← Book details Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 158 OF 171

Sashe 158

Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yawun bakin meenal gaba daya ya dauke da wani irin mahaukacin kishin saahar, tabbas inda ace akwai bindiga yanxun a hannunta babu abinda zai hanata harbawa saitin zuciyar saahar, tako ina ita dimma tasan zati da cikar haiba nutsuwa da kamalar säahar ta zarta tata,saidai kuma bata jin ko kadan wannan Karan zatay giving up, ba zata sassauta ba wajen farautar toufeeq har sai taga abinda ya turewa buzu nadinsa,don haka ta tattara dukkan qwarin gwiwarta tayi taku biyu zuwa inda suke takawa,cikin fari da ido, lanqwasa harshe da yauqi tace

"'Barka da dawowa yaa mohanmu.....

"'Wayy!" Säahar ta datsin maganar da meenal ta debo tana lanqwashewa, abinda ya maida dukkan hankalin toufeeq kanta

"Yaya? me ya faru?" Cikin wata muguwar shagwaba data shigeshi gaba daya cikin jini da julya tace

"Qafafuna,na gaji,nidai ka daukeni"

"Angama" ya furta yana nannade hannun tsadadden yadin jikinsa. A tausashe sannan a hankali ya tsugunna yasa hannunsa ya dagata cak ya fara takawa da ita zuwa sashensa idanunsa cikin nata yana tambayarta

"Are u comfortable?" Kai ta jinjina masa sannan a sace ta dubi sashen da su labiba sukayi mutuwar tsaye,cikin sa'a suka hada idanu,ta aje musu wani kallo na baku isa ba sannan ta maida kanta saman qirjinsa ta kwantar a shagwabe.

Dariya labiba ta qyaqyace da ita sanda taga haseena da tayi mugun shaqa,ta kuma gaza boye shaqar da tayi din ta hanyar binsu da kallo, duk da cewa sun bacewa ganinta

"Ashe dai duka burga ce,ashe dai ba'a isa din ba,ashe duk kwana da tashin da akeyi gida daya duka suna ne,ah wai" labiban ta furta tana tura dauninta gaban goshi,duk kuwa da cewa ita dinma ta shaqi bacin rai har kusan fiye dana haseena.

A mugun fusace haseena din ta waiwayo
'Ke, ki saurara malama, koda giwa ta fadi tafi qarfin wawa, ni ba sa'arki bace,don nafi qarfinki har abada" sosai labiba ta sanya dariya harda shewa

"Mu gani a qasa mana,wai inji kare ana biki a gidansu yace mu gani a qasa,ashe duk wani cika baki da fankamar uwar taki na banza ne, tunda ta gaza mallaka miki mutum daya tal a rayuwarki,wannan ma ya isheku hasara da kaico, bayan kaicon da a wunin yau kafin faduwar rana yake shirin samunku, ku shirya zuwarma gagarumar FALLASA wadda zata cimma rayuwarku" daga wannan sai ta juya tana taku d'ai d'ai, cikin ranta tana jin FALLASAR da zata auku a yau din, tamkar mabudin nasara ne a garesu.

_to maji ma gani wai an binne tsohuwa da ranta_

A bisa bigire daya suke takawa,saidai kowacce zuciyarta cike take da alwashi da kuma mugun tanadi ga ‘yar uwarta,wani irin kallo a sace wanda bakuna basu furta komai ba sai fatan cikan burika, a haka har suka iso mararrabar sassan guda biyu,dr jarma yay gaba. Daga Mansura har fauziyyar kowaccensu tsawa tayi "Ina miki barka da isowa qasarki ta gado,ina miki barka da isowa bigiren da zaki fahimci bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane,ina kuma yi miki jaje da kalar qaddarar da yau din tazo miki da shi, ina miki fatan samun juriya a bisa hakan" sai da gaban hajiya qarama. yadan fadi, amma kuma tayi gaggawar ture wannan daga ranta da tunaninta,don kuwa a kaf tarihinta bata taba yarda kalaman barazana sun tsoratata daga bakin abokin adawa ba. Jifanta tayi da murmushi duk da zuciyarta na cike da kokwanton yadda mansura ke magana kanta tsaye cike da qwarin gwiwa

"Ke ya kamata ki riqe wadan nan kalaman kiyi bitarsu da kyau,domin a yau kadai zaki fahimci ni fauziyya nike sanyawa a auro a kuma saka sannan ayi kome a duk sanda naso hakan, baya ga wanna kuma..…... Tarantin
nan da kike shirin taka gefansa, kina gab da gain asarar da bazaki iya qidanya adadinta ba" murmushin ta jefa mata Itama

"Ni dake shege ka fasa"

"Dan halak sai kallo" sai kowannensu ya juya yana nufar sashensa, saida dukkansu zukatansu cike suke da fargabar yagewar zaninsa a tsakiyar kasuwa,saboda gaba dayansu sunsan sunyi birniya me zurfi da kowa a cikinsu yasan da mummunar ajiyar dan uwansa,amma cikar da zukatansu sukayi da daukan fansa da samun cikar burin diyoyinsu ya sanya suke jin komai zasu iyayi, komai ta fanjama fanjam.

*_turqashi, kuzo kuyi kallon dinkin gadar zare zai tsinke_*

Da hanau gwara mannau inji hausawa * ,ku yimin uzuri,jiya dama ta bayar,yau kuma sal a hankali, na gode qwarai_*

Zafafabiyar
"HUGUMA*

*TABARMAR KASHI_*

Book 02 Page 65

Zucivarta kamar zata fado take takawa zuwa bedroom din Dr jarma din. Hankalinta na tashi idan duk second daya da zai shude idan tayi tunanin ko dai fauziyya ta sanya Dr jarma ya dawo da shifa dakint? tunda dai kalamanta hakan suke nunawa yana shirin faruwa. Kai ta girgiza, indai hakanne har abada ba ) zata taba yadda ta zauna da shifa ba, ba zata taba aminta wata mace ta shigo mata gidanta ba gidan data ciwa burika masu yawa,take kuma sanya ran ita daya ce macen da zata yiwa dr jarma takaba ta kuma karba tumunin takabar ita daya.

Fuskarsa cike da nishadi yake cire kayan jikinsa da zummar yin wanka,jya walwalar dake saman fuskarsa ya sake dasa mata matsananciyar fargaba "'Drya akayi na ganku tare da maji ne?, dama tare kukayi tafiyar?" Waiwayawa yayi ya dubeta yadda ta cake tana masa tambayar wadda tafi kama da titsiye. Kansa ya dan kawar yasan akwai dan rashin kyautatawa da yayi mata,a galla ya shaida mata koda ta waya ne zai maida aurensa

"'Me kikeson ii mansura?"

"Ka maida matarka ne?" Sake maida dubansa yayi a kanta

"Me kike ci na baka na zuba?, ki barni na watsa ruwa mana, ba tun muna can kika gayan kin shirya mana liyafa tare ba?" Kai ta jinjina masa kawai

• "Okay, bari na watsa ruwa na fito, saikiyi gogarin shaidawa kowa ya fito akan lokaci aci abincin tare. hakan dama va kamata lokaci lokaci a dinga yi, saboda vana kawo hadin kai da garin fahimtar juna" bata iya amsa masa ba har ya wuce zuwa bandakin,sai ta furzar da iska daga bakinta,ta dunqule hannunta ta daki dava tafin hannun nata, ta koma ta zauna ta kirayi daya daga cikin masu aikinta tace ta sake shaidawa kowa,amma sashen toufeeg a shaida musu ta waya. Ajiye wayar tayi gaba daya tana jin nutsuwa tana yin qaura daga gangar jikinta,duk yadda taso bawa kanta qwarin gwiwa da kwantarwa da kanta hankali abun ya faskara, sai ta bude wavarta ta hau shirya komai cikin shirin ko ta kwana koda
bugatar hakan zata taso.

Tun a hallway ya din bedrooms dinsu ya fara rage
mata kayan [ikinta,yana tsaye daga bayanta yayin data dogara dukkan wani garfi nata a jikinsa,cikin wani irin slow motion suke takawa shida ita,sadarwar skin to skin din dake a tsakaninsu tana rura wutar dake zukatansu gaba daya. Ta dauka yana isa qofar bedroom dinsa zal bude, sai taga bai tsaya ba har dai dava isa gaban full length mirror din dake bangon garshe na hallway din. Tar surarta da tashi suka bayyana a jikin madubin, tsananin kunya ta sanyata juyowa da sauri ta bawa madubin baya tana boye kanta a qirjinsa.

Wani galabaitaccen murmushi ya saki yana ci gaba da kallonta ta cikin madubin, yana jin yadda zuciyarsa ke sake laushi tana narkewa cikin soyayyarta. A nutse ya sanya lausasan tafukan hannunsa ya dago fuskarta yana kallon tsakiyar qwayar idanunta. Irin wanann kallon yana da bala'in tasiri cikin zukatan da jikkunansu su duka,musamman da suke kan irin wannan yanayin

"'Biyan bashi zanyi yau din,i hope you're ready?" Wani lallausan murmushi da tasan vana tarwatsa duk wata
nutsuwa tashi ta sakar masa,sanann tayi farrr da fararen idanunta da suka qara haske sosai,da zazzaqar muryarta tace dashi

"Babies sun shirya sada zumunci da abbynsu...
sassauta muryarta sosai

"Nima ummien babies din a shire nake,i crave for you since

"Shshshsh" ya furta yana murmushi hadi da dora yatsansa saman labbansa yana sakin murmushi

"I know,i can read it ta can gasan wadan nan fitinannun idanuwan" tabe baki tayi kamar me shirin sanya masa kuka

"You mean.....na zama fitinanniya fa?" Qaramar dariya ya saki

"Ba ke bace ai nasan laifin babies ne"

"Allah Allah nasan ni kake nufi" ta furta tana narke masa tare da dunqule hannunta ta daki qirjinsa. Hannu daya yasa ya dafe saitin zuciyarsa hadi da lumshe ido

"Ya salam ya Allah, maji zata illatani, bayan ban fara komai akan sonta ba,zo muje ki gani,na tabbatar hallway din nan yayi mana kadan" sai ya dauketa ya wuce nutsatsen bedroom din nan nasa dake da wani irin tattausan yanayi dake garawa zukata da feelings na masoya armashi.

Yadda a yau din ya susuce a kanta sai da abun ya bata mamaki ya kuma tsaye mata sosai a rai, don daga ita har shi din sun aminta da juna maqura,sai ya dinga jin kamar säahar din an sake sabunta masa ita ne,da ayar ta samu ta lallabashi ya shiga wanka itama ta wuce nata dakin don ta shiva,ranta da zuciyarta cike fal da mamakin sauyawarta,bata gajiya ko kadan da bugatuwa zuwa ga toufeeq din

"Allah yasa kici gaba da tabbata a haka koda bayan kin bani ajiyata ne" furucin da ya fada mata kenan a dazun yana gangame da ita.

Tsaf ta shirva cikin wani material me sulbi sosai
cream color da adon brown flowers da wani avalli a jiki.
Ta kusa mintuna ukun tana tsaye gaban madubi tana kallon kanta da kanta, bataga laifin toufeeq ba, dole ya sake haukacewa a kanta ya kuma sake manne mata, fuskarta ta aje wani kyau na musamman tayi mugu mugun yin fresh.Qaramin murmushi ta saki tana daukan wani siririn turarenta dake da wani sirrintaccen gamshi ta feshe jikinta da dashi sannan tasa wasu slippers masu taushi a gafarta da suka dace da kalar material din jikin nata.

Har ta juya ta dakata,ta dawo da bava tana duban cikinta. Har yanzu a shafe yake ga idanun mutane saidai idan ta sanya English wears ko kuma ta dora hannun nata saman mararta shine take iya jin tasawarsa. Ko a yanzun saman mararta ta dora hannun nata, ta shafi cikin a hankali, iva tudun nasa da takeii kadai vana saukar mata da wani irin farinciki me tarin yawa,qauna mara misaltuwa da ita kanta batasan adadinta ba akan cikin.
Chapter 158 · 0% Book details