Sashe 76
Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai wajen Tara na dare,dai dai lokacin kwanciya baccin fadeela sannan ta shirya ta fita don tayi mata shirin bacci,aikin kulawar ya rage mata sosai tunda ko yaushe nadeeya na kula mata da ita koda bata a kusa. Qaramin hijab ta zura ta fito a dakin.
Kasancewar qofar dakin bata kammala rufewa ba tun bata gama shiga ba ta fahimci video call sukeyi,duka ita da fadeelan na samon gado sunyi rub da ciki,sun sanya system din nadeeya din a gaba suna faman surutu.
*HUGUMA*
*_TABARMAR KASHI_*
67
"'yauwa maji....gata nan" nadeeya ta fada
tana murmushi idanunta akan fuskar sãahar.
Tsarguwa kawai tayi,tasan hirarta akeyi
kenan batasan itakam wanne irin gauna
nadeeya da fadeela ke mata ba da basa gajiya
da ambatonta ba a duk wurin da suka zauna
ba
"Marhaban da ita‚ta qaraso mu gaisa" wata
nutsatsiyar murya dake dauke da accent na
arabic ya fidda amon maganar.
Bata da wani zabi,tunda taji abinda ta
fada,uwa uba sunan maji ba bago bane a kunnuwanta,suna ne da a galla tana jinsa daga bakin nadeeya da fadeela yafi sau uku a rana.
A nutse ta taka zuwa gefan gadon,nadeeya ta zauna sosai tana juyar mata da fuskar system
din zuwa tata fuskar
"Ma sha Allah, intee jameela" murmushi sãahar ta danyi,tana dan sadda da kanta daga kallon tata kyakkyawar fuskar,fuskar da shekaru suka fara bayyana samanta,amma kuma bisa dukkan alamu kyakkyawar kulawa da ingatacciyar rayuwar da take ciki bai bar tsufa ya bayyana ba. Wani irin kyau me daukan hankali wanda dukka kamanninta sune tsaf bisa fuskar nadeeya a yanzu
"Ki dayra,wesh wella famille?" Ta tambayeta da tantagaryar labarancin larabawan Algeria
"Maii namu larabcin fa ba irin naku bane"
nadeeya tayi magana da shagwabar da sãahar
bata taba gani tayi ba
"Ya salam, ina mantawa ne,kina lafiya? ya kuma iyalinki?" Murmushi ta sake
"Alhamdulillah, da fatan kina lafiya"
"Alhamdulillah, Allah yayi albarka,naji dadin ganinki,na san sunanki da kyau,amma bansan fuskarki ba" maii ta fadi mayalwacin murmushin dake dauke da nutsuwarta ta halitta na fita a fuskarta. Har qasan zuciyarta tana jin dadin yadda idanunta ke iya hango sauyi daga jikartata,fadeela rayuwarta ce,tana mata wani irin so da zata iya cewa soyayyar da takewa toufeeq da nadeeya ce tayi tsuntsuwa ta koma kanta,fadeela ita daya ce makamin data tabbatar a yanzun dukkan maqiyinta dake Nigeria zai iya amfani dashi ya cutatar da ita,cutarwar kuma ta risketa kai tsaye har gasarta Algeria. Cikin dabara ta sulale ta wuce wardrobe din fadeela tana fidda mata kayan bacci,saidai hakan bai hanata jin wasu hirarrakin nasu sama sama,duk da bata dora hankalinta a kai ba.
Tana fita daga closet din taji an daneta an riqeta qam qam,kafin tace komai muryar fadeela ta ratsata
"Albishir dinki aunty nanny" dariya taso kubce mata,saboda yadda tayi hausar ma kanaji kasan ba iya karin maganar tayi ba,saita zura hannu ta kamota ta dawo da ita gabanta
"Wannan hausa taki....to ba laifi goro"
"Ni bana cin goro,amma dai..
.. ki tayani
murna,am very happy today,
next week abby zai dawo" sai ta qyalgyale da dariya tana nuna zallar murnarta. Da kyau sãahar ta kama hannuwan fadeela cikin nata tana tayata murmushin,duk da hakanan taji zuciyarta ta harba ba tare da wani dalili ba
"Am so happy nima fadee,congratulations" rungume sãahar din tayi,itama sai ta buda hannayenta ta sanyata sosai a jikinta tana tayata murnar.
*******Cikin kwanakin gaba daya shire shiryen dawowarsa akeyi cikin gidan,nadeeya gaba daya ta kasa zama,ita da fadeelan batasan waye yafi wani murna da zumudi ba,itadai 'yar kallo ce,amma kusan kullum sai an fita shopping na dawowar abbyn fadeela.
Tun tana janye jiki har nadeeya ta sakata tsundum a harkar,tunda ta fahimci sãahar din ta iya mota ta hanata sukuni,duk inda zasu saita marairaice mata akan tayi drive nasu
Zuwa gurin,hakanan ba yadda ta iya take karba su tafi.
Sai a sannan ra fahimci siyayyar da suke fita sukeyi,a nata gurin tsabar son yawo ne irin na nadeeya,qananun kayayyakin amfani dake sashensa ake canzawa,abinda taji hajiya qarama na cewa nadeeyan tayi magana da company suzo su sauya masa komai kamar yadda aka saba,amma son yawo dai yasa tace da kanta zata siyo komai. Duk da ko sau daya bata taba takawa sassan sa ba,amma bataga wani abu daya baci ko ya lalace da za'a sauyashi ba. Kamar nadeeya tasan me take tunani, ranar suna tafe cikin ShopRite tana zaban wasu turarukan daki na ruwa masi shegen tsada,ta dan ja tsaki kadan ta waiwayo tana duban sãahar dake amsa wayar afifa
"Aunty N,don Allah tayani zaben turarukan nan mana,yaa toufeeq akwai shi da taste a zabi inason kome na siyo ya zama unique" zare wayar taki daga kunnenta tana duban nadeeya,duk lokacin data ambaci sunan
TOUFEEQ sai taji gabanta ya fadi,ranta kuma ya baci
"Basu isa bane haka sis nadeeya?" Ido tadan fidda
"Da saura,indai yaa ya dawo daga tafiya muddin ya wuce one month yakai two to sai an canza masa irin wadan nan kayayvakin" batace komai ba sukayi sallama da afifa,ta tako gurin zuciyarta na tuna mata maganganun da sukayi da afifa yanzu akan mahmud. Ta fuskanci ta garfi da yaji mahmud din yakeson kafa kanshi a gidansu tare da maida kansa dan gida,to amma zata gani indai ana siyan so a dole.
Sosai ta nutsu ta zaba wasu kalolin, wadanda ita kanta nadeeya sai data yaba
"Wow,gaskiya u are the best selector" murmushi ya qwacewa saahar din,saita koma gefe tana jiran su kammala.
Tana ganin yadda suka koma zaben kayan da zasu saka ranar da abby din zai dawo, nadeeyan tayi tayi tazo ta zaba itama,saita girgiza musu kai alamun a'ah,fadeela ta marairaice kamar zata saki kuka,ta rige hannunta kam
"'Please anty N"ta fada itama kamar yadda taji nadeeya ta koma ce mata
"Okay,kije ki zabarmin fadee na,koma meye i will accept it" da haka ta samu ta barta,bayan sun kammala kuwa sai gasu da leda wai duka kayanta ne na tarar abby
"Wai wai,sis nadee, thank you, amma kayan is too much gaskiya" murmushi ta sake
"'Wallahi Allah ko?" Ta fada tana duban sãahar
"Ina jinki ne kamar wadda muka fito ciki daya da ita,banajin banbanci tsakaninki da yaa toufeeq "
ambatar sunan ya sake sanyata lumshe idanu sannan kuma ta budesu, Allah ya sani bata qaunar jin sunan sam,saidai don babu yadda zatayi,shi daya ne tal ambaton sunansa yake sanyata jin faduwar gaba.
A falonsu na biyu ta barsu baaba ramatu tana tayasu duba siyayyar ta shige dakinta ta watsa ruwa,sannan ta wuce kitchen don ta samar musu da abinda zasuci,saboda fafur sukaqi girkin zuwaira,sal ya zamana ita ke musu girki su hudun,nadeeya fadeela ita sai baaba ramatu. Ta sauya musu abinci sosai,daga girke girken fararen fara zuwa abinciccikan hausawa da abincin yaran maamanta wato buzaye,sai na yaren abbanta wato shuwa,duk da har yanzun bata tantance yarensu ba su din, amma kana kallonsu kasan babu ta inda suka hada Jini da HAUSA banda yaren dake bakinsu,a ido kuma sai ka rantse zo na kasheka da hausan basu sani ba. Ita dinma mutane da yawa kallon da suke mata kenan.
Tun a ranar suka gama tsara bin guard airport su taho da abbyn fadeelan, harda sunanta suka jefa a ciki, murmushi tayi can qasan zuciyarta tace "Saboda gayyar sodi" amma a zahiri batace dasu dai komai ba,ita haka kawai take jin dama me gidan da suketa zumudin dawowar tasa zaiyi zamansa a can,cikin gidan yaci gaba da kasancewa iya yasu yasu mata.
********Ana gobe zai dawo nadeeya ta hanata sakat,duk da yana da cook dinsa permanent da yake masa girke girke tare da tanadar dukkan abinda yakeso,qwararren cook daya qware waien sarrafa nau'ikan abinci,cook din da ake biya da kudade masu nauyi,samfurin albashin wani ma'aikacin na wata guda…...amma duk da haka nadeeya sai data shirya nata dafe dafen
"Yaa moha ya jima baici abinci na ba,zan bashi mamaki wannan karon,zaiji canjin taste" yadda nadeeya keta sanyata a abubuwa tana zugewa yasa a wannan gabar don kada taji babu dadi ta karba ragamar yin fried rice.
Saidai kuma a daddafe ta gama hada kayan bugata ta ajiye,saboda wani ciwon kai da ya saukar mata lokaci guda,sauqin abun taji suna maganar evening flight ne,sai tasa a ranta zuwa goben xata warware in sha Allah. Ba wanda ta gayawa a cikinsu don kada su sanya damuwarsu a kanta,ta kawowa walwala da farincikin da suke ciki naqasu,sai ta wuce daki kawai ta kwanta abinta.
Washegari ta kammala komai akan lokaci,duk da har lokacin tana dannewa ne kawai amma bata dawo dai dai ba,tana gamawa ko wanka bata iyayi ba ta koma gado ta nade tana sauke numfashin,sauqin abu daya tana fashin sallah,a haka bacci yayi nasarar daukarta.
Da zumudinta fadeela data gama shirinta tsaf ta shigo dakin,tana tsammanin ganin sãahar ta shirya,sai ta sameta akwance tana bacci, zuciyarta a karye fuska a jagale ta koma falon
"Ta gama shiryawa?" Nadeeya ta tambayi fadeelan tana qoqarin cire wayarta daga chargy
"Sister nadeeya,bacci ma fa anty N din takeyi"
"Bana tunanin lafiya qalau take gaskiya, kamar na fahimci bata da lafiya" baaba ramatu ta fada fuskarta na nuna alhini. Take damuwa ta bayyana saman fuskarsu gaba daya
"Rabu da ita fadeela muje,may be ma jiyan bata samu isashen bacci ba.na fuskanci kamar tana da zurfin ciki"
"Alamu sun nuna kam" baaba ramatu ta maidawa nadeeya amsa sai suka fice baaba ramatun na rakasu da addu'a. Har sai da suka garasa ficewa ta dauke idanunta tana girgiza kai sai wasu qwalla masu dumi suka biyo kuncinta,ta saka gefan yalwataccen mayafin jikinta ta goge sannan taci gaba da abinda takeyi cikin falon.
/
*******Cikin tarin nutsuwa kamewa da kuma kwarjinin nan nashi yake saukowa daga cikin jirgin tare da jerin matafiya da suke jerin first class.
Ba abinda zaka fara hangowa sai
kyakkyawar farar fatarsa din nan me surkin ja ja,wadda bata cika wani fari me yawa sosai ba saboda surkin jaa din da take dashi.
Sanye yake da button up shirt me dogon hannu cream color dake da maballai gun metal color hakanan slim fit trouser din jikinsa me sulbi ya kasance kalar button din rigar tasa,wasu lafiyayyun loafers ne a gafarsa kalar trouser din jikinsa,nannunsa daure da tsadajjen agogon rolex daya fito sosai sakamakon tattare dogon hannun rigar tasa da yayi kadan ya rage yakai gwiwar hannunsa.
Kasancewar qofar dakin bata kammala rufewa ba tun bata gama shiga ba ta fahimci video call sukeyi,duka ita da fadeelan na samon gado sunyi rub da ciki,sun sanya system din nadeeya din a gaba suna faman surutu.
*HUGUMA*
*_TABARMAR KASHI_*
67
"'yauwa maji....gata nan" nadeeya ta fada
tana murmushi idanunta akan fuskar sãahar.
Tsarguwa kawai tayi,tasan hirarta akeyi
kenan batasan itakam wanne irin gauna
nadeeya da fadeela ke mata ba da basa gajiya
da ambatonta ba a duk wurin da suka zauna
ba
"Marhaban da ita‚ta qaraso mu gaisa" wata
nutsatsiyar murya dake dauke da accent na
arabic ya fidda amon maganar.
Bata da wani zabi,tunda taji abinda ta
fada,uwa uba sunan maji ba bago bane a kunnuwanta,suna ne da a galla tana jinsa daga bakin nadeeya da fadeela yafi sau uku a rana.
A nutse ta taka zuwa gefan gadon,nadeeya ta zauna sosai tana juyar mata da fuskar system
din zuwa tata fuskar
"Ma sha Allah, intee jameela" murmushi sãahar ta danyi,tana dan sadda da kanta daga kallon tata kyakkyawar fuskar,fuskar da shekaru suka fara bayyana samanta,amma kuma bisa dukkan alamu kyakkyawar kulawa da ingatacciyar rayuwar da take ciki bai bar tsufa ya bayyana ba. Wani irin kyau me daukan hankali wanda dukka kamanninta sune tsaf bisa fuskar nadeeya a yanzu
"Ki dayra,wesh wella famille?" Ta tambayeta da tantagaryar labarancin larabawan Algeria
"Maii namu larabcin fa ba irin naku bane"
nadeeya tayi magana da shagwabar da sãahar
bata taba gani tayi ba
"Ya salam, ina mantawa ne,kina lafiya? ya kuma iyalinki?" Murmushi ta sake
"Alhamdulillah, da fatan kina lafiya"
"Alhamdulillah, Allah yayi albarka,naji dadin ganinki,na san sunanki da kyau,amma bansan fuskarki ba" maii ta fadi mayalwacin murmushin dake dauke da nutsuwarta ta halitta na fita a fuskarta. Har qasan zuciyarta tana jin dadin yadda idanunta ke iya hango sauyi daga jikartata,fadeela rayuwarta ce,tana mata wani irin so da zata iya cewa soyayyar da takewa toufeeq da nadeeya ce tayi tsuntsuwa ta koma kanta,fadeela ita daya ce makamin data tabbatar a yanzun dukkan maqiyinta dake Nigeria zai iya amfani dashi ya cutatar da ita,cutarwar kuma ta risketa kai tsaye har gasarta Algeria. Cikin dabara ta sulale ta wuce wardrobe din fadeela tana fidda mata kayan bacci,saidai hakan bai hanata jin wasu hirarrakin nasu sama sama,duk da bata dora hankalinta a kai ba.
Tana fita daga closet din taji an daneta an riqeta qam qam,kafin tace komai muryar fadeela ta ratsata
"Albishir dinki aunty nanny" dariya taso kubce mata,saboda yadda tayi hausar ma kanaji kasan ba iya karin maganar tayi ba,saita zura hannu ta kamota ta dawo da ita gabanta
"Wannan hausa taki....to ba laifi goro"
"Ni bana cin goro,amma dai..
.. ki tayani
murna,am very happy today,
next week abby zai dawo" sai ta qyalgyale da dariya tana nuna zallar murnarta. Da kyau sãahar ta kama hannuwan fadeela cikin nata tana tayata murmushin,duk da hakanan taji zuciyarta ta harba ba tare da wani dalili ba
"Am so happy nima fadee,congratulations" rungume sãahar din tayi,itama sai ta buda hannayenta ta sanyata sosai a jikinta tana tayata murnar.
*******Cikin kwanakin gaba daya shire shiryen dawowarsa akeyi cikin gidan,nadeeya gaba daya ta kasa zama,ita da fadeelan batasan waye yafi wani murna da zumudi ba,itadai 'yar kallo ce,amma kusan kullum sai an fita shopping na dawowar abbyn fadeela.
Tun tana janye jiki har nadeeya ta sakata tsundum a harkar,tunda ta fahimci sãahar din ta iya mota ta hanata sukuni,duk inda zasu saita marairaice mata akan tayi drive nasu
Zuwa gurin,hakanan ba yadda ta iya take karba su tafi.
Sai a sannan ra fahimci siyayyar da suke fita sukeyi,a nata gurin tsabar son yawo ne irin na nadeeya,qananun kayayyakin amfani dake sashensa ake canzawa,abinda taji hajiya qarama na cewa nadeeyan tayi magana da company suzo su sauya masa komai kamar yadda aka saba,amma son yawo dai yasa tace da kanta zata siyo komai. Duk da ko sau daya bata taba takawa sassan sa ba,amma bataga wani abu daya baci ko ya lalace da za'a sauyashi ba. Kamar nadeeya tasan me take tunani, ranar suna tafe cikin ShopRite tana zaban wasu turarukan daki na ruwa masi shegen tsada,ta dan ja tsaki kadan ta waiwayo tana duban sãahar dake amsa wayar afifa
"Aunty N,don Allah tayani zaben turarukan nan mana,yaa toufeeq akwai shi da taste a zabi inason kome na siyo ya zama unique" zare wayar taki daga kunnenta tana duban nadeeya,duk lokacin data ambaci sunan
TOUFEEQ sai taji gabanta ya fadi,ranta kuma ya baci
"Basu isa bane haka sis nadeeya?" Ido tadan fidda
"Da saura,indai yaa ya dawo daga tafiya muddin ya wuce one month yakai two to sai an canza masa irin wadan nan kayayvakin" batace komai ba sukayi sallama da afifa,ta tako gurin zuciyarta na tuna mata maganganun da sukayi da afifa yanzu akan mahmud. Ta fuskanci ta garfi da yaji mahmud din yakeson kafa kanshi a gidansu tare da maida kansa dan gida,to amma zata gani indai ana siyan so a dole.
Sosai ta nutsu ta zaba wasu kalolin, wadanda ita kanta nadeeya sai data yaba
"Wow,gaskiya u are the best selector" murmushi ya qwacewa saahar din,saita koma gefe tana jiran su kammala.
Tana ganin yadda suka koma zaben kayan da zasu saka ranar da abby din zai dawo, nadeeyan tayi tayi tazo ta zaba itama,saita girgiza musu kai alamun a'ah,fadeela ta marairaice kamar zata saki kuka,ta rige hannunta kam
"'Please anty N"ta fada itama kamar yadda taji nadeeya ta koma ce mata
"Okay,kije ki zabarmin fadee na,koma meye i will accept it" da haka ta samu ta barta,bayan sun kammala kuwa sai gasu da leda wai duka kayanta ne na tarar abby
"Wai wai,sis nadee, thank you, amma kayan is too much gaskiya" murmushi ta sake
"'Wallahi Allah ko?" Ta fada tana duban sãahar
"Ina jinki ne kamar wadda muka fito ciki daya da ita,banajin banbanci tsakaninki da yaa toufeeq "
ambatar sunan ya sake sanyata lumshe idanu sannan kuma ta budesu, Allah ya sani bata qaunar jin sunan sam,saidai don babu yadda zatayi,shi daya ne tal ambaton sunansa yake sanyata jin faduwar gaba.
A falonsu na biyu ta barsu baaba ramatu tana tayasu duba siyayyar ta shige dakinta ta watsa ruwa,sannan ta wuce kitchen don ta samar musu da abinda zasuci,saboda fafur sukaqi girkin zuwaira,sal ya zamana ita ke musu girki su hudun,nadeeya fadeela ita sai baaba ramatu. Ta sauya musu abinci sosai,daga girke girken fararen fara zuwa abinciccikan hausawa da abincin yaran maamanta wato buzaye,sai na yaren abbanta wato shuwa,duk da har yanzun bata tantance yarensu ba su din, amma kana kallonsu kasan babu ta inda suka hada Jini da HAUSA banda yaren dake bakinsu,a ido kuma sai ka rantse zo na kasheka da hausan basu sani ba. Ita dinma mutane da yawa kallon da suke mata kenan.
Tun a ranar suka gama tsara bin guard airport su taho da abbyn fadeelan, harda sunanta suka jefa a ciki, murmushi tayi can qasan zuciyarta tace "Saboda gayyar sodi" amma a zahiri batace dasu dai komai ba,ita haka kawai take jin dama me gidan da suketa zumudin dawowar tasa zaiyi zamansa a can,cikin gidan yaci gaba da kasancewa iya yasu yasu mata.
********Ana gobe zai dawo nadeeya ta hanata sakat,duk da yana da cook dinsa permanent da yake masa girke girke tare da tanadar dukkan abinda yakeso,qwararren cook daya qware waien sarrafa nau'ikan abinci,cook din da ake biya da kudade masu nauyi,samfurin albashin wani ma'aikacin na wata guda…...amma duk da haka nadeeya sai data shirya nata dafe dafen
"Yaa moha ya jima baici abinci na ba,zan bashi mamaki wannan karon,zaiji canjin taste" yadda nadeeya keta sanyata a abubuwa tana zugewa yasa a wannan gabar don kada taji babu dadi ta karba ragamar yin fried rice.
Saidai kuma a daddafe ta gama hada kayan bugata ta ajiye,saboda wani ciwon kai da ya saukar mata lokaci guda,sauqin abun taji suna maganar evening flight ne,sai tasa a ranta zuwa goben xata warware in sha Allah. Ba wanda ta gayawa a cikinsu don kada su sanya damuwarsu a kanta,ta kawowa walwala da farincikin da suke ciki naqasu,sai ta wuce daki kawai ta kwanta abinta.
Washegari ta kammala komai akan lokaci,duk da har lokacin tana dannewa ne kawai amma bata dawo dai dai ba,tana gamawa ko wanka bata iyayi ba ta koma gado ta nade tana sauke numfashin,sauqin abu daya tana fashin sallah,a haka bacci yayi nasarar daukarta.
Da zumudinta fadeela data gama shirinta tsaf ta shigo dakin,tana tsammanin ganin sãahar ta shirya,sai ta sameta akwance tana bacci, zuciyarta a karye fuska a jagale ta koma falon
"Ta gama shiryawa?" Nadeeya ta tambayi fadeelan tana qoqarin cire wayarta daga chargy
"Sister nadeeya,bacci ma fa anty N din takeyi"
"Bana tunanin lafiya qalau take gaskiya, kamar na fahimci bata da lafiya" baaba ramatu ta fada fuskarta na nuna alhini. Take damuwa ta bayyana saman fuskarsu gaba daya
"Rabu da ita fadeela muje,may be ma jiyan bata samu isashen bacci ba.na fuskanci kamar tana da zurfin ciki"
"Alamu sun nuna kam" baaba ramatu ta maidawa nadeeya amsa sai suka fice baaba ramatun na rakasu da addu'a. Har sai da suka garasa ficewa ta dauke idanunta tana girgiza kai sai wasu qwalla masu dumi suka biyo kuncinta,ta saka gefan yalwataccen mayafin jikinta ta goge sannan taci gaba da abinda takeyi cikin falon.
/
*******Cikin tarin nutsuwa kamewa da kuma kwarjinin nan nashi yake saukowa daga cikin jirgin tare da jerin matafiya da suke jerin first class.
Ba abinda zaka fara hangowa sai
kyakkyawar farar fatarsa din nan me surkin ja ja,wadda bata cika wani fari me yawa sosai ba saboda surkin jaa din da take dashi.
Sanye yake da button up shirt me dogon hannu cream color dake da maballai gun metal color hakanan slim fit trouser din jikinsa me sulbi ya kasance kalar button din rigar tasa,wasu lafiyayyun loafers ne a gafarsa kalar trouser din jikinsa,nannunsa daure da tsadajjen agogon rolex daya fito sosai sakamakon tattare dogon hannun rigar tasa da yayi kadan ya rage yakai gwiwar hannunsa.