarsa da yakeyi. A hankali ya zare idanunsa daga kansu ya mayar ga hadiman gidan,wanda kusan duka maza ne suna kai kawo kowa yana gudanar da nasa aikin.
Qwayar idanunsa ya juya kadan ya rufeta sannan ya bude a lokaci guda yana gogarin controlling kansa game da mayafin jikinta.
Cikin jininsa qin mayafin yake,tun daga lokacin da ya fara ganinsa jikin nadeeya ya hanata amfani dashi,bata kuma sake ba.
Iska yaja sosai yana fesarwa hadi da dauke kansa yana kallon gefansa,so yake ya lalubi zuciyarsa yayi kaya control,meye nashi na shiga sha'anin shigar da duk taga dana ta zabawa kanta? nadeeya qanwarsa ce,jininsa ce wannan kuma fa?.
"'Matarka ce" yaji ana bashi amsa daga can wasan zuciyarsa. Kai ua girgiza a hankali
•ya juya da kansa yana sake maidawa kansu sanda suke gab da qarasowa inda yake.
Sarqewa idanunsu sukayi cikin na
Juna, kallon second biyu rak suka yiwa juna kiwa ya janye idonsa yana jun haushin kansa, toufeeq kam kasa jurewa yayi sai da ya saki qaramin tsaki yana jin hausnin abinda ya sake maidashi ga kallon fuskarta da tayi wani haske,skin dinta data dauki gyara fiye da zato ta hadu da hasken ranar safiyar,ranar da bata kammala budewa ba saboda gajimare daketa haduwa yana alamta haduwar hadari, irin hadarin farko farkon damina.
Suna isowa nadeeya bata tsaya jiran komai ba ta zame ta wuce ta barsu a gurin.
Shuru ya ratsa gurin,kowa a cikinsu yana ji da kansa,yana jin kuma faduwa ce ya yiwa dan uwansa magana. Iska ya sake furzarwa yana son abinda ya tsaya masa a maqoshi ya wuce,kamar bazai motsa ba kafin daga bisani ya fara takawa a hankali zuwa ciki. Bayansa ta gallawa harara,ta motsa bakinta zata ia tsaki amma saita hadiye abunta saboda tunawa da tayi da abinda ya faru da ita company sanadin tsakin,ta murguda bakinta wai duk ko zata huce sannan ta bishi a baya tana gunaguni gasa gasa
"Girman kai,fadin rai,bagin rai duk mutum shi daya" ta furta can qasan zuciyarta ba tare data bari ya fito sarari ba.
Tun tana hararar bavan nasa har taji kamar idanunta na neman juyewa,a hankali ta janye idanunta,tana dan rufesu kadan sannan ta sake budesu,kai tsaye saman baqar sumarsa da a kullum take cikin gyara ta sauka,ta kwanta sosai da wani irin gyara daya dace da shigarsa ta wani creamy color din yadi na maza,mara nauyi wanda kana iya hangen vest din jikinsa ta zallar cotton fara qar gar da ita.
Yadda yake dauke gafarsa da saukewa kadai zai nuna maka yawan kuzari da baiwar lafiya da Allah ya bashi,wani irin taku me cakude da
'yar sassarfa kadan wadda take sanyawa yake danyi mata nisa,har sai tadan qara nata saurin kadan. Shi kansa takun gani takeyi kamar akwai izza da gasaita a cikinsa
"Aikin kawai" ta furta tare da jan tsaki. A wannan karon tsakin nata ya bayyana,sai taga ya rage adadin takun nasa da yakeyi.
Gabanta ya fadi,ta dora zara zaran yatsuntsa da suka sha lallae saman bakinta tana dan fidda idanunta waje,ba tare da ya waiwayo ba sai taga yaci gaba da tafiyarsa,ta sauke boyayyar ajiyar zuciya yaci gaba da bin bayansa tana kame kallonta daqa kansa,kada wani tsautsayin yasa ta sake wani abun da dukkansu shi da ita zasu raba hali gaban suruka.
Da sallama a bakinsa ya tura gofar dakin maii,ita da 'var uwarta wassila suka hada baki wajen amsawa. Fuskar maji din fal da murmushi,wani farinciki yana sauka a zuciyarta. Ganinsu kadai tare ya haifar mata da farinciki me tarin yawa,tana ii a jikinta sãahar din itace addu'ar data jima tana yiwa toufeeq wajen roqa masa ubangiji yayi masa musaya mafi alkhairi da zai wanke dukkan quncin da ya samu kansa a ciki
"Qaraso mana ibnaty" maii dake duban sãahar cikin kulawa da murmushi ta fada. Tsananin kunya ce ta dabaibayeta,ta tako a hankali ta qaraso gabanta,sannan ta zame saman gwiwoyinta tana fadin
"Barka da asuba" gogarin dagota maji keyi amma sãahar din ta kasa sakewa bari ta mige kamar yadda maji keda buqata,dole ta barta fuskarta da murmushi tana dubanta tace
"Barkanmu ibnaty,ya kwanan bagon waje?"
"Alhamdulillah" ta amsa da gyar tana wasa da yatsunta
"Allah yayi muku albarka,yasa albarka a tarayyarku" maji ta fadi. Kasa amsawa tayi,sai daga kanta da tayi a hankali tana gaida wassila wadda suke magana qasa qasa da toufeeq,bata kuma iya jin ainihin abinda suke fadi. Itama kamar maji din,tana da matuqar kirki,hakanan ta karanci kamar akwai kyakkyawar mu'amala tsakaninta da toufeeq.
Qasa qasa maji ke janta da hira,saidai sam ta kasa sakewa da ita,surukuta sosai takeji,a gefe guda wanzuwar sa a waien yasa take jinta gaba daya a takure,saboda basu saba zama a muhalli guda ita da shi ba har irin haka. Duk da ta gefen idanunta tana lura da yadda ya karkata hankalinsa ga wayarsa,abinda ta karanta kwata kwata babu sabo ko shaquwa me yawa tsakaninsa da mahaifliyarsa. Inda itace tayi missing maama haka,ta tabbatar zuwa yanzu tana magale da ita.
Cikin harshen larabci wassila tayi magana da maji sannan ta juya ta yiwa toufeeq shima magana,ta cewa da saahar cikin gurbatacciyar hausarta
"Zanje na dawo surukata" sai ta gyada kai caking jin nauyin sunan data kirata dashi. Zata fita baaba ramatu na shigowa, fuskarta itama yalwace da fara'a tayi musu barka da fitowa suka kuma gaisa
"Ki hado mana breakfast din duka tare dasu,a nan zamuci" maji ta bada umarni, cikin girmamawa baaba ramatu ta juya ta fice.
Ba jimawa ta shigo ita da masu taimaka mata dauke da manyan trays guda uku,ta ajjiye a gabansu ta juya ta fita. Wayar hannunta maii ta ajjiye bayan ta kashe,ta jawo dukka trays din tsakaninsu ta dubi sãahar
"Matso maza diyata,cin abinci tare da juna yana gara dangon gauna soyayya da kuma fahimtar juna.
..tafaddal moha" ta garasa fada
tana sauke idanunta akan fuskar toufeeq,cikin zuciyarta tana juya halayyarsa da har yanzun bata barshi ba,a gefe guda kuma tana sake yarda da hirarsu da nadeeya ta daren jiya.
Tabbas akwai aiki a gabanta,wanda kuma zata aiwatar dashi. Sãahar nada kyakkyawar zuciyar da bazataso ahalinta su rasata ba,zatayi dukkan me yiwuwa ta tabbatar ta riqeta cikin iyalinta.
Bata taba kawowa zai sauko din kamar yadda maji ta buqata ba,sai gashi ya ajiye wayar tasa,ya kuma zamo daga saman sofa din da yake zaune,ya balle links din rigarsa yana tattare hannun rigar tasa sama. Bugun zuciyarta ne taji yana qaruwa saboda kusancin da suka samu sosai dashi,ya zamana yana tsakiyarsu ita da maji,qamshinsa me wani irin taushi,irin gamshin nan dake tashi a hankali ya fara karakaina a wajen,yana cakuduwa da nata
qamshin.
Dukka su biyun suka kai hannu lokaci guda a tare saman fararen plate din da baaba ramatu ta hado dasu don fara zubawa maji abinci,ya damqi saman hannunta a tausashe yana tsammanin plate din zai dauka. Karon farko kenan da hakan ta fara faruwa a tsakaninsu,a tare kowannensu ya dauke nashi hannun,wani irin abu yaji ya tsarga yarrr a jikinsa,tun daga hannun nasa ya aika sagon kowanne sashe na jikinsa. Yayin da saahar taji kamar wutar lantarki ce ta jata,cikin rashin saninsu kowannensu sai ya shiga yarfar da hannu,maji dake karantarsu a fakaice tace
"'Zuba mana moha" sake maida hannunsa yay,,ya buda komai ya zubawa maji ya ajjiye a gabanta
"Wannan yayimin yawa,kuci kai da
matarka,samu plate ka zubamin kadan" ta fada idanunta akan wayarta kamar batasan ta fadi wani abu ba. Sam bai taba mata musu ba,don haka ya dauki wani plate din ya zuba matan ya ajjiye mata,ya sanya cokali biyu cikin plate din kamar yadda ta umarta,sai ta ajiye wayartata tana gyaran zaman glass din fuskarta,ta jawo nata plate din da cup din tea tana murmushi tace
"Toh.... bismillah ko?"
"Dangari" sãahar ta furta a ranta,maji ta gama daureta da dukka jijiyoyin jikinta,batasan ta inda zata fura buda baki tana cin abinci a gaban wannan dan rainin hankalin ba,tana jin ta bata wani babban aiki ne da batasan yadda zata alwatar da shi ba.
Idanunsa ya lumshe shima vana budesu duka lokaci guda,ya motsa bakinsa kamar zalyi magana,sai yaga idanun maji din a kansa,don haka ya cinye duk wani uzuri da yaso bata,ya gyara zamansa yana lanqwashe gafafunsa ya dauki spoon daya tare da fara motsa abincin,ya riga ya fahimci abinda majin keso,zai kuma amintar da ita. Yadda taga yayin itama hakan tayi,saidai a nata bangaren ko loma daya ta kasa kaiwa bakinta,abin yayi mata yawa tako ina,gefe daya ga maji da takejin nauyi matuqa,daya bangaren kuma ga uban 'yan girman kan nan da takejin yadda ya sanya mata ido sosai. A nutse yake juya lomar abincin a bakinsa,duk da cewa bawai wani yunwa yakeji ba,amma saboda ya faranta ran maji din yake cin abincin. Yadda ta takura din shi hakan yayi masa,yana karantarta tsaf ta gasan idanunshi,wanda ba lallai bane ka karanci hakan kai tsaye.
*HUGUMA*
* TABARMAR KASHI_*
Book 02 Page 16
Ko a fuska ba zaka taba zaton karantar tata yake ba,har zuwa lokacin da maji ta magantu
"'Ki saki ilkinki dani khadijatu,ina jinki ne tamkar moha da nadeeya,ke yanzun diyata ce halak malak,zan iya raba kowacce damuwa tawa da sirrina dake" garamin murmushi ta saki tana jinjina kai. Tabe baki yayi kadan yana matsawa gefe daga gaban kwanukan alamar ya qoshi,duk wadan nan abubuwan gani yakeyi kawai salo ne irin na mata wanda kaidinsu ba qarami bane,sai yanzu ya karanci dalilin da ya sanya dukkansu ta tafi da hankalinsu,cikin ransa yake gulmarta,ta wani sadda kai qasa,tamkar ba itace wannan mara kunyar ba me shegen tsiwa dake iya yarfa masa maganar da duk duniya ba macen data isa ta gaya masa bayan maji
"Ban baku kowacce gudunmawa ba ko?" Maji ta fada tana murmushi,a nutse toufeeq ya waiwaya ya dubeta
"Wacce iri maji?"