← Book details Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 171

Sashe 22

Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Have a seat please" ya fada yana karyar da murya. Bata fiyason ayita roqonta abu ba,hasalima tun asali mutum ce da bata qaunar mita da kuma jan magana,don haka ga qarasa ta zauna a hannun kujerar da ya zaid ya tashi a kai

"Na gode" ya fada yana jin dadin yadda ta girmama buqatarsa,sai ya koma kan kujerar da ya tashi shima,idanunsa a kanta,abinda ya fara sanya ranta baci kenan,batason yawan kallo kwata kwata.

"Basai mun dawo da doguwar magana ba, tunda na fuskanci abinda bakeso kenan,kaina tsaye zan gaya miki,sonki nakeyi sãahar,so kuma irin na aure,qauna ta fisabilillah,bance ki soni yanzu yanzu ba,a'ah ina son ki bani dana zuwa wani lokaci,har zuwa sanda zaki aminta a karan kanki da soyayyar da nake miki,ki kuma gamsu da cewa ke din zaki iya aurena" ya fada yana hade tafukan hannayensu biyu waje daya,kamar me neman gafara.

Ji tayi kamar ya sanya wuqa ya yanki naman zuciyarta,tun bayan rabuwarta da adam yaune karon farko data zauna har kunnuwanta suka saurari kalmar soyayya daga bakin wani namiji,kalmar data jima dayin jana'izarta a kaf littafin rayuwarta,kalmar da takeji a ranta zuwa yanzu cewa qarya ce,babu wani so na gaskiya,saidai SON RAI da SON ZUCIYA da kuma SHA'AWA,sune zallarsu,ake musu ado da fenti a kirasu da soyayya.

A ranta taji kawai mahmud din yazo ne don ya bata mata lokaci,eh....bata lokaci mana, tunda bazai taba samun abinda yakeso daga gareta ba,sai ta miqe tsam

"Zanyi shawara" tayi furucin don ta samu ficewa a dakin,bawai don tana nufin yin shawarar bane da gaske,shawara akan abinda baida muhimmanci?,abinda ta riga ta sani ko sama da qasa zasu hadu bazai samu wannan buri nasa daga gareta ba

"Alfarma ya biyu,don Allah badon ni ba" yayi hanzarin fada ganin ta doshi qofar fita,dole ta tsaya ba tare data waiwayo ba

"Ko sau daya ne tak a rana ki dinga daga wayata"

"Banyi alqawari ba" ta fada kai tsaye tana qarasa ficewa harda 'yar sassarfa wannan karon,kamar wadda akace za'a kama.

Hanyar yabi da kallo harta bace masa,ya dunqule hannunsa ya kaiwa iska naushi,saidi fuskarsa murmushi ne a kwance,ko iya hakan yaji dadi a ransa,koba komai sunyi musayar kalamai duk da ba masu tsayi bane,a qalla an samu improvement ko yaya yake,zaici gaba da trying,bazai gaji ba,ya daga tsadajjen agogon rolex dake hannunsa ya duba lokaci,sai ya taka yana fita daga setting room din,wanda kafin ya iso tuni ya yiwa guard dinsa umarni sun shigo da uban siyayyar da yayo dukka domin sãahar din,karon farko daya fara tad'i da ita a cewarsa.

Rana ce da kuma lokaci na musamman a rayuwarsa da bazai taba mantawa da ita ba,duk da ba wani abun kirki ta gaya mishi ba,bai samu hankalinta da lokacinta yadda yakeso ba.

A wani mugun quntace take komawa zuwa falon abban,gaba daya ta shiga rudani da firgici,hankalinta a tashe yake kamar wadda wani mummunan abu ke shirin samunta.

Tana sallama dr mamman ya zuba mata ido bayan ya dauke kansa daga kan takardar dake hannunsa kafin yakai ga amsa sallamar tata,yana sauke qafafunsa dake harde waje daya qasa tare da binta da idanu,yanason karantar yanayinta da gaske.

Kanta a qasa ta tako lallausan carfet din dake shimfide a falonsa,madadin marbles din da aka qawata fiye da rabin qasan ginin gidan,ta zame a hankali cikin matuqar mutuwar jiki da wata fargaba ta zauna daura dashi

"Gani abba" zama ya sakeyi sosai,ya ajjiye takardar yana dubanta

"Ina kyautata zaton ba yau ne karon farko da kika fara ganinsa,nasan kuma zakiyi mamakin yadda akayi ya samu izinin ganinki direct daga wajena.....ya nema izinin soma ganawa dake ne kamar yadda shari'a da kuma al'ada ta tanadar,ya cika dukkan sharudda da akeson mai neman auren diyarka ya cika,wannan ya sanya na bashi izini,zaici gaba da zuwa har zuwa lokacin da zaku daidaita kanku,ku kuma aminta da junanku,kije kiyi addu'a,Allah yayi miki albarka" ya qarqare maganar ba tare daya bata damar cewa komai ba.

"Ameen" tayi qarfin halin kalato jimlar daga kowanne sashe na bakinta ta hadata sanann ta furtawa abban.

Sai da tayi namijin qoqari sannan ta yunqura ta miqe,kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki,haka ta dinga ji tun daga zuciyarta zuwa gangar jikinta a birkice.

Kasa qarasawa tayi cikin gidan,ta biyo ta farfajiyar gidan,sanna a hankali ta karkata zuwa sashen hagu na gidan,inda aka kebance wajen da wasu qawatattun kujeru domin hutawa musamman da yammaci,irin yammacin da zafin rana ke damun dan adam.

Kujera daya taja ta zauna akai,daidai sanda take fidda wata ajiyar zuciya me nauyi da zafi,tasa dukka hannayenta biyu ta dafe kanta da taji yana niyyar fara mata ciwo saboda nauyin da maganar ta yiwa qwaqwalwarta. Ko da wasa bata taba sanyawa a ranta mahmud zai iya zama saua daga cikin matsalolinta ba a rayuwa,kwata kwata ma bata taba daukar batunsa da muhimmanci ba,shi yasa bata ja masa layi tunda wuri ba,ashe tayi sake,gashi yayi mata shigar burtu,yakai wani guri da idan batayi da gaske ba zai iya sawa a tanqwarata tayi abinda bata da niyya ko lissafin yi.

Shurun da afifa taji yayi yawa sãahar din bata dawo ba,shi ya sanyata kashe laptop din ta sauko daga gadon,dakin maama ta leqa,ta sameta ta fito a wanka tana shiryawa

"Bata shigo ba,tunda kuka wuce daki tacemin ta taho da ayyuka daga office zata rage banga ta sake fitowa ba" sai afifan ta juya zata fita,har takai qofa maaman ta kirata

"Ko abbanku yayi maganar da ita?" Kai afifa ta gyada

"Haka nake tunani maama" jinjina kai tayi fuskarta na bayyanar da damuwa

"Dubata don Allah" juyawa afifan tayi ta fice itama jikinta yana bata lallai akwai damuwa.

Ta jima lausasan tafukan hannuwanta kife saman fuskarta,tanason ta daidaita yanayinta ne ta kuma ragewa kanta damuwa kodon ayyukan data debo masu yawa daga office. A nutse taji an dafa kafadarta,ko bata juyo ba tasan wacace,amma sai tayi burus,a wannan gabar itama afifan ta shafeta,haushinta takeji sosai,ko banza ta taka muhimmiyar rawa wajen faruwar wannan abun,tasan babu ta inda mahmud zai samu cikakken information a kanta sai wajen afifan,inda ta barshi kamar yadda ta bashi tsaye a wajen..... tun a ranar,da tuni an wuce wajen,batajin zata sake bashi damar ganinta ma bare wani abu makamancin wannan ya biyo baya.

Zagayowa tayi ta zauna ganin taqi waiwayowa gareta duk da ta tabata,tasan fushinta akanta,wannan din kuma da tayi alamace na tayi fushi. Sai data zauna sosai sannan tayi kiran sunanta,tsahon wasu sakanni ba tare data motsa ba,kamar bata jita ba,daga bisani kuma ta fara sauke hannuwan nata idanunta fes akan afifa.

Kallon kallo suka yiwa junansu,kafin ta miqe a nutse tara ture kujerarta baya

"Don't say anything......kinsan kome tunda kece silar faruwar komai din" ta fada calmly tana niyyar wucewa. Murmushi ne ya subucewa afifan,amma tasan cikin bacin ran da taketa kokawar dannewa take,don haka bata bari taga murmushin nata ba,ta miqe kawai tabi bayanta

"A shirye nake na fuskanci kowanne irin hukunci,nidai na shirya sauya rayuwar 'yar uwata ta kowacce hanya me kyau,wannan karon tare nakeson a daura mana igiyoyin aure uku" kamar ta sanya waigi ta tsaida sãahar din,ta dakata da tafiyar da takeyi,sannan ta waiwayo ta zubawa afifa fararen idanun nan nata,ta motsa siraran labbanta a hankali

"Aiba watanni shida masu zuwa ba,nan da shekara shida ma,ki rubuta ki ajjiye nan daura damaran yin aure ba" dukka girarta biyu afifa ta dage cike da tsantsar mamakin yadda kullum take dada zurfafa wajen tsanar maza,da kuma nisanta kanta da yin aure

"Ahhh.....kice mun kusa bada sadakar wata yarinya a gidan nan"

"Bismillah" ta fada a taqaice ganin afifa nason maida batun wasa,bata tsaya saurarenta ba ta wuce ciki.

Aiki biyu ta hadawa kwanyarta kusan lokaci guda,damuwa ga aikin office din data debo,haka ta yita yaqi da kanta,har Allah ya bata nasarar wancakalar da wancan batun,tunaninta da hankalinta ya karkata sosai ga files din da take dubawa,tanayi tana hada wasu bayanai a system dinta tana saving. Ba ita ta tashi a wajen ba sai sha biyu saura,ta fahimci abubuwa masu yawa tarin naqasu da kuma gyare gyare,tana kuma saka ran daga gobe zata fara gudanar da aikinta da dukkan fikira da baiwar da Allah ya bata,kafin ta kwanta ta hada dukkan wasu bayanai masu muhimmanci,printing dinsu as document zatasa kawai ayi idan ta isa office.

*_W A S H E G A R I _*

Ta tashi a miskilarta sosai,har ta kammala shirinta,yau dimma cikin wata lafiyayyar lafaya me bala'i kyau da asalin tsada,wadda ta dace da takalmi da qaramin band bag dinta samfurin kamfanin Hermes,tayi wani masifar kyau,daurewar fuskar tata ta sake qara mata kyau da kuma kwarjini na musamman,tayi wani irin sassanyan kyau,sulbi da laushin fatarta a ido kawai kana iya fahimtarsa. Sarai afifa ta fuskanci fushi takeyi da ita,yau da alama 'yan miskilancin har a kanta suka sauka,don haka tana tsaka da nata shirin fita gurin aikin,hannunta riqe da towel tana goge jikinta

"A sister like no other" ta fada tana kanne ido alamun tsokana,duk da cewa so take ta tsokaneta,amma har cikin ranta shigar ta sãahar tayi kyau sosai. Waiwayowa tayi ta jefa mata harara

"Ki samu wanda zakiwa dadin baki" qaramar dariya afifa ta saki, sãahar ta gama daura agogon hannunta,tana fesa lallausan turarenta afifa ta sake cewa

"Ki duba mudubi sosai fa kafin ki fita,gudun samun matsala" ta qarasa maganar tana qunshe dariya,datakawa sãahar tayi daga zuge zip na hand bag din nata,ta juyo tana duban afifa

"Matsala?,kaman yaya?"

"To ai wabillahi any moment za'a iya samun matsala,wannan kyan dake fita daga fuskarki kowacce safiya,kina zaton akwai namijin da zai iya gani ya kau da kai karon farko bai kawo kanshi ba?" Maganar ta fusgi hankalinta,saita waiwaya tana duban kanta da kanta a mudubi,tsahon wasu sakanni sannan ta dawo da dubanta ga afifa dake danne dariyarta,yanayinta yayi wani irin sanyi,kamae wadda ke shirin sakin kuka. Dukka kafadunta afifa ta dage ta yarfar da hannu

"No way out fa malama,indai ba shafa kashi zaki koma yi ba,just kawai ki bawa mahmud kai bori ya hau,shine zaki zama cikin aminci"

"Saiki auramin din mamata" ta fada adan fusace tana fusgar jakarta ta nufi hanyar fita,afifa ta saki dariyarta sosai
Chapter 22 · 0% Book details