Sashe 88
Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
To wannan magana da sukayi da
Anty farheen sai afifa ta saki jikinta,tun a washegari ita da anty farheen suka soma tsara abubuwa da gabatar da shirye shirye. Ta fannin säahar kuwa jin kanta tayi sakayau,ta tsinci kanta cikin wata iriyar walwala mara misali,hankalinta taji yayi mugun kwantawa,tana ji a ranta yanzu bata da sauran matsala a rayuwa. Saidai harkokin gabanta kawai takeyi,duk wani shiri da su anty farheen sukeyi tana gefe ta zuba musu idanu,gani takeyi bata lokacinsu da kuma kudadensu sukeyi,wani abun saidai ta kalla ta tabe baki,amma batace komai ba saboda abune da take ganin tsakaninta ne kawai da toufeeq din,babu wanda ta shaidawa manufar aurensu.
Kwanakin ukun da ya diba matan
baqi na musamman cikin girma daga gidan
Dr mahmud JARMA suka sauka a gidan Dr girema da kudin auren yaransu guda biyu.
Muhammad toufeeq ya bayar da zunzurutun kudin auren Khadija Muhammad girema har naira million daya,yayin da sajjad da ya tsunduma cikin soyayyar afifa tun ganinsa da ita na farko ya bada dubu dari biyar. Sajjad yaso qwarai a qara kudaden sufi haka,amma dr jarma yace sam,hakanma yaso yayi yawa,albarka yake nema musu. Magabatansu sun roqi sati uku kacal,dr girema da gannensa da suka karbi kudin tare basu ja ba,ganin yadda Dr jarma da kansa yaketa roqon ayi masa alfarmar hakan.
Da daren ranar dukka su biyun suna dakinsu,afifa waya take amsawa tsakaninta da anty farheen,duka maganarsu akan yadda shirye shirye zasu guda na ne,sayayyar kayan dakinsu zuwa gyaran jikinsu. Cikin satin takeso yaa muhyi ya samar musu da visa su ukun,china turkey ko Dubai,duk wadda tafi sauri da sauqi,su dora kayan ta sama yadda zayazo da wuri
"Amma ta sama anty akwai kudi fa"
"Karki damu,biyan buqata akeso,indai china ne ma babu matsala,akwai lucky cargo da kayan zasu iso cikin kwanaki galilan har nan kano(me bugatar hulda da amintaccen kamfanin saboda kawo kaya daga china zuwa Nigeria dukka states,sai ya tuntubeni ta wannan number don na hadashi da kamfanin kai tsaye 08187255862)". Sati guda takeso suyi a can,satin da suka dawo kuma sai a fara gyaran jiki da sauran hidimomin da suka shafi amare.
*HUGUMA*
* TABARMAR KASHI *
Book 02 Page 7
Har afifa ta gama wayar idanun saahar yana kan wayarta tana chart,ido tadan zuba mata zarginta yana sake tabbata,yadda sãahar me shakulaton bangaro tare da nuna halin ko inkula da dukka abinda ya shafi bikin ya sake tabbatar mata da zarginta,uwa uba ko sau daya ita dai idanunta basu taba nuna mata kiran toufeeq jarma ba
"Kina jina muna magana amma bakice
komai ba?" Dan duban afifan tayi,sai ta saki
murmushi
"To me kikeso nace?,salon nayi rash-in
kunya?,kuma ma ai kin gama komai,duk
abinda nake bugata ko zance ke kin isar
min,duk abinda ya samu ayi,wanda bai zama
lallai ba ko bai samu ba sai a haqura ko?" Kai
afifa ke girgizawa tana kallonta
"Amma dai ba haka kikayi ba a aurenki da
adamu" ajiye wayar tayi gefe wani murmushi
dake cakude da zallar nishadin da takeji
gasan ranta ya kubce mata ta zuro gafafunta
gasa cikin zummar shiga bandaki sannan ta
amsawa afifa
"Banda abinki hajiya afifatu,ai kullum dan
adam dada wayo da hankali yakeyi ko?,don
zanyi aure bawai ba hakan yana nufin na
mance da asalin su waye maza ba,ko kuma na manta radadi da daci da suka dasawa rayuwata ba"
"'Anzo gurin" afifa ta fada tana zagayowa gabanta da sauri,ta jawo stool ta zauna akai tana fuskantar sãahar wadda ke mata duban mamaki
"Bestie bandaki zan shiga,yaa haka?"
"Inason nasan gaskiya ne bestie,yau ashe anzo wata gaba da zaki dinga boyemin wani abu a rayuwarki? meye ainihin gaskiyar magana akan aurenki da toufeeq jarma,duk yadda naso na basar nayi kaman ba komai na kasa bestie,ki gayamin gaskiya" murmushi tayi hankali kwance
"Ki barni naje nayi fitsarin mana"
"Na barki" ta fada tana dubanta. A nutse ta miqe ta wuce bandakin,ba jimawa ta dawo ta koma inda ta tashi ta zauna. Komai ta warware mata,abun sai ya sanya afifa murmushi me kama da dariya
"Allah ya sanya alkhairi,abu kuma yay kyau,hakanan hankalina ya kwanta da bayananki,amma ke dashi dukka ku shirya ranar karbar sakamako a tsakaninku"
"Sakamakon me?,kefa wani lokacin kin fiya jaye jaye"
"Lokaci zai bayyana komai". Tasan halin afifan da iya saqa zance,sai kawai tabar zancanta,ta maida qafafunta saman gadon tayi kwanciyarta cikin nutsuwar data jima bata jita cikin ruhinta ba. Yayin da afifa ke duba kiran da ya shigo mata,sajjad ne,migewa tayi ta dauki scarf dinta ta fice a dakin, sãahar data fuskanci meke faruwa ta bita d kallo tana tabe baki
"Hmmm,soyayya manya,mun jima da dawowa daga rakiyarta,mu da ita ko a lahira mun raba jaha" ta fada qasa qasa kamar me qunquni tana gyara kwanciyarta,sai kuma ta tuna zata yiwa maama gyaran wardrobe,don haka ta miqe ta sauko,ta kama gashinta me santsi ta daureshi waie daya,ta dora hula a kanta ta zura slippers ta fice.
********Ya jima a zaune yana juya wayar hannunsa,dukkansu mamaki suke bashi qwarai, nadeeya maji ga kuma mai gayya mai aiki fadeela. Yadda suke nuna tsantsar zakwadi da kuma farinciki akan wannan auren abun daure masa kai yakeyi. A yau sun jima suna waya da majiirin wayar da basu taba yin me tsaho irinta ba,duk da cewa kamar dai ko yaushe itace tayi kiransa bashi ne yayi kiranta ba. Dole bayan ya gama mamakin lamarin ya ajiye wayar gefe,dai dai lokacin sajjad ya shigo gurin bakinsa dauke da sallama.
Guri ya samu ya zauna yana kallonsa yana kwance cikin lounge chair
"'nata jira naji daga gareka" kyawawan zagayyun idanunsa kawai ya daga ya kalli sajjad din
"Game da me fa?" Takaici ya kama sajjad din,kamar bazaiyi magana ba amma ya cije
"Ba aure zakayi bane malam?"
"Aure zanyi sai mene?"
"Bakasan kana da buqatar yin wasu abubuwa ba,mace fa zaka ajjiye cikin gidanka,a ina zata zauna?,ka hada mata lefe?,dinkunan biki da sauransu"
kamar bazaice komai ba,sai ya miqe ya zauna sosal sannan ya zura qafafunsa qasa yadda zaiji dadin zaman,idanunsa akan sajjad din
"Ce maka akayi wani aure ne duk da za'a tsaya masa wannan hidimar? kawai a daura ta shigo taci gaba da aikinta,ni kuma na bata gurin zama da ciyarwa da suttura that's all,duk wadan nan abubuwan da kake jerowa sai ku masu auren farko,tun wani zamani da ya shude muka rufe wanan batun" sai ya miga hannu ya janyo plate din apple da Jacob ya ajiye masa.
Ido sajjad ya zuba masa,kaman zaiyi magana sai kuma ya fasa,ya saki qaramin murmushi sannan ya miqe
"Zaka gane kurenka,indai macece ba'a cika musu baki,i pitty you duk lokacin da ka fada tarkonta,saboda haka kabi a hankali,shawarace kyauta na baka" baice masa komai ba sai qaramin miskilin murmushin da ya subuce akan fuskarsa,wannan maganar ta sajjad bata da banbancin da tatsuniya a gurinsa. Banda fadeela,babu abinda zai sanya ya biya sadakinta ta amsa sunan matarsa a bakunan al'umma bare azo gurin da sajjad din ke magana a yanzu.
*********Karo na biyu ya sake gwada kiran qanwar tasa,wannan karon ta shiga sabanin lokutan bava da kiran yake yankewa.
Spoon din hannunta ta ajiiye lokacin da kiran ke shigowa,wani hamshagin murmushi ta saki,yadda yayan nata yake bata kulawa tun daga wancan zamanin zuwa yanzu yana y mata dadi matuga,kuma har yau bata canza zani ba sanadiyyar jajircewarta
"Assalamualaikum barka da warhaka yaaya" hajiya qarama ta fada bayan ta saka wayar a kunnenta
"Yauwa barkanki dai FAUZIYYA" Cikin kulawa suke gaisawa da juna,ya tattambayeta yanayin kayan da taje siyowa a qasar. Tsahon mintuna goma suna tattaunawa sannan ya fara maganar da itace maqasudin kiran
"Kwanaki kusan bakwai ina kiranki na kasa samunki har ina tunanin akwai matsala ne"
"Babu yaaya wani lokaci ajiye wayar nake a nan hotel idan banason yawan kiran"
"To yayi kyau, Allah ya taimaka,amma inajin ai dole ki yanki ticket na dawowa sati me zuwa ko satin sama ma,don yaronki ya tashi aure,Allah ya amsa addu'armu" Wani irin mummunar faduwar gaba me hade da wani tashin hankali ne suka rufto mata,tamkar wadda ake juyewa duwatsu saman kan nata
"Yaron....na? wanne kuma?" Ta fada tana qoqarin boye gigicewar da tayi. Dan murmushi dr jarma ya saki
"Kina da wani d'an ne bayan toufeeq?,inda
'yarki nace saiki tambaya nadeeya ko
HASEENA?" Sarawa kanta yayi da matsiyacin qarfi,wani zazzafan gumi ya karyo ilahirin jikinta ta kowanne sashe,taji kamar an saka allura da zare ana daure kanta,cikinta ya juya take bayan gida ya matsota
"Yaya?,ka manta haseena naketa ajjiyewa toufeeq? tunda anyi na farko ba'a dace ba?,ita kanta yarinyar bata taba kula kowa ba saboda ta sanya ranta akan TOUFEEQ din,ko yanzu haka sati uku ne kacal ya rage ta gama karatunta ta baro hannun babanta ta dawo nan nigeria don su daidaita kansu ita dashi"
"Banda abinki mijin mace hudu ne faidan yaga yana da ra'ayi uku ne sauran da zai cike ma,sannan ita kanta yarinyar bata da matsala,na santa farin sani,itace wadda ta taba rige president na kamfani na,kuma kema kin santa,wadda ke kula da fadeela kafin tahowarki"
"Kanbun uba!" Ta fada gasan ranta har bakinta yana motsawa
"Nanny fa yaya!" Ta fadi cikin daukaka sauti
"Ba nanny bace fauziyya,kawai tayi sha'awar aikinne,amma badon ta rasa komai ko kuma bata da gata ba,infact 'yar Dr mamman girema ce,wanda kikaso a baya,kikace matarsa ce ta hanashi sauraro da kulaki" wani bala'in kawai bayanan yayan nata suka qara mata,Dr mamman da baya ganin kowacce mace a gabansa sai matarsa?‚buzuwar nijer,wadda koda wasa mamman din bai taba kallon wata mace ya taya da zummar zai aureta ba saboda yadda ya samu kula biyayya da dukkan wani jin dadin rayuwa da d'a namiji yake bugata da muradin samu daga wajen diya mace? ‚matar data wahalar da ita ta kuma kafa tarihi ta zama mace ta farko da tayi mata shamaki da abinda takeso? bayan tafiyarta toufeeq ya koma gidan,yarinyar tayi amfani da wannan damar kenan ta ja hankalinsa? har sai daya kamu da soyayyarta me zafin da ya kasa sukuni cikin sati uku kacal ya nema aurenta?,to itakam fauziyya tana me? wanne irin sakewa tayi haka?. Kamar dr jarma shima yanason canzawa,ta yaya yake maganar idan toufeeq din yana so?,bata saba jin wannan kalamin daga bakinsa ba a duk sanda ta bugaci wani abu daga garesa, komai tsananinsa kuwa
Anty farheen sai afifa ta saki jikinta,tun a washegari ita da anty farheen suka soma tsara abubuwa da gabatar da shirye shirye. Ta fannin säahar kuwa jin kanta tayi sakayau,ta tsinci kanta cikin wata iriyar walwala mara misali,hankalinta taji yayi mugun kwantawa,tana ji a ranta yanzu bata da sauran matsala a rayuwa. Saidai harkokin gabanta kawai takeyi,duk wani shiri da su anty farheen sukeyi tana gefe ta zuba musu idanu,gani takeyi bata lokacinsu da kuma kudadensu sukeyi,wani abun saidai ta kalla ta tabe baki,amma batace komai ba saboda abune da take ganin tsakaninta ne kawai da toufeeq din,babu wanda ta shaidawa manufar aurensu.
Kwanakin ukun da ya diba matan
baqi na musamman cikin girma daga gidan
Dr mahmud JARMA suka sauka a gidan Dr girema da kudin auren yaransu guda biyu.
Muhammad toufeeq ya bayar da zunzurutun kudin auren Khadija Muhammad girema har naira million daya,yayin da sajjad da ya tsunduma cikin soyayyar afifa tun ganinsa da ita na farko ya bada dubu dari biyar. Sajjad yaso qwarai a qara kudaden sufi haka,amma dr jarma yace sam,hakanma yaso yayi yawa,albarka yake nema musu. Magabatansu sun roqi sati uku kacal,dr girema da gannensa da suka karbi kudin tare basu ja ba,ganin yadda Dr jarma da kansa yaketa roqon ayi masa alfarmar hakan.
Da daren ranar dukka su biyun suna dakinsu,afifa waya take amsawa tsakaninta da anty farheen,duka maganarsu akan yadda shirye shirye zasu guda na ne,sayayyar kayan dakinsu zuwa gyaran jikinsu. Cikin satin takeso yaa muhyi ya samar musu da visa su ukun,china turkey ko Dubai,duk wadda tafi sauri da sauqi,su dora kayan ta sama yadda zayazo da wuri
"Amma ta sama anty akwai kudi fa"
"Karki damu,biyan buqata akeso,indai china ne ma babu matsala,akwai lucky cargo da kayan zasu iso cikin kwanaki galilan har nan kano(me bugatar hulda da amintaccen kamfanin saboda kawo kaya daga china zuwa Nigeria dukka states,sai ya tuntubeni ta wannan number don na hadashi da kamfanin kai tsaye 08187255862)". Sati guda takeso suyi a can,satin da suka dawo kuma sai a fara gyaran jiki da sauran hidimomin da suka shafi amare.
*HUGUMA*
* TABARMAR KASHI *
Book 02 Page 7
Har afifa ta gama wayar idanun saahar yana kan wayarta tana chart,ido tadan zuba mata zarginta yana sake tabbata,yadda sãahar me shakulaton bangaro tare da nuna halin ko inkula da dukka abinda ya shafi bikin ya sake tabbatar mata da zarginta,uwa uba ko sau daya ita dai idanunta basu taba nuna mata kiran toufeeq jarma ba
"Kina jina muna magana amma bakice
komai ba?" Dan duban afifan tayi,sai ta saki
murmushi
"To me kikeso nace?,salon nayi rash-in
kunya?,kuma ma ai kin gama komai,duk
abinda nake bugata ko zance ke kin isar
min,duk abinda ya samu ayi,wanda bai zama
lallai ba ko bai samu ba sai a haqura ko?" Kai
afifa ke girgizawa tana kallonta
"Amma dai ba haka kikayi ba a aurenki da
adamu" ajiye wayar tayi gefe wani murmushi
dake cakude da zallar nishadin da takeji
gasan ranta ya kubce mata ta zuro gafafunta
gasa cikin zummar shiga bandaki sannan ta
amsawa afifa
"Banda abinki hajiya afifatu,ai kullum dan
adam dada wayo da hankali yakeyi ko?,don
zanyi aure bawai ba hakan yana nufin na
mance da asalin su waye maza ba,ko kuma na manta radadi da daci da suka dasawa rayuwata ba"
"'Anzo gurin" afifa ta fada tana zagayowa gabanta da sauri,ta jawo stool ta zauna akai tana fuskantar sãahar wadda ke mata duban mamaki
"Bestie bandaki zan shiga,yaa haka?"
"Inason nasan gaskiya ne bestie,yau ashe anzo wata gaba da zaki dinga boyemin wani abu a rayuwarki? meye ainihin gaskiyar magana akan aurenki da toufeeq jarma,duk yadda naso na basar nayi kaman ba komai na kasa bestie,ki gayamin gaskiya" murmushi tayi hankali kwance
"Ki barni naje nayi fitsarin mana"
"Na barki" ta fada tana dubanta. A nutse ta miqe ta wuce bandakin,ba jimawa ta dawo ta koma inda ta tashi ta zauna. Komai ta warware mata,abun sai ya sanya afifa murmushi me kama da dariya
"Allah ya sanya alkhairi,abu kuma yay kyau,hakanan hankalina ya kwanta da bayananki,amma ke dashi dukka ku shirya ranar karbar sakamako a tsakaninku"
"Sakamakon me?,kefa wani lokacin kin fiya jaye jaye"
"Lokaci zai bayyana komai". Tasan halin afifan da iya saqa zance,sai kawai tabar zancanta,ta maida qafafunta saman gadon tayi kwanciyarta cikin nutsuwar data jima bata jita cikin ruhinta ba. Yayin da afifa ke duba kiran da ya shigo mata,sajjad ne,migewa tayi ta dauki scarf dinta ta fice a dakin, sãahar data fuskanci meke faruwa ta bita d kallo tana tabe baki
"Hmmm,soyayya manya,mun jima da dawowa daga rakiyarta,mu da ita ko a lahira mun raba jaha" ta fada qasa qasa kamar me qunquni tana gyara kwanciyarta,sai kuma ta tuna zata yiwa maama gyaran wardrobe,don haka ta miqe ta sauko,ta kama gashinta me santsi ta daureshi waie daya,ta dora hula a kanta ta zura slippers ta fice.
********Ya jima a zaune yana juya wayar hannunsa,dukkansu mamaki suke bashi qwarai, nadeeya maji ga kuma mai gayya mai aiki fadeela. Yadda suke nuna tsantsar zakwadi da kuma farinciki akan wannan auren abun daure masa kai yakeyi. A yau sun jima suna waya da majiirin wayar da basu taba yin me tsaho irinta ba,duk da cewa kamar dai ko yaushe itace tayi kiransa bashi ne yayi kiranta ba. Dole bayan ya gama mamakin lamarin ya ajiye wayar gefe,dai dai lokacin sajjad ya shigo gurin bakinsa dauke da sallama.
Guri ya samu ya zauna yana kallonsa yana kwance cikin lounge chair
"'nata jira naji daga gareka" kyawawan zagayyun idanunsa kawai ya daga ya kalli sajjad din
"Game da me fa?" Takaici ya kama sajjad din,kamar bazaiyi magana ba amma ya cije
"Ba aure zakayi bane malam?"
"Aure zanyi sai mene?"
"Bakasan kana da buqatar yin wasu abubuwa ba,mace fa zaka ajjiye cikin gidanka,a ina zata zauna?,ka hada mata lefe?,dinkunan biki da sauransu"
kamar bazaice komai ba,sai ya miqe ya zauna sosal sannan ya zura qafafunsa qasa yadda zaiji dadin zaman,idanunsa akan sajjad din
"Ce maka akayi wani aure ne duk da za'a tsaya masa wannan hidimar? kawai a daura ta shigo taci gaba da aikinta,ni kuma na bata gurin zama da ciyarwa da suttura that's all,duk wadan nan abubuwan da kake jerowa sai ku masu auren farko,tun wani zamani da ya shude muka rufe wanan batun" sai ya miga hannu ya janyo plate din apple da Jacob ya ajiye masa.
Ido sajjad ya zuba masa,kaman zaiyi magana sai kuma ya fasa,ya saki qaramin murmushi sannan ya miqe
"Zaka gane kurenka,indai macece ba'a cika musu baki,i pitty you duk lokacin da ka fada tarkonta,saboda haka kabi a hankali,shawarace kyauta na baka" baice masa komai ba sai qaramin miskilin murmushin da ya subuce akan fuskarsa,wannan maganar ta sajjad bata da banbancin da tatsuniya a gurinsa. Banda fadeela,babu abinda zai sanya ya biya sadakinta ta amsa sunan matarsa a bakunan al'umma bare azo gurin da sajjad din ke magana a yanzu.
*********Karo na biyu ya sake gwada kiran qanwar tasa,wannan karon ta shiga sabanin lokutan bava da kiran yake yankewa.
Spoon din hannunta ta ajiiye lokacin da kiran ke shigowa,wani hamshagin murmushi ta saki,yadda yayan nata yake bata kulawa tun daga wancan zamanin zuwa yanzu yana y mata dadi matuga,kuma har yau bata canza zani ba sanadiyyar jajircewarta
"Assalamualaikum barka da warhaka yaaya" hajiya qarama ta fada bayan ta saka wayar a kunnenta
"Yauwa barkanki dai FAUZIYYA" Cikin kulawa suke gaisawa da juna,ya tattambayeta yanayin kayan da taje siyowa a qasar. Tsahon mintuna goma suna tattaunawa sannan ya fara maganar da itace maqasudin kiran
"Kwanaki kusan bakwai ina kiranki na kasa samunki har ina tunanin akwai matsala ne"
"Babu yaaya wani lokaci ajiye wayar nake a nan hotel idan banason yawan kiran"
"To yayi kyau, Allah ya taimaka,amma inajin ai dole ki yanki ticket na dawowa sati me zuwa ko satin sama ma,don yaronki ya tashi aure,Allah ya amsa addu'armu" Wani irin mummunar faduwar gaba me hade da wani tashin hankali ne suka rufto mata,tamkar wadda ake juyewa duwatsu saman kan nata
"Yaron....na? wanne kuma?" Ta fada tana qoqarin boye gigicewar da tayi. Dan murmushi dr jarma ya saki
"Kina da wani d'an ne bayan toufeeq?,inda
'yarki nace saiki tambaya nadeeya ko
HASEENA?" Sarawa kanta yayi da matsiyacin qarfi,wani zazzafan gumi ya karyo ilahirin jikinta ta kowanne sashe,taji kamar an saka allura da zare ana daure kanta,cikinta ya juya take bayan gida ya matsota
"Yaya?,ka manta haseena naketa ajjiyewa toufeeq? tunda anyi na farko ba'a dace ba?,ita kanta yarinyar bata taba kula kowa ba saboda ta sanya ranta akan TOUFEEQ din,ko yanzu haka sati uku ne kacal ya rage ta gama karatunta ta baro hannun babanta ta dawo nan nigeria don su daidaita kansu ita dashi"
"Banda abinki mijin mace hudu ne faidan yaga yana da ra'ayi uku ne sauran da zai cike ma,sannan ita kanta yarinyar bata da matsala,na santa farin sani,itace wadda ta taba rige president na kamfani na,kuma kema kin santa,wadda ke kula da fadeela kafin tahowarki"
"Kanbun uba!" Ta fada gasan ranta har bakinta yana motsawa
"Nanny fa yaya!" Ta fadi cikin daukaka sauti
"Ba nanny bace fauziyya,kawai tayi sha'awar aikinne,amma badon ta rasa komai ko kuma bata da gata ba,infact 'yar Dr mamman girema ce,wanda kikaso a baya,kikace matarsa ce ta hanashi sauraro da kulaki" wani bala'in kawai bayanan yayan nata suka qara mata,Dr mamman da baya ganin kowacce mace a gabansa sai matarsa?‚buzuwar nijer,wadda koda wasa mamman din bai taba kallon wata mace ya taya da zummar zai aureta ba saboda yadda ya samu kula biyayya da dukkan wani jin dadin rayuwa da d'a namiji yake bugata da muradin samu daga wajen diya mace? ‚matar data wahalar da ita ta kuma kafa tarihi ta zama mace ta farko da tayi mata shamaki da abinda takeso? bayan tafiyarta toufeeq ya koma gidan,yarinyar tayi amfani da wannan damar kenan ta ja hankalinsa? har sai daya kamu da soyayyarta me zafin da ya kasa sukuni cikin sati uku kacal ya nema aurenta?,to itakam fauziyya tana me? wanne irin sakewa tayi haka?. Kamar dr jarma shima yanason canzawa,ta yaya yake maganar idan toufeeq din yana so?,bata saba jin wannan kalamin daga bakinsa ba a duk sanda ta bugaci wani abu daga garesa, komai tsananinsa kuwa