Sashe 61
Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Tunda har kuna da bakin kare kanku,ai waqa a bakin me ita tafi dadi" saita fidda waya tana kiran anty farheen
"Muna hanya afifa,muna gab da shigowa layin"
"Saikun qaraso" sai ga juya gasu dr mamman
"Abba,don Allah ku jira minti uku,ga raba gardamar nan isowa" jin kalmar afifa ta qarshe ta kada hanjin cikin momee,zatonta ya bata jami'an tsaro kawai suka kira musu kai tsaye,sai ta kama hannun adam tana cewa
"Tashi mu tafi,Allah zai saka mana da wannan qazamin qazafin da sukayi maka saboda kana auren diyarsu"
"Ina zaku?,ku koma ku zauna,ai bakwa tafi muna zarginku ba,gwara a warware gaskiya ko hajiya?" Cewa dr mamman girema.
Jikinta ne ya dauki rawa ta fara kame kame,saidai kafin ta dire kame kamen nata sallamar sãahar ta dauki hankalin kowa.
Sanye cikin wani lallausan yadi da aka yiwa dinkin doguwar riga,da gyale mahadinsa,fuskarta har yau bata cika ba a yadda take a baya,saidai sassanyan kyan nan da baya gushewa kwance saman fuskar tata. Akwai alamu na samun nutsuwa a tattare da ita,sabanin satittikan baya da dukka wata natsuwa tayi qaura daga rayuwarta,ake shirin haukatata,a maidata mahaukaciya zalla,idan ta yiwu ma yazo da qarar kwana,bataga abinda zai hanata ta baqunci lahira ba.
Cikin azama tare da son nunawa duniya shi din wankakke ne,kuma masoyi ga matarsa ya miqe cikin zallar mamaki ya nufeta yana qwala kiran sunanta. Rungumeta yayi nufin yi,saidai kafin yakai ga aikata hakan ya samu tsarabar wani lafiyayyen mari saman fuskarta,sannan ta tattara dukka qarfin data shigo dashi ta ingizashi baya ya fada saman momee dake zaune cikin kaduwa da tsurewa.
Zumbur ya miqe yana shafa wajen,sannan ya maida dubansa a kanta,sanda take tsaye ta kafeshi da fararen manyan idanunta dake dauke yau din da wani irin matsanancin fushi da bai taba ganin irinsa tattare da ita ba
"Baki warke bane sãahar?,subhanallahi"
"Kaine zaka shiga taka haukar yanzun nan,mayaudari maciyin amana,ina neman tsarin Allah daga kai" sai ta fashe da kuka ta soma sulalewa a gurin zata zauna,anty farheen ta riqeta da kyau tana bata baki. Tuni maama ta qaraso bayan ta tabbatar ba mafarki takeyi ba,ta rungume 'yarta tsam tana jero addu'o'in godiya ga Allah
"Ya kamata kowa ya samu waje ya zauna" yaa Saifullahi ya magantu cikin nutsuwarsa,domin ya karanci akwai babban al'amari dake shirin faruwa,komai ya fara bayyanar masa saman fuskar adam da babarsa,sannan ya akayi sãahar take a gidan muhyiddeen duk da tsahon lokacin da aka dauka ana nemanta ba tare da kowa ya sani ba?,ga adam da momee suna matsawa daga bakin qofa?,tamkar yaa zaid ya lura,sai ya matsa yayiwa kansa mazauni daga can hanyar qofar,suka zamana a tsakiya.
A nutse afifa ta qaraso tsakiyarsu ta dire jakar. Lokacin da idanun adam suka sauka a kan jakar sai ga fitsari ya balle masa yana daga zaunen,zazzafar gudawa ta soma qoqarin kufce masa amma ya matseta da kyau,gurbatacciyar ziciyarsa tana gaya masa akwai sauran dama adam,kada ka karaya,muddin baka amsa ba ba wanda ya isa ya tilastaka,koda kuwa a kotu ne.
A gaban kowa sãahar ta matso,ta daga jakar ta zazzage komai ya tarwatse a qasa,wani zazzafan kuka ya taso mata,amma ta danneshi. Daya bayan daya ta soma basu labarin yadda suka fara hadaka a rayuwarsu,yarjajeniyar rashin daukan ciki,canjin halayensa,kamashi da tayi a waya da zuba mata tablet da yayi na zubda ciki,bayyanar ha'incin da yake mata ba tare amma data kama sunan raihanatu ba,azabar daya dinga gana mata har zuwa sanda Allah yayi fitarta daga gidan da taimakon afifa da kuma raihanatu. Kamar wani mahaukacin zaki ya miqe ya soma zage zage,yaa zaid baisan sanda yasa qafa ya kwasheshi ba cikin matsanancin fushi,sai gashi kif a qasa
"Idan ka sake mana magana sai na cire maka harshe" kota ina jikin momee rawa yake,duk sauran qwarin gwiwar da take dasu sun kwaranye sunbi ruwa,don itama wasu abubuwan batasan dasu ba.
Jakar ta fara musu bayani,tana zazzage abubuwan ciki tana nunawa kowa,sai maama ta kasa daurewa,ta rufe fuskarta da hannunta kuka mara sauti yana qwace mata. Duka duka nawa sãahar din take da har zata fuskanci irin wannan cin zarafin cin fuska da zallar cin amana daga gurin da namiji?,ko ita data kawota duniya bata taba fuskantar wani abu da yayi kamanceceniya da wannan ba
"Duk abinda ta fada gaskiya ne,ni shaida ce" muryar raihanatu ta ratsa falon,sai suka waiwaya suna kallonta, idanunta cike fal da qwallar tausayin sãahar din,don itama wasu abubuwan sai yanzu takeji.
Mamaki ya cika momee qwarai,wato raihanatu zata zame mata 'yar kuka?,ta raini makashiyarta?
"Ki daina mamaki momee,ko kina tunanin bansan ba don Allah kike riqe dani ba?,bayan bautar da nake muku kina lissafin sake maidani machine din tatsar kudinki?, bayan kin cinye dukka abinda mahaifiyata ta mallaka,tun tana raye bata da bakin musa miki?" Maganar ta sake zuwarma momee a bazata,lokaci guda ta nemi sukurkuta mata runani,ya akayi yarinyar tasan wannan
"ni zaki butulcewa raihanatu?"
"Dalla malama ki rufewa mutane baki" yaa Saifullahi ya fada cikin muguwar tsawa,ransa baqiqqirin,tamkar zai kifawa momee din mari,hannu Dr mamman ya daga masa,saboda shi wani abuma ya tsaye masa a wuya ya kasa magana,idanunsa qirrr saman fuskar adam,yana tuna girma da nauyin karamcin da ya yiwa rayuwarsa,tarin alkhairai wanda ko sãahar da take matarsa ya hana ya gaya mata,yakance masa
"Nayi maka ne fisabilillahi saboda Allah,ko ummin abba banaso ta sani,kasan su mata,wani qaramin tunani garesu,qanqani abu zai hadaka dasu sai su goranta maka".
Sam basu farga ba,ashe tuni yaa zain yayi kiran mopol,kafin kace wani abu sai isowarsu akaji da sanyo kansu cikin gidan
"Waye yayi hakan a cikinku?" Dr mamman ya tambaya
"Kayi haquri abba,nine" ya zaid ya fada yana miqewa,yanason a hukunta masa adam da mahaifiyarsa hukunci Mafi tsanani da radadi,irin hukuncin da har su koma ga Allah ba zasu mance dashi ba.
"Amma ina zaune ba zaka fara neman shawarata ba zain?"
"Kayimin afuwa abba" yana gama fada ga fita,cikin second biyar suka cika falon.
"Wait please" ya Saifullahi ya fada,ya miqa hannu ya ciro paper,ya zaro pen daga aljihunsa ya dorawa adam da ake qoqarin cukuikuyewa
"Maza rubuta mata takardarta" kai ya girgiza cikin taurin zuciya da taurin kai
"Matata ce,kuma ina sonta har yanzu,don haka bazan saketa ba,saidai......." Bai qarasa fada ba ya Saifullahin ya daukeshi da wani kyakkyawan mari
"Mu zaka gayawa maganar banza da wofi?,wato saboda baka daku ba har kana da qwarin gwiwar yi mana musu ko?" Duk da marin amma sai ya sake girgiza kai
"Saidai ta mutu da igiyar aure na"
"Ba zata mutu ba kuwa,saboda mudin ba jahilai bane,kawai kotu akwai shari'a kuma" ya muhyiddeen da mamakin adam ke sake kasheshi ya fada. Saidai yana rufe bakinsa mopol din ya saukewa adam din wani irin zazzafar mahangurba da lokaci guda ta sauke masa jini ta hanci da labbansa,ta kuma tara masa wani lafiyayyen jini a gefen idanunsa. Ihu momee ta saki tana neman taimakon wai za'a kasheta ita da danta
"Saketa,ka saketa nace karsu kasheka baka da gata" koda momee din bata fada ba zai rubuta,shi kadai yasan kalar azabar da yaji,idanunsa a rurrufe ya rubuta mata saki daya. A fusace ya Saifullahin ya duba
"Don ubanka qarashe mata sauran biyun" dr mamman ne da nasa mamakin ya qarasa daskarar dashi ya daga masa hannu
"Rabu dashi" ya basu umarni a taqaice,daa yaso ya hana a tafi dasu,amma yadda suka nuna rashin nadama kwata kwata bisa fuskarsu yasa ya kasa hana mopol din tafiya dasu.
"So nake a azabtarmin dasu yadda ya kamata,a sassaba masa kamanni shida uwarsa,banason kowa yasan inda suke,kada kuma a daga musu qafa ko na kwana daya,zamuyi waya" yacewa da shugabansun
"Karka damu,sakamakon mummuna ai mummuna ne" shima ya fada cike da jin takaicin adam da uwarsa.
Ko minti biyar basu qara a gidan ba suka tattara nasu ya nasu suka fice a gidan,sãahar ce tabi raihanatu da kallo wadda ta hada nata kayan ta fara yin titi
"Abba bata da kowa a qasar nan,kuma ko yanzun bata da wajen zama,dama suke riqe da ita,na tabbatar kuma ba zasu ci gaba da riqonta ba" wannan yasa suka dauki raihanatun,abban kuma ya tabbatarwa sa sãahar zai kula da nauyinta da rayuwarta,zuwa gaba kadan kuma zasuje ghana a binciko danginta na qwarai,don susan irin riqon da momee tayi mata. Ajiyar zuciya sãahar ta sauke
"Allah yasa su iya wani abu,saboda momee ta cikasu da kyaututtuka,a yanzu kuwa lalacewa ta tattaru a cikin dangi,duk lalacewarka izgilancinka da rashin ganin girman mutane,taka mutane da mugunyar halinka kaida iyalinka,muddin kana ungo ungo,sai idanun 'yan uwa su rufe daga aibunka,a rasa wani tsayayyen da idan kayi ba daidai ba za'a tsaya a tsawatar maka a kuma hukuntaka dai dai da laifinka" kai abban ya jinjina,maganar sãahar tana kan hanya
"Wannan shine yake kawo lalacewar zumunci da tabarbarewarsa,dole sai an hadu za'a gyara,dole sai an hadu an hukunta me qarfi ko mara qarfi,ya zamana kowa baifi qarfin doka ba,Allah ya kyauta,yasa mufi qarfin zukatanmu"
"Muna hanya afifa,muna gab da shigowa layin"
"Saikun qaraso" sai ga juya gasu dr mamman
"Abba,don Allah ku jira minti uku,ga raba gardamar nan isowa" jin kalmar afifa ta qarshe ta kada hanjin cikin momee,zatonta ya bata jami'an tsaro kawai suka kira musu kai tsaye,sai ta kama hannun adam tana cewa
"Tashi mu tafi,Allah zai saka mana da wannan qazamin qazafin da sukayi maka saboda kana auren diyarsu"
"Ina zaku?,ku koma ku zauna,ai bakwa tafi muna zarginku ba,gwara a warware gaskiya ko hajiya?" Cewa dr mamman girema.
Jikinta ne ya dauki rawa ta fara kame kame,saidai kafin ta dire kame kamen nata sallamar sãahar ta dauki hankalin kowa.
Sanye cikin wani lallausan yadi da aka yiwa dinkin doguwar riga,da gyale mahadinsa,fuskarta har yau bata cika ba a yadda take a baya,saidai sassanyan kyan nan da baya gushewa kwance saman fuskar tata. Akwai alamu na samun nutsuwa a tattare da ita,sabanin satittikan baya da dukka wata natsuwa tayi qaura daga rayuwarta,ake shirin haukatata,a maidata mahaukaciya zalla,idan ta yiwu ma yazo da qarar kwana,bataga abinda zai hanata ta baqunci lahira ba.
Cikin azama tare da son nunawa duniya shi din wankakke ne,kuma masoyi ga matarsa ya miqe cikin zallar mamaki ya nufeta yana qwala kiran sunanta. Rungumeta yayi nufin yi,saidai kafin yakai ga aikata hakan ya samu tsarabar wani lafiyayyen mari saman fuskarta,sannan ta tattara dukka qarfin data shigo dashi ta ingizashi baya ya fada saman momee dake zaune cikin kaduwa da tsurewa.
Zumbur ya miqe yana shafa wajen,sannan ya maida dubansa a kanta,sanda take tsaye ta kafeshi da fararen manyan idanunta dake dauke yau din da wani irin matsanancin fushi da bai taba ganin irinsa tattare da ita ba
"Baki warke bane sãahar?,subhanallahi"
"Kaine zaka shiga taka haukar yanzun nan,mayaudari maciyin amana,ina neman tsarin Allah daga kai" sai ta fashe da kuka ta soma sulalewa a gurin zata zauna,anty farheen ta riqeta da kyau tana bata baki. Tuni maama ta qaraso bayan ta tabbatar ba mafarki takeyi ba,ta rungume 'yarta tsam tana jero addu'o'in godiya ga Allah
"Ya kamata kowa ya samu waje ya zauna" yaa Saifullahi ya magantu cikin nutsuwarsa,domin ya karanci akwai babban al'amari dake shirin faruwa,komai ya fara bayyanar masa saman fuskar adam da babarsa,sannan ya akayi sãahar take a gidan muhyiddeen duk da tsahon lokacin da aka dauka ana nemanta ba tare da kowa ya sani ba?,ga adam da momee suna matsawa daga bakin qofa?,tamkar yaa zaid ya lura,sai ya matsa yayiwa kansa mazauni daga can hanyar qofar,suka zamana a tsakiya.
A nutse afifa ta qaraso tsakiyarsu ta dire jakar. Lokacin da idanun adam suka sauka a kan jakar sai ga fitsari ya balle masa yana daga zaunen,zazzafar gudawa ta soma qoqarin kufce masa amma ya matseta da kyau,gurbatacciyar ziciyarsa tana gaya masa akwai sauran dama adam,kada ka karaya,muddin baka amsa ba ba wanda ya isa ya tilastaka,koda kuwa a kotu ne.
A gaban kowa sãahar ta matso,ta daga jakar ta zazzage komai ya tarwatse a qasa,wani zazzafan kuka ya taso mata,amma ta danneshi. Daya bayan daya ta soma basu labarin yadda suka fara hadaka a rayuwarsu,yarjajeniyar rashin daukan ciki,canjin halayensa,kamashi da tayi a waya da zuba mata tablet da yayi na zubda ciki,bayyanar ha'incin da yake mata ba tare amma data kama sunan raihanatu ba,azabar daya dinga gana mata har zuwa sanda Allah yayi fitarta daga gidan da taimakon afifa da kuma raihanatu. Kamar wani mahaukacin zaki ya miqe ya soma zage zage,yaa zaid baisan sanda yasa qafa ya kwasheshi ba cikin matsanancin fushi,sai gashi kif a qasa
"Idan ka sake mana magana sai na cire maka harshe" kota ina jikin momee rawa yake,duk sauran qwarin gwiwar da take dasu sun kwaranye sunbi ruwa,don itama wasu abubuwan batasan dasu ba.
Jakar ta fara musu bayani,tana zazzage abubuwan ciki tana nunawa kowa,sai maama ta kasa daurewa,ta rufe fuskarta da hannunta kuka mara sauti yana qwace mata. Duka duka nawa sãahar din take da har zata fuskanci irin wannan cin zarafin cin fuska da zallar cin amana daga gurin da namiji?,ko ita data kawota duniya bata taba fuskantar wani abu da yayi kamanceceniya da wannan ba
"Duk abinda ta fada gaskiya ne,ni shaida ce" muryar raihanatu ta ratsa falon,sai suka waiwaya suna kallonta, idanunta cike fal da qwallar tausayin sãahar din,don itama wasu abubuwan sai yanzu takeji.
Mamaki ya cika momee qwarai,wato raihanatu zata zame mata 'yar kuka?,ta raini makashiyarta?
"Ki daina mamaki momee,ko kina tunanin bansan ba don Allah kike riqe dani ba?,bayan bautar da nake muku kina lissafin sake maidani machine din tatsar kudinki?, bayan kin cinye dukka abinda mahaifiyata ta mallaka,tun tana raye bata da bakin musa miki?" Maganar ta sake zuwarma momee a bazata,lokaci guda ta nemi sukurkuta mata runani,ya akayi yarinyar tasan wannan
"ni zaki butulcewa raihanatu?"
"Dalla malama ki rufewa mutane baki" yaa Saifullahi ya fada cikin muguwar tsawa,ransa baqiqqirin,tamkar zai kifawa momee din mari,hannu Dr mamman ya daga masa,saboda shi wani abuma ya tsaye masa a wuya ya kasa magana,idanunsa qirrr saman fuskar adam,yana tuna girma da nauyin karamcin da ya yiwa rayuwarsa,tarin alkhairai wanda ko sãahar da take matarsa ya hana ya gaya mata,yakance masa
"Nayi maka ne fisabilillahi saboda Allah,ko ummin abba banaso ta sani,kasan su mata,wani qaramin tunani garesu,qanqani abu zai hadaka dasu sai su goranta maka".
Sam basu farga ba,ashe tuni yaa zain yayi kiran mopol,kafin kace wani abu sai isowarsu akaji da sanyo kansu cikin gidan
"Waye yayi hakan a cikinku?" Dr mamman ya tambaya
"Kayi haquri abba,nine" ya zaid ya fada yana miqewa,yanason a hukunta masa adam da mahaifiyarsa hukunci Mafi tsanani da radadi,irin hukuncin da har su koma ga Allah ba zasu mance dashi ba.
"Amma ina zaune ba zaka fara neman shawarata ba zain?"
"Kayimin afuwa abba" yana gama fada ga fita,cikin second biyar suka cika falon.
"Wait please" ya Saifullahi ya fada,ya miqa hannu ya ciro paper,ya zaro pen daga aljihunsa ya dorawa adam da ake qoqarin cukuikuyewa
"Maza rubuta mata takardarta" kai ya girgiza cikin taurin zuciya da taurin kai
"Matata ce,kuma ina sonta har yanzu,don haka bazan saketa ba,saidai......." Bai qarasa fada ba ya Saifullahin ya daukeshi da wani kyakkyawan mari
"Mu zaka gayawa maganar banza da wofi?,wato saboda baka daku ba har kana da qwarin gwiwar yi mana musu ko?" Duk da marin amma sai ya sake girgiza kai
"Saidai ta mutu da igiyar aure na"
"Ba zata mutu ba kuwa,saboda mudin ba jahilai bane,kawai kotu akwai shari'a kuma" ya muhyiddeen da mamakin adam ke sake kasheshi ya fada. Saidai yana rufe bakinsa mopol din ya saukewa adam din wani irin zazzafar mahangurba da lokaci guda ta sauke masa jini ta hanci da labbansa,ta kuma tara masa wani lafiyayyen jini a gefen idanunsa. Ihu momee ta saki tana neman taimakon wai za'a kasheta ita da danta
"Saketa,ka saketa nace karsu kasheka baka da gata" koda momee din bata fada ba zai rubuta,shi kadai yasan kalar azabar da yaji,idanunsa a rurrufe ya rubuta mata saki daya. A fusace ya Saifullahin ya duba
"Don ubanka qarashe mata sauran biyun" dr mamman ne da nasa mamakin ya qarasa daskarar dashi ya daga masa hannu
"Rabu dashi" ya basu umarni a taqaice,daa yaso ya hana a tafi dasu,amma yadda suka nuna rashin nadama kwata kwata bisa fuskarsu yasa ya kasa hana mopol din tafiya dasu.
"So nake a azabtarmin dasu yadda ya kamata,a sassaba masa kamanni shida uwarsa,banason kowa yasan inda suke,kada kuma a daga musu qafa ko na kwana daya,zamuyi waya" yacewa da shugabansun
"Karka damu,sakamakon mummuna ai mummuna ne" shima ya fada cike da jin takaicin adam da uwarsa.
Ko minti biyar basu qara a gidan ba suka tattara nasu ya nasu suka fice a gidan,sãahar ce tabi raihanatu da kallo wadda ta hada nata kayan ta fara yin titi
"Abba bata da kowa a qasar nan,kuma ko yanzun bata da wajen zama,dama suke riqe da ita,na tabbatar kuma ba zasu ci gaba da riqonta ba" wannan yasa suka dauki raihanatun,abban kuma ya tabbatarwa sa sãahar zai kula da nauyinta da rayuwarta,zuwa gaba kadan kuma zasuje ghana a binciko danginta na qwarai,don susan irin riqon da momee tayi mata. Ajiyar zuciya sãahar ta sauke
"Allah yasa su iya wani abu,saboda momee ta cikasu da kyaututtuka,a yanzu kuwa lalacewa ta tattaru a cikin dangi,duk lalacewarka izgilancinka da rashin ganin girman mutane,taka mutane da mugunyar halinka kaida iyalinka,muddin kana ungo ungo,sai idanun 'yan uwa su rufe daga aibunka,a rasa wani tsayayyen da idan kayi ba daidai ba za'a tsaya a tsawatar maka a kuma hukuntaka dai dai da laifinka" kai abban ya jinjina,maganar sãahar tana kan hanya
"Wannan shine yake kawo lalacewar zumunci da tabarbarewarsa,dole sai an hadu za'a gyara,dole sai an hadu an hukunta me qarfi ko mara qarfi,ya zamana kowa baifi qarfin doka ba,Allah ya kyauta,yasa mufi qarfin zukatanmu"