← Book details Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 127 OF 171

Sashe 127

Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Halan marowaciya ce ke ko?" Ya furta yana lullumshe mata ido, kamar wanda ke jin bacci. Bai jira tace komai ba ya kai bakinsa a nutse saman nata bakin. Bread din ya gutsira a tausashe, numfashinsa ya gauraye da nata,ya janye idanun a nutse yana tauna bread din, sai ya kama hannunta dake riqe da cup na tea din yakai bakinsa ya kurba a hankali. Kai ya jinjina,komai ta dafa yana da wani irin taste na daban da baya jinsa a ko ina. Ko daya hadiye dake gutsire sauran na bakinta yayi,sannu sannu sai gashi ya cinye mata bread din tas da tea din,ya saketa a nutse yana murmushi

"Thanks for this beautiful breakfast,i love you" yayi maganar yana tafiya da baya da baya idanunsa a kanta kamar bazai janye ba. Har yakai qofa sannan ya juya da hanzari ya qarasa ficewa yana jin shauqi na ratsashi.

A gurguje ta juya itama tana wucewa daki, ko ina cikin kanta na maimaita amsa kuwwar muryarsa cikin taushin nan nata da kalmarsa ta qarshe ta

"| LOVE YOU"

"He loves me?" Ta tambayi kanta tana tsaiwa gaban madubi tana duban fuskarta. Ta yaya zai fada sonta indai har da gaske ne? bayan dab take da kammala aikinta ta koma inda tafi wayo?, qwaqwalwarta ta daure tsam, daidai lokacin da kira ya shigo wayarta. Da sauri ta dauka tana komawa gefen gado, maji ce,kamar tasan kuwa a yau take shawarar kiranta,ta tabbatar itace hanya mafi sauqi da zata bi tayi tafiyarta a sirrance cikin kwanciyar hankali. Cikin kunya da nauyi ta daga kiran.

Kamilar muryar maji din ta ziyarci kunnenta da kyakkyawar sallama

"Ibnaty.....kaif einty"

"Barka da warhaka maji" sãahar din ta fada tana murmushi cikin kunya matuqa,kunyar da sai a yanzu takejinta ta gasken,irin kunyar dake wanzuwa tsakanin suruka da surukarta

"Barka kadai d'iyata,munyi waya da nadeeya tace kina sashenki,ina fatan komai lafiya,kuma komai yana tafiya cikin kiyayewar ubangiji ba tare da matsala ba?"

"Komai lafiya alhamdulillah"

"Nima ina gab da dawowa,wata matsala ce takeson faruwa fil usbu'il maadi(cikin satin da ya wuce) wala kin in sha Allah sa'arji'u ilaikum fi hazash shahr(saidai in sha

Allah zan dawo gareku cikin wannan watan)"

"Allah ya amince maji munyi kewarki, nahnu mushtaquna ilaiki(munyi kewarki)" murmushi ta saki cike da jin dadi

"Wa'ana aidan yabnaty (nima haka d'iyata)"

"Maji" ta kirata a sanyaye

"Na'am diyata,me yake faruwa?" Ta fada kai tsaye saboda yanayin kiran da taji tayi mata

"Akwai maganar da nakeso mui,nayi wani danyan hukunci ba tare da neman shawararki ba"

"Karkiji komai diyata,nayi imanin ba zaki taba cutar da kowa nawa ba,saboda addu'ata a kanki take,kuma Allah ya zabar mana ke,na tabbatar in sha Allah ke da duk abinda zakizo mana dashi alkhairi ne,gayamin kanki tsaye, menene?"

*HUGUMA*

* TABARMAR KASHI_*

Book 02 Page 40

"Na shirya tafiya da fadeela don yi mata aiki ta rabu da lalurar da take fama da ita a sirrance ba tare da ko mahaifinta va sani ba bare mutanen da muke rayuwa
tare dasu ba"

"Allahu akhbar " maji ta maimaita har sau uku
"Kamar tare dake muke wanann tunanin? wannan shine abinda na shirya aiwatarwa na farko bayan na dawo Nigeria,na baki goyon baya alf bil alf(dari bisa dari)"

"Amma maji, banason kowa ya sani saboda ina tsoron kada a sanya abun yaqi yiwuwa" kamilin murmushi maji ta saki

"Fauziyya hajiya qarama,ko ba ita kike tsoron kada ta sanya moha ya hana ba?,ina da labarin yadda tayi ruwa tayi tsaki ta hana duk wata maganar da za'a tayar akan a yiwa fadeela aiki,na bar zancen ne akan cewa ni daya zan iya aiwatar da aikin, koda ita din bataso,saboda nasan duk inda takai ga girman kaidinta,bata isa ta sanya moha ya hanani ba.….....har yanzu bakisan me fauziyya ta yiwa rayuwata ba,zauna da kyau diyata yau na gaya miki labarin da masu shekaru irin naki dake rayuwa tare dani basu sani ba" a sanyaye sãahar ta gyara zamanta saman gadon sosai, tun kafin taji komai daga bakin maji jikinta ya sanyaya,ba abinda take haskowa sai fuskar hajiya qarama a sannan.

* TUNA BAYA 1988 *

Mummunar faduwa gabanta yayi,wani irin hargitsatsen kallo daya watsa mata shi ya sanyata cikin rudani, batasan me tayi masa banda kulle qofa da tafiya da key din,kallon daya watsa mata yafi qarfin wannan laifin, kallo ne na zallar qasqanci da kuma tsana,tasan dai ranar yau lafiya galau suka rabu,ya fita cike da murna zai karbo upper dinsa aiki ya samu,suna ta murna dukkansu tare da saka ran fita daga tsanani zuwa sauqi, sai dukka gwiwarta tayi sanyi da irin nau'in kallon da yake jefa mata.

Kafin ta qaraso ainihin tsakar gidan sai wulgawar fauziyya ta gani, wadda kanta ke daure da bandeji da yayi tsatstsafar jini gaba daya daga samansa,ta nufeshi a gigice ta cukuikuyeshi tana neman mafaka a bayansa,bakinta na wani irin rawa na zallar toro da firgici take cewa

"Na shiga uku akh, gata nan ta dawo,don Allah ka boyeni,kada ka bari ta qaraso,wallahi zata qarasa illatani kamar yadda taci alwashi" tayi maganar tana wani irin haki da tawar jiki, kamar wadda tayi gudun kwana da wuni.

Baki kawai ta saki galala tana kallon fauziyya,qwaqwalwarta gaba daya ta rikice,me take nufi ne? saita maida dubanta ga bandejin kanta tana mamakin me ya sameta daga fitarta

"Bata isa tayi miki komai ba,a yau qarshen al 'amarinta yazo, muguntarta a kanki kuma ta qare!" Muryarsa mai zurfi dake fita da amon fushi ta fusgi hankalinta, saita maida dubanta kansu gaba daya, kwanyarta na sake rikicewa da salon maganganunsu da ba ganewa takeyi ba.

Ci gaba tayi da kallonsa, saidai ya zaro biron dake.
gaban aljihunsa ya kuma dauko takarda a daya aljihun nasa,ya bude kan biron cikin fusata. Cikin mamaki me yawa taga fauziyya ta kama biron ta riqe gam

"Me zakayi yaaya, ka rufamin asiri don Allah, kada kace zaka saketa saboda ni" ta fada hawaye na wanke mata fuska. "Ki saki fauziyya,duk mutumin da bayason jininka kaima baya qaunarka,ban ga amfanin zama da ita ba, baya ga tarin dimbin gori da maganganun data fada a kanmu" kuka sosai fauziyya keyi,ta kuma riqe abun rubutun taqi sakar masa tana bashi haquri, abinda yayi masifar daure tunanin SHIFA, me yasa fauziyyan dake burin afkuwar haka ita ke bada haqurin kada a saketa?.

"Kinci darajarta,ki dubi abun kunya wanda kike quntatawa shine yayi silar kubutar dake daga afkuwar wani mummunan abu a kanki" mamaki ya sake kasheta,kanta ya daure tamau, tama kasa cewa komai baki sake take kallonsa har ya miqe ya nufi hanyar soron gidan,har yanzu zallar bacin ran dake saman fuskarsa bata gushe ba. Har yakai bakin qofar sai kuma ya dawo,ya tsaya gaban fauziyya dake zube tana kuka

"Tashi ki wuce ciki". Bai barta ba har sai daya rakata cikin dakinta,ya dan jima ma a ciki kafin ya fito,zuwa sannan shifa ta ja jikinta da qyar ta wuce zuwa nata dakin clkin mawuyacin hali,tare da hasashen me yake ta faruwa da ita ne a rayuwarta haka? tun ranar da fauziyya ta sanya qafarta a gidan da nufin zama dasu,na wata shidda kawai ta samu kwanciyar hanakali bayan zuwan nata,daga bayan wannan watanni shidan bata sake samun sauqi ko salama ba.

Duk wani farinciki nata ta warwareshi tasss ba tare da tasan meye dalilin da yasa taketa aikata hakan ba. A iya saninta,mahaifiyarsu mahmud macace mai kirkin gaske da kowa ke yabonta bayan rasuwarta, zamanta da fauziyya na watanni shidan nan,zama ne na kyautata mata da kula da ita,saboda
tana mata kallon mahmud, mahmud kuwa ba zata manta da soyayyarsa a gareta ba, duk da cewa ba kowa cikin danginta ke son aurensu da shi ba, kasancewarsa shi din dan Nigeria ne, ita kuma 'yar Algeria ce, duk da shi dimma
fari ne tas kalar yarensu da idan ba fada kayi ba za'a
dauka Algerian ne shi dinma, kasancewar ya fita daga
tsatson SHUWA-ARAB wanda asalinsu dama larabawan ne.

Wani irin zama tayi cikin dakin cikin qunci da
kukan zuci,da Muhammad da nadeeya kowa kuka
yake, amma kusan hanakalinta yayi nisa a tunani,taji
alamun kuke sukeyi,amma saboda tsanar tunani da
damuwa bata farga da kukan da sukeyi ba,har sai da
taga fadowar fauziyya dakin kamar wadda aka jeho.
Kafin tayi kowanne irin tunani ta dauke nadeeya dake
tsaye daga bayanta tana kiran sunanta ta hau jijjigata.
Sallamar mahmud da shigowarsa cikin dakin shi ya ankarar da maji dalilin wannan shigowar ta fauziyya ta ba zata,iya saninta ko daya bata iya tayata wahalar yaran,zafi ko sanyi koda azumi akeyi ita zata yi korai dinta fauziyyan na daga kwance, saidai ta fito ta debi abincinta ta koma daki, idan ta gama sabgoginta kuma ta wanke jikinta tayi ficewarta unguwa,ba zata dawo ba sal ta daidaicin lokacin dawowar dan uwanta.
Hannu yasa ya karbi nadeeyan, fauziyyan da ta sake tara wani qwallan ta dubi yaran

"Ku tayani bawa maji dinku haquri, kada tayi fushi da ni,ni din marainiya ce,bani da kowa sai yayana sai ita da nake saka ran ta zamemin makwafin uwa" ta qarasa fada tana share qwallar munafurci. Gaba daya jinin jikin maji so yayi ya tsaya da harbawa,tabi fauziyya dake ci gaba da sharar qwalla da kallo

"Ni kadai na isa na tsaya miki, jeki abinki" mahmud ya fada yana miqa mata leda daya da ya shigo da ita ta takeaway. Har qasa ta durqusa ta saka hannu biyu ta karba tayi masa godiya tana fita.

Wani kallo ya juyo ya watsawa maji, ba komai idanunsa face zallar bacin rai da har yanzu bai gushe ba "Yau na gani da ido na,ansha gayamin yadda yake wulaqantar da yaran nan,hatta a wajen aiki ba wata
Kulawar kirki suke samu ba,saboda baqin hali tun daga waje nake jiyo kukansu amma kin gaza rarrashinsu,to daga rana irin ta yau na soke batun aikinki, ki zauna a gida ki kulamin da yarana da 'yar uwata" yayi maganar yana kamo toufeeq,ya zaunar dashi gefansa nadeeya na saman cinyarsa,ya bude musu daya takeaway din ya fara
basu.

Har yanzu jin komai take kamar a mafarki,sai a lokacin ta samu qwarin gwiwar waiwayawa gareshi
Chapter 127 · 0% Book details